Showing 252001 words to 255000 words out of 332834 words

Chapter 85 - Bakar wasika Complete Hausa Novel

06 Oct 2024

65608

kara mata da nata.
 
“Idan asiri gaskiya ne ai sai ki je yi, baki san ma na mallake shi ba sai na hana shi aurenki, kuma kauye ai kowa salinsa kauye ne”
 
Boom! Wannan karon Leila ce ke mamakin jin furucin Aminatu ba Talba ne, he was shocked ace kalaman nan daga bakin Aminatu suka fito, how? Yaushe tai baki haka? Bata ma jin tsoron. Ya kalli Leila da tai shiru tana wani irin cika kamar zakanya, sannan ya kalli Aminatu still yana mamaki.
 
“So you can talk”
 
Leila ta kalleshi da mugun takaici.
 
“What do you mean she can talk? Are you supporting her? Taya kana kallon karamar yarinya kamar wannan tana fada min magana without doing anything?”
 
Hawaye ya sauko a idonta.
 
“I'm not supporting her, ke kika fara fada mata magana marar dadi and ta rama, na ce na goyi bayanta?”
 
“Thank You”
 
Ta furta tana murmushin daya fi kuka ciwo sannan ta juya zata fice, sai ya kirata da sauri.
 
“Leila...”
 
Bata amsa ba balle ta juyo ta kalleshi ma, ta fice dakin cikin bakinciki da bacin rai. Talba ya kalli Aminatu cikin rashin jindadin yadda Leila ta fita dakin.
 
“You shouldn't talk to her this way Babe, be kamata ki fada mata haka ba”
 
Kamar mai jira nan da nan nata idon ya cika da hawaye.
 
“Ni me na mata da take fada min magana? Ita da mahaifiyarta me na tare musu? Kana jin tana ce min yar kauye kazama”
 
Ya daga kansa sama yana sauke numfashi.
 
‘Oh ya Allah’
 
Ya furta a ransa sannan ya mika mata hannunsa, sai ta nade hannayenta ta matsa baya tana turo baki, hawayen har ya fara sauko mata, wani zafi ma take jin zuciyarta na mata saboda ya shigarwa Leila.
 
“Ni ka kira min Mama, ta zo ta tafi da ni”
 
Sai ya sauko a hankali saman gadon ya mike tsaye, ya karasa inda take cike da karfin hali ya rumgumeta.
 
“Yi hakuri. Kin ga babu waya tare da ni, bari Ali ya shigo ko Kabir na tambaya waya dauki wayata sai na kira miki ita, amman kamin nan yanzu ina son ki hada min tea na sha, sai ki zuba min abinci gashi nan a cooler. Zan wanke bakina”
 
“Toh”
 
Ta amsa cike da shagwaba, murmushi yai ya sake ta, ba karamin burge shi take ba idan tana masa shagwabar, ko ba komai hakan da take tana nuna masa shi ne gatanta, kuma shi ne wanda zai iya share mata hawaye, kuma ya fahimci damuwarta, daman mace da shagwaba aka santa, ba kamar namiji ba. Ya fara takawa cike da karfin yana jin kirjinsa kamar zai rabe gida biyu, sai dai baya son nunawa kar ta gani hankalinta ya tashi. Sai ya shiga bandaki ya rufe sannan ya ya dafe kansa ya durkushe a kasa ya cige bakinsa, alamar yana jin azaba sosai. Sai da ya lumshe ido ya bude a hankali sannan ya yunkurin ya tashi yana ambaton Allah a zuciyarsa ya karasa gurin da tub din yake.
 
 
*** **  ***  **  ***
Leila ta nufi inda su Momy suke zaune tana hawaye ta zauna tana jin kuka na son kwace mata, bata taba sanin haka take kishin Talba ba sai yau, ji tai kamar ace tana da wuka a hannunta ta yanka naman Aminatu.
 
“Ke Lafiya”
 
Hajiya Saratu ta tambaya.
 
“Mama ina shiga dakin nan na same ta rumgume da shi, na yi magana har tana cewa wai ta yi asirin sai ma ta hana shi aurena, imagine yar kauye kamar wannan zata fada min magana”
 
Momy ta saki baki da mamaki.
 
“Ashe yar iska ce? Ita Aminatun ta fada miki haka? Shi Talba yana nan, ita wannan yarinyar har ta samu baki?”
 
“He take her side”
 
Ta amsa tana share hawayenta. Hajiya Saratu ta tabe baki.
 
