Showing 63001 words to 66000 words out of 296192 words

Chapter 22 - GABA DA GABANTA

mata tambayar. Gaba daya annurin fuskarta ya ɗauke, tayi shiru ba ta ce komai ba.
"Hafsa meyasa kike gudun amsa mini tambayar nan ne?".
"Saboda ƙaddarata"
"Mecece ƙaddarar taki gaya mini, zan fahimceki".
Ta share hawayen da suka fara zubo mata ta ce "Zan gaya maka idan ka sake dawowa, amsarka bayan jin mecece ƙaddarata ita zata amsa maka tambayar da kake mini na idan ina sonka"
"Ki gaya mini yanzu ko zan samu nutsuwa mana".
"A'a dare ya fara yi kuma ga sanyi, zan gaya maka insha Allah"
"Shikenan, jeki ki gayawa Mama zan shigo in gaisheta" Hafsa ta tashi ta tafi, shi kuna ya buɗe jug ɗin ruwan, ya zubar da sauran, ya ƙulle kuɗi a leda ya saka mata, dan ya san idan ya ce zai bata ba zata karɓa ba.

Ya shiga suka gaisa da Mama, Bayan ya fito Hafsa ta biyo shi da wata leda babba, ta bashi. Ya sa hannu ya karɓa ya ce "Ni kome kika bani karɓa zan yi, ni ba irinki bane"
"To ni ɗin ya nake?"
"Kin fini sani ai, ranar ai a kan 500 kika kusa yi mini tijara"
Murmushi Hafsa tayi ta ce "Baka da mantuwa ko?"
"Ina zan manta, sai da safe" yayi mata sallama sannan ya tafi gida, aikuwa a hanya Hafsa ta dinga kiransa a waya, ya san a kan kuɗin nan ne, dan haka yaƙi ɗagawa. Gaba ɗaya zuciyarsa ta tafi a kan son sanin ƙaddarar da ke cikin rayuwar Hafsa.

Da yaje gida a falo ya shigo da ledar, jin ledar da zafi tun lokacin da Hafsa ta bashi, ya san cewa abin ci ne a ciki.
Ya sa Amina ta kawo masa plate da cokali, Mummy sai binsa take da kallo, tana tambayarsa daga ina yake.
"Wurin Abdul" ya bata amsa.
Ya zazzage ledar, Awara ce fal, da miyar jajjage ga kabeji da cucumber fal a gefe. Murmushi yayi ya juye a kan plate ɗin, ya sa cokali ya fara ci"

"Me kake ci haka ne?" Mummy tayi maganar tana leƙa plate ɗin.

"Mummy awara ce fa" ya faɗa yana cigaba da ci.

Yamutsa fuska ta yi ta ce "Awara Khalil? Kaima ka fara irin wannan cimar yunwar? Meye haɗinka da wata awara?"

Khalil ya ce "Mummy amma naga Abinci ce itama, ta burgeni ne shi ne na saya".

"Duk Abincin da yake gidan nan ka rasa me zai burgeka sai awara? Me akayi a ka wata awara, wannan ƙazantar da ake sayarwa a bakin hanya, wato shi dai Abdul ɗin nan dole sai ya maida kai irinsa, shike koya maka duk wani halin ƙauyanci da shirme, yanzu idan cikin ka yayi ciwo fa?"

"Mummy ba Abdul ne ya sani saya ba, ni na saya da kuɗina fa".

"Tun da kake a gidan nan ka taɓa ganin an sa kuɗi an sai wanna abar? Saboda kalan yunwa da nemawa kai masifa shine kaje ka saya kana sawa a cikinka, baka san da yadda aka yi ta ba, ke zoki ɗauke wannan a bar kuje ku cinye ta" tayi maganar cikin tsawa tana kallon Amina.

Mamaki ne ya kama Amina, duk a kan awarar ake wannan tashin hankalin, wato idan ma abun mutuwa ne su suci su mutu kar ɗanta ya ci. Khalil yana ji yana gani, Amina ta ɗauke awarar kitchen ta kai awarar ta ce "Aikuwa ba zamu ci ba, shi ɗin ne zai cinye a barsa, wannan matar lamarin nata ya wuce tunani" Khalil yayi fushi ya bar Falon, dan ba ƙaramin daɗi awarar tayi masa ba, dan da gani ta musamman ce Hafsa tayi masa.
Ta ƙofar corridor Amina tabi, taje ta ƙwanƙwasawa Khalil ƙofa. Kamar ya share sai kuma ya buɗe.

