Showing 21001 words to 24000 words out of 332834 words

Chapter 8 - Bakar wasika Complete Hausa Novel

06 Oct 2024

65555

maimaita kalma”
 
“Baka san abun da ya faru ba”
 
“Bana son na sani”
 
Ya fada yana matsawa kusa da ita, kana kallon cikin idonsa ka san ransa ya bace. Sai da ta kalli Momy sannan ta kalli Baaba ta ce.
 
“Ki yi hakuri”
 
“Babu komai ya wuce”
 
Baaba ta fada sannan ta nufi kofar fita falon zuwa BQ inda dakinta yake. Sai da ta fice sannan Momy ta karaso inda Talba yake tsaye tana fadin.
 
 
“Wannan be kamata ba sam, taya zaka wulakanta yar'uwarka a gaban yar aikin?”
 
“Be kamata ta dauki hannu ta mareta ba Momy, no matter what Baaba tai mata, ta yi jika da ita”
 
“Gaskiya ka ci mutunci Leila, ka tauye mata hakki Talba, na yi shiru ne kawai saboda bana son na yi magana a gaban Baaba”
 
“Kin san inda na fito Momy? Gidan marayuna, yaran da suke can basu da uwa ba su da uba, wasu ma a titi aka dauko su aka kawo su nan, wasu kuma danginsu basa iya kula da su, amman Leila Allah ya ba ta komai, kudi, uwa, uba, ilmi, dukiya, sai dan na saka ta ba da hakuri ne zai zama cin mutunci?”
 
“Wannan kuma ai dabam ne, akwai tazara mai fadi mai tsawo tsakanin mai kudi da talaka, akwai abun da be kamata ayi agabansu ba, ko kuma a saka ayi musu, musamman inda muke da gaskiya”
 
“Wannan zarar da kike magana, ban tana ganinta ba, kuma ba zan taba ganinta ba, ban taba jin na fi wani dan yana talaka ina da arziki ba, sai dai na ji nafi shi saboda yana kasa da ni a aiki ko a shekaru, ko kuma saboda ni ina miji ita tana mata, amman ba zan taba iya cin mutuncin wanda ya haife ni ba, wasu talakawan sun fi mu a gurin Allah”
 
Yana gama fadar hakan ya nufi kofar fita a fusace. Momy ta bishi da kallo tana kada kai.
 
“Finally, gatan Daddynka ya saka har ni kana iya tsayawa ka fadawa magana... ”
 
Be juyo ba dan be ji akwai abun da zai sake ce mata. Balle kuma ta kuma ya kula Amal dake zayyana masa abun da ya faru daga can inda take tsaye.
 
“Ya Leila ce ta kawo mata ruwa shi ne, gurin mika mata carpet ya tadeta ruwan ya zuba a jikin Ya Leila sai ta mareta...Shi ne abun da ya faru Ya Talba ko baka tsaya ba na fada maka, Ya Leila ce bata da gaskiya”
 
Ta karasa ita da Leila suna watsawa juna harara, daman can haka suke kamar ba yan'uwa ba, basa shan inuwa daya.
 
 
 
________
 
Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai, muna da kwalli mai karfin gaske (Mujarrabun sadidan) Akwai na farin jini for yan mata da Zaurawa. Akwai wanda ba a bawa mai kishiya, akwai na mazajen da kr neman mata, muna da rantse baki da kishiya, muna da back to virgin, for yan matan da kaddara ta fadawa, ko Zaurawan dake son zama yan mata, akwai jigida mai kyau, muna da man ayu 100% natural. Akwai na maza masu hannun Dambe.
Hajiya sai n gwada akan san na kwarai, ba cuta ba cutarwa, duk wanda kika siya sai kin dawo.
 
 Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.
 
Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.
 
*💔 BAKAR WASIKA 💔*
 
 
By Khadeeja Candy
 
 
Page -7️⃣
 
Bayan Baba ya sauke wayar ya kalli Inna cikin yanayin damuwa yace.
 
“Bashiru ne yake mana maganar komawar mu can”
 
Inna ta girgiza kai.
 