“Hmmm ai raba kanki da yan kauyen nan, ai idan suka shiga birni sun fi yan birnin iskanci, da nuna isa, ko kishi kike da yar kauye sai a fi sonta da ke, ai yan kauyen nan kwace miji suke yi,duk wata kirsa da kisisinar shiga zuciyar miji sun sani, kuma basa barin zama banza ai”
 
“Tab di jam, Leila ba karamin aiki ke gabanmu, tun yanzu kenan? Me kike tsammani a gaba?”
 
Momy ta fada, sai Hajiya Saratu tai kwafa.
 
“Ki bar komai a hannuna, Wallahi wannan bokan ya iya aiki, shiyasa ma nake son Leila ta tafi ko miye zai mata yayi mata abubuwa su fara tafiya yadda muke so, ya fada min da bakinsa cewar da Ja6a ma zai yi aikin, kin san ko yadda Ja6a take da wari dole ma zai rabu da ita”
 
“Yauwa haka muke so”
 
Cewar Momy, sai Leila ta sake share hawayenta tana kallon Hajiya Saratu.
 
“Minene Ja6a Mama Sadiya?”
 
“Wata abu ce mai shegen warin tsiya, zaki ganta kamar 6era amman ita wari ne da ita sosai, ba a son tana ra6ar mutane ne ma saboda warinta”
 
Leila ta dan shinshina jikinta.
 
“Amman fa ni ina jin wani wari, marar dadi ni ban ma taba jin irinsa ba, ko dazun sai da na yi wanka sannan na daina jinsa, sunan Aminatu kika bada ko nawa?”
 
Daga Momy har Hajiya Saratu kallon Leila suke da mamaki.
 
“Tun kwanan baya na fara jinsa, ina jin yau kwana biyu ko uku kenan warin har hawan kaina yake...”
 
Leila na kai aya kiran Madina ya shigo wayarta dake hannunta, sunan Madina na appearing gaban Leila yai mugun faduwa.
 

 
Hmmm idan kaga anzudda Miya to cinikin tuwo yakare.Kowa yace wutar Kara ta kwana to shine baiyi bacciba.Arashin Kira Karen Bebe ya Bata.Ina ma,abuta son gyara Manyan Mata idan nace mata Ina nufin wadanda suka San ciwon kansu sukasan darajar gyara da mutuncin da yake kankarowa👌to kuzu kumatso kusa taku dai dindaice Yar Gidan maifata Yar mutan Zamfara tazomaku da kalar nata ingantattu km gangariyar kayan gyara wadanda suka gwada sungani km sun sani wadanda km Basu gwadaba karkubari abaku labari kayan Basu bukatar dogon biyani sai dai gawadanda Basu sanmuba kayane kala kala iri daban daban, amma munhi gwanewa wurin gyaran matsaloli irin na aure da km gyaran amare da tsofi masu son tada komada Kai abundai sai Wanda ya gwada Don neman Karin bayani ko walwale rashin fahimta za'a iya tuntubata a number waya kamar haka 08169311410 ko km chat 09029891757 Ko km a address Dina dake Nasarawa Gusau wurin masallacin Mai solar Allah yasadamu da alkhairansa🤝🙏🤲
 
Ya dan yi yar kara, sai tai saurin daga daga jikinta idonta na cika da hawayen farinciki.
 
“Sannu Sannu Sannu, bari na kira likita”
 
Ta juya da sauri, sai yai hanzarin bude idonsa ya rika hannunta da hannunsa na hagu. Tana jiyowa ya girgiza mata kai alamar aa, sai ya sake lumshe ido. Tsoro ta ji ganin ya rufe idon duk da, duk da kasancewar yana rike da hannunta. Kura masa ido tai tana ta kallon fuskarsa, ganin be bude idon ba har na tsawon lokaci yasa ta matsa kusa da kunnensa ta kirashi a hankali.
 
“Yallabai...”
 
Sannan ta dago ta kalleshi, still idonsa a rufe, sai ta sake maida bakinta sautin kunnenta.
 
“Talba”
 
Ta sake dagowa a karo na biyu ta kalli fuskarsa, still be bude idon ba. Sai maida bakinta tai a karo na uku sai dai wannan karon ba saitin kunnensa ba ne, sai tin kumatunsa ta kai bakin ta sumbance da soft pink lips dinta a hankali. A hankali ya fadada fuskarsa da murmushi yai bude idon yana kallon dayya ta saka dayan hannunta tana jiran ya bude nasa idon ta rufe nata.
 