Amina ta miƙa masa plate ta ce "Ga awararka nan na kawo maka, Naga kana so" ya ɗan ƙura mata ido sannan ya karɓa ya ce "Na gode sosai".

"Never mind" ta faɗa a taƙaice ta juya ta koma.

Fadila tai ta jujjuya maganganun Yusar a kan Yazeed, ƙarshe kawai tayi tsaki ta bar zancen Yusran a shiririta.
Sai dai ba abinda ya sauya, daga yawan mafarkin Yazeed da take yi.

"Baba ga karin kumallo na kawo maka" Amina tayi maganar hannunta riƙe da wani ɗan madaidaicin faranti, tana kallon Baba.
"Yauwa uwata, Allah ya yi miki Albarka".
"Ameen, amma ya aka yi naga idonka yayi ja?"
"Mura ce ta sakani a gaba, ta saka mini ciwon kai da zazzaɓin dare".
Cikin kulawa Amina ta ce "Baba to ka karya sai in raka ka Asibiti mana".
"A'a uwata, zan warware insha Allah, zan dafa rai ɗore in sha, na kuma karɓo magani a Chemist"
"Baba gara dai muje Asibitin"
"Ki bari idan ban warke ba zuwa gobe in Allah ya kaimu sai inje" ya ƙarasa maganar tari na taso masa"

"Sannu Baba, ka karya sai ka kwanta, hannunka ma ya ɗau zafi sosai".

Baba yana tsaka da karyawa, Fadila ta fito tana ta wani hura hanci, ta yiwa Baba alama da yazo.
Baba na shirin tashi, Amina ta ce "Baba zauna, bari ni naje" ta tashi ta nufi in da Fadila take.

Fadila ta kalleta a wulaƙance ta ce "Ba ke nake kira ba, Babanki nake kira".

Amina ta ce "Bashi da lafiya ne shiyasa na zo".

"And so? Baki ji me mace bane babanki nake kira bake ba" ganin kamar suna jayayya ya sanya Baba tasowa, ya ƙarasa in da suke tsaye ya ce "Gani".

Fadila ta kalleshi ta miƙa masa kuɗi ta ce "Gashi nan, kaje ka tari Napep kaje gidan su Yusra zata baka saƙo ka kawo mini"

Amina ta ce "Ni ki kwatanta mini gidan sai inje, Baba bashi da lafiya fa".

Cikin tsawa Fadila ta ce "Nace Babanki na aika bake ba, karki sake saka mini baki a maganata"

"Kiyi haƙuri dan Allah ni ki aike ni, jikinsa da zazzaɓi"

"Baban naki ma ya aka cika idan an aike shi, shi da ya daɗe a birni balle ke bagidajiya 'yar ƙauye kije gidan mutae kiyi musu hauka da jahilicin naki da kika saba ki zubarwa da mutane mutunci"

Baba yayi gyaran murya ya kalli Amina ya ce "Uwata, ai jikina da sauƙi sosai Alhamdilillah, bari inje maza jeki ɗau Abincina ki rufe mini yanzu zan dawo" Baba ya juya ya nufi gate, yana takawa a hankali saboda jikinsa ba daɗi.
Fadila kuma ta koma ciki abunta, Amina kuwa tamkar an dasata, sai ma wasu hawaye masu zafi da suka fara biyo kuncinta.
Tana nan tsaye Alhaji Ahmad ya fito, cikin suffarsa ta kwarjini da kamala, tun da ya fito Amina ta zuba masa idanuwa, har sai da ya tsargu, amma har ya gifta ta ko gaishe shi bata iya yi ba.
Ya wuce ya hau motarsa, wannan karon ba direba da kansa yake tuƙi, Zakiru ya buɗe masa gate ya fice.

"Tabbas kan in bar gidan nan, sai nayi maka abin da har 'yarka ta koma ga Allah ba zata manta ba, sai taji abin da nake ji idan taci zarafin mahaifina".

Ayshercool
08081012143GABA DA GABANTA

AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

To get the latest update of the story
Follow me on Watpad
Ayshercool 7724
Arewabooks
Ayshercool 7724
What's app 08081012143


*Littafina Aƙidata da kuma Ruɗin ƙuriciya, na kuɗi ne, sauran duk free me*

18-19

Amina ta ja jikinta a hankali, ta koma wurin zaman Baba ta zauna, tana jin yadda sanyi ke ratsata, wani irin tausayin Baba ya mamaye zuciyarta, Allah kaɗai ya san irin ƙalubale da wulaƙancin da ya dinga fuskanta a gidan nan, amma yake dakewa yana shanyewa.
A ƙalla Amina ta shafe awa guda a zaune, amma Baba bai dawo ba, haka ta tashi ta koma cikin gidan, zuciyarta na mata ƙuna game da abin da Fadila ta yi wa Babanta.