“Babu inda zanje, ba a tserewa mutuwa a ko'ina take”
 
“Na san da haka amman dai ya kamata mu bar garin nan saboda ance akwai yiyuwar su dawo, kuma kina gani kullum mutane barin garin nan suke”
 
“Babu inda zanje Malam, na fi son mutuwata ta same ni a inda nake”
 
“Ai kaji matsalarki kenan, shi kansa abun da yake ta magana kenan a lallaba masa ke”
 
Inna bata sake cewa komai ba, har Baba ya ci ya shude. Duk abun da suke Aminatu na dama furar tana saurarensu, bayan ta gama ta kawo ma Inna ta zauna kusa da ita ta fara bata a hankali tana sha, Inna bata hana Aminatu shayar da ita ba, duk kuwa da kasancewar zata iya sha da kanta. Sai da ta tabbatar ta koshi sannan ta rufe furar ta koma gurin girkin da take. Har ta girka ta gama bata cikin walwala da sakewar zuciya, ba na rashin yan'uwa ba, na tunanin kalaman da Inna tai mata? Ta ya zata rayu babu Inna? A hannu waye zata zauna ma? Ba ita kadai ba Baba ma ya zai ji idan suka wayi gari babu Inna? Ko da ace tana da aure rayuwa ba zata taba mata dadi babu uwa ba, balle kuma a yanzu da take tare da ita, Saurayinta Maniru ma yana cikin mutanen da yan bindigar suka kashe, bayan ta gama ta zubawa Baba nasa ta zubawa Isah a inda ake saka masa sannan ta kwashe sauran a Samira babba, ta debi ruwa ta shiga bandaki. Sai da ta cire komai na jikinta sannan ta zauna saman dutsen da suke zama idan zasu yi wanka ta fashe da kuka.
Kuka tai sosai sannan tai wanka ta fito idonta a kumbure, ta dora alwala ta shiga dakinsu tai sallah, bayan ta gama ta d hannayenta sama tana rokon Allah.
 
“Ba ni da gata sai naka Allah, ka dauke yan'uwana a lokacin da ka so, ka sauya rayuwata zuwa yadda ka kaddara min, Allah ka yafe min ka jikan yan'uwana, ka ba mahaifiyata lafiya ka bar ni da ita Allah”
 
Ta karasa hawaye na sauko mata, sannan ta shafa addu'ar ta mike tsaye, ta fito waje, sai da ta zuba ma Inna ruwa a buta sannan ta rika ta, ta kaita bandaki bayan ta fito ta taimaka mata tai alwala sannan ta shimfida mata abun sallah.
 
“Allah ya miki albarka Auta”
 
Inna ta fada tana kokarin gyara zamanta, domin a zaune take sallah a yanzu. Aminatu ta kalleta kamar ba zata ce komai ba sai kuma ta amsa.
 
“Ameen”
 
Ta mike tsaye.
 
“Bari naje na yi itace yamma ta yi”
 
Kai kawai Inna ta daga mata, ita kuma ta shiga dakin ta dauko hijabinta ta saka ta ta dauki zaren da take daure itacen idan ta yi, sannan ta saka talkaminta ta fice, ba ita kadai ba kusan duk yan matan garin da ma matan aure suna zuwa daji ne su yi kara da yamma saboda dafa abinci, abu ne mai wahala ka ga gidan da ake siyen itace a yanki, yawanci duk a daji suke yin kara.
A da ta saba idan zata tafi yin kara akan biyo mata ko kuma ita ta biyawa wasu, sai dai tun bayan da aka tarwatsa rabin garin take tafiya ita kadai, saboda an tafi da wasu yan mata, wasu kuma sun yi gudun hijira, sauran da suka rage kadan ne. A gurin da ta saba tsayawa ta tsaya ta shimfida zanen sannan ta aje zaren a gefe, kana ta shiga tsintar karan, tana yi tana tuna yadda suke yi a da, ita da kawayenta, har tigengen suke cikin nishadi da walwala, sabanin yanzu da suka bar ta da kewa.
Sai da tai rabin sannan ta samu kanta da mugun faduwar gaba, marar misaltuwa, a take ta nade wanda ta tara a daure ta dauka ta nufo gida da gudunta, kowa sai kallonta yake, kamin ta iso har hawaye ya fara sauko mata, bakin kofa ta jefar da karan ta rugo da gudun gurin Inna da ke kwance tana bachi ta taba ta.
 
“Inna...Inna.... Inn”
 
Bata karasa ba, Inna ta bude idonta da sauri tana kallonta.
 
“Lafiya Auta?”
 
Sai ta fashe da kuka, wanda hakan yasa Inna ta tashi zaune.
 
“Tsoro nake ji Inna, gabana faduwa yake”
 
“Tsoron me? Miya faru?”
 