“I love you Babe”
 
Ya furta da kamar rada, sai tai saurin rufe idon tana jin wani kalar kunya ta rufeta. Hannunta dake cikin nasa yaja ya kai saitin kirjinsa yana kallon fuskarta data rufe da dayan hannunta.
 
“Hawo nan mu kwanta”
 
Ta janye hannunta da sauri.
 
“Zan kira likita ya dubaka, wannan Abokanka, ko wani”
 
Ya girgiza mata kai.
 
“Yana zuwa zai fara damuna da magana babu abun da zai min a yanzu, zo mu kwanta”
 
Ya fada yana gyara kwanciyarsa daker  domin har yanzu kirjinsa ciwo yake, matsa mata yai ta yadda zata samu gurin kwanciya a saman gadon. A kokarin na ki gujewa kwantawa gurin ta ce.
 
“Ina da wani labari da zan baka”
 
“To kwanta a nan sai ki fada min”
 
Tsayawa tai kallon gadon sannan ta cire talkaminta ta hau saman ta kwanta gefensa tai matashin kai da gefen kirjinsa zuwa damtsen hannunsa, tana kwantawa sai tai lamooo kamar bata gurin, sai kamshin turarensa ke kai mata hari a hanci. Ya kai bakinsa ya sumbacin goshinta yana kallon saman idonta kasancewar ta rufe idon ne gabanta sai faduwa yake.
 
“Fada min kyakkyawata labarin me?”
 
Ta bude idon ta sauri saboda ya tabo inda yake mata kaikayi.
 
“Da baka dawo ba, sai wannan abokinka likita ya ce matarsa ta kai ni gida....”
 
Daki daki ta tsara masa hadda lamarin ya faru har zuwa inda take son direwa, tana yi tana zane a jikin rigarsa, kana gani kasan tana cikin farinciki da jindadi. Murmushi yai yana ta kallon kwayar idonta, ba zai karyatata ba, amman labarinta be yi making sense ba, after ta fada masa ta rasa duka familynta yanzu kuma tace ta ga yayanta? How? Kallonta tai jin yayi shiru be ce komai ba, yasa ta fara rantsuwa.
 
“Wallahi da gaske nake, ba karya ba”
 
Ya kalli bakinta dake matsawa a hankali, sannan ya sake kallon idonta.
 
“Hug me rumgume ni”
 
Ta sauke nata idon daga nashi tana dan turo baki ganin ba ce komai ba.
 
“Baka yarda da labarina ba?”
 
Yayi murmushi ya lumshe ido, baya son musu da ita a yanzu kuma baya son ya zurfafa a tattaunar, domin jikinsa baya masa dadi.
 
“Hug Babe”
 
Ta dan yi sama kadan ta mika hannunta jikin wuyansa ta rumgume shi tana kallon kyakkyawar fuskarsa,sai ta kai hannu ta taba tsinin hancinsa, murmushi yai ba tare daya bude ido ba, ita ma murmushin tai tana kallon fuskarsa. Kara turo kofar dakin da suka ji yasa ta dago ta leka kofar sai tai arba da Kabir, Talba kam ko motsawa be yi ba, cos to him ba wani abu ba ne dan an tararsa shi yana kwance da ita a gado daya, idan ma akwai wanda zai ji ma kunya Daddy ne ko Momy, amman sauran siblings dinsa ba.
 
“Wanene?”
 
Ya tambaya still idonsa a rufe.
 
Sai tai masa rada tana kallon Kabir dake doso inda suke.
 
“Kabir ne gashi nan yana zuwa gurinmu”
 
Kabir yayi murmushi yana kallonta cike da burgewa.
 
“Ashe kin iya rada, yan matan Talba”
 
Sai tai saurin rufe idonta tana murmushin jin kunya, Talba ya bude idon ya dago cike da karfin hali yana kallon Kabir.
 
“Dan sa'ido”
 
Kabir yayi murmushi ya kai hannunsa ya cirewa Talba drip din dake hannunsa sannan ya zauna yana kallonsa.
 
“Ya jikin?”
 
“Alhamdulillah, kirjina ciwo yake sosai”
 
“Dole ne wannan, saboda kirjin ne ya bugu, amman yanzu tun da ka farka ai sai ayi maka hoton gurin a duba matsalar”
 
He nodded his head
 
“Ina Daddy?”
 
“Tare muka zo da shi, yana waje”
 
“Ya sani?”
 
“Yeah ya zo dazun ma, yanzu kuma ya sake kirana yace na zo muje, i told him ai fa ba zaman lafiya tun danka na asibiti”
 
Talba ya fadada fuskarsa da murmushi yana cin kaunar Daddy har ransa. Aminatu ta fara kokarin tsallaka Talba ta sauka.
 