Ta tagar corridor Amina ta hango Baba ya nufo hanyar shigowa cikin gidan.
Da sauri ta fito falo, idon Baba duk yayi ja, saboda yadda ya sha ƙura a hanya. Fadila kuwa na zaune sai kaɗa ƙafa take, tana latsa remote hankali kwance.
Baba ya ƙaraso ya ɗan risuna yana miƙa mata ledar hannunsa.
"Wai kai dan Allah duk lokacin da aka aikeka, sai kaje kai zamanka?"

"Yi haƙuri ba haka bane, titunan ne akwai cunkoson ababen hawa, mussaman yau da aka tashi da hazo".

"Ajiye a wurin ka je, Na gode" ya ajiye mata ya miƙe, Amina ta fito ta biyo bayansa, amma Fadila ta kalleta ta ce "Ke zo nan" Amina ta tsaya cak ta waiwayo tana kallon Fadila.

"Akwai undeas ɗina a toilet, ki je ki wanke mini, sannan ki sauke jakunkuna na daga hanger duk ki goge mini su" Wani abu mai ɗaci ya tsirgawa zuciyar Amina, Baba ya kalleta yayi murmushi, yana gyaɗa mata kai cikin bata ƙwarin gwiwa da kwantar mata da hankali.

Amina ta juya ƙafafuwanta suna rawa, ta nufi sashin Fadila.

Sai da Hafsa ta yiwa Khalil mita a kan kuɗi da ya bata haka da yawa, ta dinga mita tare da cewa ya zo ya karɓi kuɗinsa, a karo na farko da ya nuna mata ɓacin ransa tun bayan haɗuwarsu, sai kuma taji babu daɗi dan ƙarshe ma kashe wayarsa yayi.
Sai da ya wuni be kirata ba, idan ta kira shi kuma yaƙi ɗagawa, gaba ɗaya ta shiga damuwa.
'Kenan da gaske na fara son Khalil? Idan kuma ya san wacece ni ya ƙi aurena fa ya zan yi?' ta tambayi kanta, take kuma taji kanta yayi mata wani irin dumm babu daɗi, ta shiga taradaddin halin da zata shiga idan Khalil ɗin ya kasa ɗaukar ƙaddarar da ta faɗa mata.
  Kasancewar an tashi da hazo sosai, ya sanya Hafsat take ta kula da Mama, dan kar ta fito tsakar gida ko tace za tayi wani aiki, saboda yanayin jikinta, ba ta da cikakkiyar lafiya, amma hakan bai hana tari ya sarƙe Mama ba, duk wani taimako da Hafsa zata iya bata ta bata, amma abu yaci tura, dan har numfashinta ya fara sama sama.
Cikin hanzari ta tashi ta samo abin hawa, suka tafi Asibiti. Suna zuwa aka basu gado, likitoci suka fara ƙoƙarin suga numfashin Maman ya daidaita.
Hafsa ta ƙurawa Mama ido, an saka mata Nebulizer, ga drip a rataye.
Hafsa ta sa kujera ta zauna, ta cigaba da kallon Mama, ta riƙo hannun Mama tana tuno abubuwan da suka gabata a rayuwarsu, da kuma yadda aka yi Mama ta haɗu da wannan larurorin da suka mamayeta. A hankali wasu irin hawaye suka shiga zubowa daga idanunta, ba dan kuɗin da Khalil da ya bata ba da bata san ya zata yi da ciwon Mama ba.
  Kwanansu biyu a Asibiti, amma Khalil baya ɗaga wayarta, gaba ɗaya ta shiga cikin damuwa, sai da hakan ta faru sannan ta gane a 'yan kwanakin nan ba ƙaramin sabawa tayi da Khalil ba.
Shi kansa Khalil daurewa yake yi, baya jin daɗin rashin wayar da ba ya yi da Hafsa, amma dole ya dinga nuna mata fushinsa idan ba ta kyauta ba, yana matuƙar son ta, kuma yana son ya taimakesu, mussaman duba da yanayin halin da suke ciki, amma taurin kan Hafsa yafi ƙarfinta.
A kwana na uku ne, Hafsa na saka ran a sallami Mama, dan a kwanakin nan kuɗin wurin Khalil da ke hannunta sun ƙare, harta fara shiga na sana'arta, dan kullum cikin kawo kawo ake a Asibitin kamar ba na gwamnati ba.
Ba tsammani taga kiran Khalil, amma ta share, sai da Mama ta kalleta ta ce "Ba kiran wayarki ake ba?"