“Ban san ni ba, bana son na yi nisa da ke”
 
“Auta kenan, kin isa ki tare min mutuwa ne? Da wani na tarewa wani mutuwa ai da na tarewa Yayana, kin san babu uwar da za a kashewa yaya a gabanta kuma ta kyale alhalin tana da ikon yin wani abu?”
 
Maganar da Inna tai ya isa ya tabbatar da cewar ta fi jin bakincikin kashe mata yaya da akai fiye da keta mata haddi da aka yi. Aminatu ta yi kasa da kanta tana kuka sosai.
 
“Kina kuka da wuri, ki adana kukanki saboda gaba”
 
Ta kalleta.
 
“Miyasa kike min fatan kuka Inna?”
 
“Saboda zaki yi kuka mai yawa Aminatu, dole zaki yi kuka, ranar da zaki bude ido babu ni, ranar da zaki ga wata uwar idan kika tuna da taki dole ki yi kuka, ranar da kika ga wasu yan'uwa kika tuna da naki dole ki yi kuka, ranar da kika nemi wani abu kika rasa dole ki yi kuka, ni na riga na gama tawa rayuwar har na yi jikoki kuma na yi Auta, ke kuma yanzu rayuwarki take kan ginuwa, ta fara miki a haka, me kika tsammani a gaba? Dadi? Dadin yana tafe bayan wuya amman, yanzu na fi tausayin rayuwarki fiye da ta kowa Aminatu”
 
Ta share hawayenta, ta kara matsawa kusa da Inna ta kwanta jikinta, ta lumshe ido, tana maida numfashi a hankali.
 
“Allah ga yata, Allah ka zame mata gata”
 
Inna ta fada a ranta hawaye na sauko mata, ba tana kalamai ba ne domin ta daga mata hankali, a a har ga Allah tana fadin abun da take jin ya kusa tabbatuwa a gareta ne, kuma tana jin nata mai kiran ya kusa kiranta, jikinta da mafarkanta suna bata haka, domin tana jin wani kalar yanayi na dabam a jikinta wanda bata taba jin irinsa ba, sai dai a kusa? Ko a nesa? Yau ko anjima? Shi ne abun da bata da tabbaci.
Bayan sallah Magariba, Baba da Isah suna daki sun saka Inna a gaba suna ta kokarin convinced din Inna akan ta amince da magabar Bashiru su ma su yi hijira su bar garin amman ta ki, Aminatu kam tana zaune waje sai kallon hadarin dake haduwa take, ita kanta bata san na yi ba, tafiyar ko zaman? Inna tana da gaskiya idan sun tafi ba za su tserewa mutuwa ba, sai dai barin garin zai taimaka Inna ta manta wata damuwar, domin a cikin abubuwan da suke bata mata rai har da zaman gidan da take ganin an kashe yayanta kuma tana ganin a kowa ne dare kamar za su shigo ne su yi mata sallama kamar yadda suka saba, yadda rayuwa take a baya.
Sai da akai kiran sallah isha'i sannan Baba da Isah suka fito waje, sukai alwala suka yi haramar zuwa masallacin.
 
 
 
TALBA POV.
 
Ya kusan minti ashirin a cikin motar sannan ta fito, kamin ta bude motar ta shiga ma wani aiki ne, ba karamin kufula shi tai ba, domin ya tsani jira ya tsani a bata matsa lokaci.
Sai dai ko kadan be nuna mata ransa ya bace ba, ya ja motar suka fita fuskarsa ba yabo ba fallasa.
Mai gadin be yarda ya tsaya jiran sai Talba ya danna horn sannan ya bude masa ba, tun a lokacin da ya ga ya shiga motar yai hanzari bude gate din ya tsaya, be bar gurin ba har sai da motar Talba ta fice daga gidan.
Be kalli inda take ba, tukinsa kawai yake yana sauraren fm din dake gabatar da wani program, sai dai ita lokaci zuwa lokaci tana satar kallonsa, duk kuwa da kasancewar bata son su hada ido gudun kar ya ga tana kallonsa.
A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta lumshe ido ta bude ta maida dubanta gurin titi, ya zata yi ta canja Talba? Shine tambayar da ta zo mata a rai, gata a mota daya da shi amman baya nuna mata wata alamar kauna, Baya ma son kallon inda take kamar ba masoyinta ba.
 