“Bari na kira Likita”
 
“Ni kuma Nurse ne?”
 
Kabir ya tambaya yana kallonta, sai Talba yai hanzarin riko kwankwasonta, yana kokarin dawowa da ita.
 
“Ai kai ba likita ba ne”
 
“Saboda ban tana miki allura ba ko?”
 
“Aa ai likitoci da an gansu ana gane su, wannan abokin nasa ai shi kowa ya san likita ne, ban san ko wasa kake ba dai”
 
Kabir ya wara ido yana murmushin daya fi kama da dariya.
 
“Wato ni bana da kama da likitoci?”
 
“Aa ina nufi...”
 
“Shiiiiii”
 
Bata karasa ba Talba ya dakatar da ita ta hanyar yi mata alama da tai shirun, sai tai shiru kamar yadda ya bukata.
 
“Kai gawa ta ki rame, daga dawowarka zaka fara damun mutane?”
 
“Talba yayi murmushi, Please je ka shigo min da Daddy”
 
“Ya kamata ka ci wani abu yanzu ba”
 
“Kira Momy ta bani”
 
Kabir ya mike tsaye, sai da ya kalli Aminatu sannan ya juya ya fice daga dakin. Talba ya kalli Aminatu.
 
“Babe bana son kina sakewa da mutane, baki san muryar mace al'aura ba ce?”
 
“No muryar mace ba al'aura ba ce”
 
“To ni a gareni al'aura ce, bana son kina sakewa da maza any how, yanzu kin fada min wani wai kin ga yayanki waya sani ko kama ce kawai? And ya za'ayi ya zama yayanki bayan duka yan'uwanki an kashe su? And now you're sitting next to me kina magana da Kabir kamar wani dan'uwanki i don't like it”
 
“Ai ba wata maganar nake da shi ba, kuma shi din ai dan'uwanka ne”
 
“Dan'uwana ne, amman idan na mutu a yanzu he can marry you, bakin san wani namiji yana kishin aji muryarsa matarsa ba, balle har ace wani yana magana da ita? Ko da mummuna ce balle ke da kike kyakkyawa, muryarki kuma tana da dadin saurare, hakan zai iya sakawa mutum ya jaki da dogon hira saboda yai ta saurarenki”
 
Shiru tai bata ce komai ba, ba dan bata da abun fadar ba, sai dan bata son musu da shi.
 
“Sauko kar Daddy ya iskoki haka”
 
Ta rika hannunsa ta sauko saman gadon, ta nufi inda aka aje flask din ruwan zafi.
 
“Bari na hada maka shayi”
 
Ya kalleta kawai yayi murmushi ya yunkura ya tashi zaune daidai ya jingina da gadon. Tana daukar cup Momy na shigowa dakin tare da Kabir da Hajiya Sadiya da wata yar'uwar Daddy Hajiya Tuni, sai Daddy dake tare da wani abokinsa Alhaji Tukur. Kowane fuskarsa sake cike da farinciki. Ban da Daddy daya matso daf da Talba ya zauna saman gadon yana kallonsa fuska a hade. Talba na ganin yanayin Daddy ya san da magana a bakinsa, sai ya sauke kasan kasa yana amsa ya jikin da ake masa.
 
“Daman ka dade baka kwanta gado ba, yanzu ai ka kwanta yadda kake so, tun da baka da hankali baka san ciwon kanka, balle ka damu da halin da wasu zasu shiga idan wani abu ya same ka”
 
Alhaji Tukur ya tari numfashin Daddy.
 
“Kaddararo ne, ba a isa a kauce musu ba, kuma tun da har ya samu lafiya ai komai mai sauki ne”
 
Daddy ya kalli Alhaji Tukur rai a bace ya ce
 
“An fa fada yadda ya hau titin, duk abun da yai da gangan yai, tun da ya san akwai motoci a fiti ba shi kadai akai wa Titi ba, idan ma wani abun be ba akwai police ba, ce masa akai idan ya kama mutumen tsayawa zai yi? Waya sani ma ko yana da makami yai masa wata illar?”
 
“Daddy I'm sorry...”
 
Talba ya fada sai Daddy ya daka masa tsawa.
 