"Eh wayata ce".

"To ki ɗaga mana"

"To zan ɗaga" ta amsawa Mama amma taƙi ɗagawa.

Ganin Mama ta ƙura mata ido ne, ya sanya ta ɗaga wayar, tana tura baki ta amsa masa sallamar da yayi da ƙyar.

"Na je gida ba kowa, kuna ina ne?"

Ta kalli idon Mama sannan ta ce "Muna Asibiti Mama aka kwantar"

"What? Amma baki gaya mini ba, wane Asibitin ne?".

"Ai sallamar mu za ayi yanzu, likitan dare muke jira ya sake dubata mu tafi".

"Ba wannan na tambayeki ba, wane Asibitin ne?" Har ga Allah Hafsa bata son yawan ɗawainiyar da Khalil yake yi da su.

"Hafsa magana nake miki fa"

"Mhm nifa nace maka gida zamu taho"

"Wai ya kike mini jayayya ne?" Ya faɗa a hasale.

Haka ta haƙura ta gaya masa tana tura baki, dan taji haushin ɗaga mata murya da yayi.

Da hanzari ya shiga falo yana dube-dube.

"Ya aka yi ne?" Mummy ta tambayeshi.

"A nan na bar car keys ɗina?"

"Me zaka yi da makullin mota yanzu da daddare ba ka dawo gida ba kenan?".

"Eh zani wani wuri ne".

"Ina ne wani wuri?" Tayi maganar tana tsare shi da ido.

"Mummy sai kace wani mace, wani wuri zani fa, yanzu zan dawo" yayi Maganar yana ɗaukar key ɗin da yake kan dining yayi waje.

Fadila ta ce "Wurin wata zashi, ina ga wannan Yarinyar ce, ko ita aka kwantar Asibiti, ko wani nata, kan ki fito ya shigo yana waya".

Mummy ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Wai ni 'yar waye Yarinyar nan, yakamata in sani tunda wuri".

"Waya san masa, shi zaki tambaya".

Bai fi mintuna Arba'in ba, Khalil ya sake kiran Hafsa, ya ce ta zo ta shiga da shi, amma taƙi fita, ta gaya masa lambar ward ɗin da suke.

Sai da ya daure sannan ya iya shiga ɗakin, marasa lafiya sun kai mutum Ashirin a ciki, sai ƙarni da warin Asibiti da ke surnanowa daga cikin ward ɗin, haka ya daure ya shiga, tun da ya shigo ta hango shi, amma ta basar yaita lalube ya gano su.
  Sai da ya ƙaraso sannan Mama ta gane shi, ya nuna kamar bai ga Hafsa ba, ya durƙusa ya gaida Mama, ta amsa masa cikin kulawa.
Nan ya zauna yana yiwa Mama sannu, Mama ta kalli Hafsa ta ce "Ke baki iya gaisuwa ba?".

Fuskarta ba fara'a ta ce "Ina wuni" ba tare da ta kalli Khalil ba.

"Mama ƙyaleta, bana neman gaisuwata, Fushi nake da ita, Mama kwana uku kina Asibiti amma yarinyar nan ta kasa kirana a waya ta gaya mini, sai ma wani cika da take tana batsewa".

"Da na kiraka kana ɗagawa ne?" tai maganar tana kuma ɓata rai.

Mama sai da ta ƙulu da abin da Hafsa tayi, amma tayi shiru ta rabu da ita, kasancewar likitan da zai sallami Mama bai shigo da wuri ba, ya sanya ya ce Mama ta bari sai da safe.

Ya tashi zai tafi, ya sanya hannu aljihunsa, ya ciro kuɗi ya ajiye a kan side bed, Mama za tayi magana Hafsa ta rigata "A'a ka barsu gaski... Ba ta ƙarasa ba Khalil ya watsa mata wani irin kallo, da ya sanya ta haɗiye maganar da take son ƙarasawa.

Ya kalli Mama ya ce "Mama in dai ni ɗanki ne, bai kamata ki ƙi karɓar abin hannuna ba, Allah ya baki lafiya, gobe Insha Allah in an sallameki, zan zo gida in sake dubaki" yayi sallama da Mama ba tare da ya ko kalli Hafsa ba, yayi gaba abin sa, tabi bayansa da kallo tana jin haushin yadda ya shareta.