“Rufe mana baki, daman abun da kuka iya kenan bada hakuri, lokacin da zaku yi abu ba zaku duba kanku ko halin da na kusa da ku zasu shiga sai kawai ku aikata, idan an zo magana ku fara bada hakuri”
 
“Ai ba laifinsa ba ne, laifin wannan yar iskar yarinyar ne, mahaukaciya daga ganin mutum sai ki fara cewa ga wanda ya kamaki can, waya sani ko ba shi ba ne, shi kuma komai ta fada masa sai ya dauka”
 
Cewar Momy cikin tsawa tana watsawa Aminatu data kasa juyowa harara.
 
“Idan ta fada masa, shi ba shi da hankali ne? Ai ba fada masa ne matsalar ba, yadda yake wasa da rayuwarsa ne, taya zaka hau titi kana gudu kamar kai kadai akai wa titin”
 
Daddy ya kara fada, Kabir yayi murmushi.
 
“Wato dai idan mutum yana da uwa da uba a raye ya huta, ji yadda kuka masa fada kamar karamin yaro”
 
Aminatu ta juyo a hankali rike da cup din da bata gama hadawa ba, kanta kasa. Momy ta mata wani mugun kallo.
 
“La la la.... Uban waye ya ce ki taba kayan tea din nan? Da na aje cewa na yi ki dauka ki hada ki sha...?”
 
“Aa daman... ”
 
Bata karasa ba, Hajiya Saratu ta kai mata duka a kafada.
 
“Makira, munafuka”
 
Aminatu ta aje kofin da sauri idonta na cika da hawaye. Talba ya kalli Aminatu da sauri yana jin ba dadi.
 
“Haba Mama Saratu ni nace ta hada min”
 
“Ko ba kai kace ba, ma ai matarka ce, tana da yancin ta taba duk wani abu daya alakantu da kai, weather we like it or no, ta riga ta zama part of us, wannan abun da kuke yi ma yarinyar nan be dace ba Momy”
 
Kabir ya fada cikin rashin jindadi, sai Momy ta watsa masa harara, zata yi magana Daddy ya rigata.
 
“Na dauka na gargadeki akan yarinyar nan? Ita miye laifinta a ciki? Idan zaki huce haushi ki sauke akan Mu'az, ba ita ba. Kuma wannan ya zama na karshe da za ku sake cin mutuncin yarinyar ko ku kai mata hannu”
 
Momy bata yarda ta sake cewa komai ba, ta fice daga dakin cikin bacin rai Hajiya Saratu ta rufa mata baya, kofar bata rufe ba Ali ya shigo, farincikin dake fuskarsa baya boyuwa na ganin abokinsa a zaune. Sai da ya gaisa da su Daddy sannan ya shiga duba Talba, yana tambayarsa abun da yake ji.
 
“Kirjin ne dai kawai yake ciwo”
 
“Za a maka hoto sai a rubuta wasu magungunan, yanzu dai ka saka wani abu a cikinka”
 
“Okay”
 
Daddy ya mike tsaye.
 
“Kai ma Ali kana da kana laifin ai, idan ka ga Talba zai yi wani abu kamata yai ka hana shi, amman ka bar shi yana risking rayuwarsa kamar mai rai biyu”
 
Alhaji Tukur yayi dariya kamar Yadda Kabir da Hajiya Tuni suke. Ali ya ce.
 
“Daddy ka san halin ďanka ba jin magana yake ba”
 
“Yanzu dai aikin gama ya gama, sai dai a harari gaba, Allah ya kara tsarewa, kuma ya baka lafiya Talba”
 
Cewar Hajiya Tuni, sai duk suka amsa da Ameen, ban da Aminatu da ta maida fuskarta gefe tana ta hawaye. A tare Daddy ya fita da yar'uwarsa da kuma abokinsa, sannan Kabir ya saci kallon Aminatu.
 
“Ta hada maka wani tea, ko na hada maka”
 
“Zata hada”
 
Talba ya amsa masa, sai yai murmushi ya fice. Talba ya kalli Ali dake kallon Aminatu ya ce
 
“Ali samo min tissue please”
 
“Ayi me?”
 
“Hawayen matata zan share saboda na san zata min kuka”
 
“Kai ka gwada mata ta rika maka kukan kenan”
 
Ali ya fada sannan ya nufi kofa, yana ficewa Aminatu ta juyo ta fado jikin Talba ta fashe da kuka mai sauti riri kamar yar shekara biyu. Talba ya rumtse ido domin ya ji ciwon fado masa da tai.
 
“I knew it”
 
Kuka take masa sosai har wani maida numfashi take da karfi, Talba ya saka hannunsa a bayan hijabinta yana shafata ba tare da yace tai hakuri ba. Suna haka Ali ya dawo dakin, rike da tissue

Join Our Groups

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login