Bayan fitar sa sai da Mama ta yiwa Hafsa ta tas, a kan abin da take yiwa Khalil.

  Amina tana ta ƙoƙarin kula da Baba, amma Hajiya Zainab da Fadila suka tsiro da wani wulaƙanci, da sun fuskanci tana son wurin Baba, sai a tsiro da aikin da za'a sakata su hanata zuwa, haka kurum 'yan kwanakin nan suke tsangwamarta, ta rasa me ta tare musu.
  Yau ɗaya daga cikin 'yan ajinsu Amina take sauka Alqur'ani, kuma an gayyaceta, tana son zuwa ko dan ta ƙare sanin kan cikin birnin Kano. Ta nunawa Baba katin gayyatar, ya amince taje, tare da yi mata nasiha sannan ya ce ta tambayi Hajiya Zainab, kar fitar tata ta zamana laifi.
Ba dan Amina ta so ba, ta tambayi Hajiya Zainab, ba ta sa ran ma zata barta ba, amma cikin ikon Allah kawai taji ta amince.
  Amina ta dinga murna, dama sun yi da ƙawarta Azima, zata biya gidansu su tafi tare, dan bata san gidan saukar ba.

Duk da gidansu Azima bai kai na su Fadila girma da kyau ba, amma suma da gani suna da kuɗi sosai, sai dai halayyar 'yan gidansu Azima ya sha banban da na su Fadila, Maman Azima na ganin Amina, ta karɓeta da fara'a tana faɗin "Yau ga Aminan Azima a gidana, kullum sai an bani labarin Amina H shanono, yau dai gani gata" Amina ta ƙunshe fuska tana murmushi.
Maman Azima ta ce "Tana can tana wanka, ita da idan ta shiga banɗaki, tamkar tana ɗakinta, bari a kawo miki Abinci".
"A'a Ammi na ƙoshi" ta ɗan tsuke fuska ta ce "Hala ita Aziman bata gaya miki idan an zo gidan nan ba na bada abu aƙi karɓa ba? Dole ki ci Abinci Amina, ga ɗakin Aziman can, ki shiga sai a kai miki Abincin can" Amina ta shiga ɗakin Azima, ɗakin ya haɗu sosai da sosai.
Azima na fitowa daga wanka, taga Amina, ta daka tsalle ta rungume Amina.

"Ke cikani kar ki tsirara malama"

Azima ta ce "Ashe zaki zo ɗin 'yar rainin hankali kawai, amma dai ba da wannan shigar zamu je wurin saukar ba?".

Amina ta kalli kanta ta ce "Me shigata tayi?"

"Ke ba zamuje a raina mu ba, kin san halin 'yan ajinmu, bari in shiga shagon Ammi, in ɗauko miki sabuwar riga" Amina ta zaro ido tana shirin magana, mai aiki ta shigo ɗakin, ta dinga ajiyewa Amina kayan ciye-ciye.

Azima ta fita ta dawo da wata rantsatiyar doguwar riga purple da takalmi da jaka duk kalar rigar.

Azima ta ce "Gashi nan Ammi ta ce a baki ki saka" da yake Ammi na da shagon botiques a cikin gidan.

Jiki a sanyaye Amina ta ce "Azima, kin san ni wacece, dan Allah ki bar kayan nan, in je da na jikina"

"To sai ki je ki gayawa Ammin ai"

Amina fafur taƙi yadda ta saka kaya, sai da Ammi ta zo da kanta, Amina ta ce "Ammi ba ƙin karɓa nayi ba, Baba zai tambayeni ina na samo kayan nan, kuma gidan aikina zasu tambayeni".

"Kar ki damu, direba ne zai kai ku, ya mayar da ke gida, sai a yiwa Baban naki bayani"

Da ƙyar Amina ta yadda, ta cire hijjabin jikinta, da yayi haske saboda ya gaji, tun irin wanda ta zo da su daga ƙauye ne.
Ta canza kaya zuwa doguwar rigar nan, ga uban gashinta da yake natural, ta tattare shi da tsohon ribbon.
Azima ta sakata a gaba, ta saka comb tana taje mata gashin nan, ta shafa mata mai, ta kawo kayan make up, tayi mata simple make up.
Azima ta ce "Ke yarinyar nan Allah yayi miki kyau, amma ko hoda ba kya shafawa haka kike yawonki"

"Ke ni ƙyaleni da wata hoda" yadda Amina tayi kyau, ba zaka ce daga ƙauye take ba, Azima ta buɗe wani

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login