“Na fasa zuwa shopping din take me home”
 
Sai a lokacin ya kalleta tare da kiran sunanta.
 
“Leila...”
 
Ta kalleshi Irin duban nan na fusata, sai dai kwarjininsa ya hanata nuna masa fushinta.
 
“I'm not your driver, and this should be the last time da zaki umarce akan wani abu”
 
“Amman ni dazun ka cilasta ni na bawa Baaba hakuri bayan kuma bata cancanci haka ba”
 
Ta fada idonta na cika da kwalla.
 
“Me ka dauke ni ne Talba? Baiwa?”
 
Be amsa ta ba, ya juya motar zuwa gida, kamin su isa hawaye da ya wanke mata fuska ya fi a kirga, yana yin farkin ta bude motar ta fita tana share hawayenta. Sai a lokacin ya juyo da fuskarsa yana kallonta har ta danna door bell din aka bude mata ta shige, sannan ya maida dubansa gurin Daddy dake tsaye jikin motarsa yana magana da Momy da gaba daya hankalinsu yake kan Talba.
Bude motar yai ya fito ya rufe ya nufi gurin da Daddy yake tsaye yana wata irin tafiya kamar baya son taka kasa, kamin ya karasa ya zuba hannayensa aljihu kana ya sadda kansa kasa.
 
“Ranka ya dade baka burge ni ba, da baka tura Leila gida gurin Gwaggo ba”
 
Daddy ya fada yana kallon dansa, sai Talba ya kalli Daddy, kamin ya maida dubansa gurin Momy wanda hakan kr tabbatar masa da cewar Momy ta fadawa Daddy abun da yai ma Leila kenan.
 
“Momy ba zamu iya yin abu a tsakaninmu ba har sai Daddy ya ji?”
 
“Yes, ya kamata ya ji ne, saboda kana kokarin wuce guri”
 
“Just because...”
 
“It's just because? Tun ba yau ba Talba kana treating Leila kamar ba yar gidan nan ba, ya kamata ka sani ita ma tana da right fa!”
 
“Miyasa karamin Abu zai bata miki rai Momy?”
 
“Kai kaja komai, wacan yar aikin ma dana kora saboda kai na koreta Talba, saboda kana nuna kamar ta fi Leila gata a gidan nan, and now kana son na kori Baaba ko? Ka cigaba”
 
Tana kaiwa nan ta nufi hanyar da zata sadata da bangarenta, daga Daddy har Talba kallonta suke har ta shige, sannan Daddy Talba ya ce.
 
“Ka saba da halin Momy ka ba tun yau ba, kar hakan ya dame ka”
 
Talba yayi murmushi.
 
“Daddy fita zaka yi?”
 
“Yeah zan je gaisuwar Galadima ne”
 
“Lemme drive you”
 
“No tare da direba zamu je, go and rest”
 
Murmushi ya sake yi ya dan ja baya, ya budewa Daddy motar sai Daddy ya shiga yana fadin.
 
“Ance an kai hari Galadi, ya kamata A shirya wani abu a kai musu, mutanen nan suna cikin matsi”
 
“Inshallah Daddy, ban ji ba two days ban duba news ba”
 
“Sai na dawo”
 
“Allah ya kiyaye”
 
Ya fada yana rufe masa motar, sannan yaja ya tsaya har sai da driver ya ja motar Daddy suka fice daga gidan. Sannan ya nufi bangarensa, daga shi har Faruq da part dinsa yake kusa da nasa a kasa dakunansu suke, tsabanin bangaren Daddy da Momy da akai yi ma upstairs.
 Dakin da yake aje tardunsa ya nufa ya bude ya shiga cikin natsuwa ya zauna a kujera ya bude system dinsa ya cigaba da wani aikin da be karasa ba, be bar dakin ba sai kusan 6pm.
 Freezer ya nufa ya bude ya dauko ruwa ya zuba a cup ya surka da wasu sannan ya sha, bayan ya ajr cup din ya nufo kofar fita yana duba agogon hannunsa. Kai tsaye bangaren Momy ya nufa domin ya san izuwa yanzu ta huce fushin da take. Door bell din ya danna, yana dauke hannunsa Amal ta bude masa da sauri hawaye na sauko mata.
 
“Lil Sis?”
 
“Na'am?”
 
“Me ya same ki?”
 
Ya tambaya a yayinda ya saka kafarsa cikin falon yana dubanta.
 
“Baaba ce...”
 
Sai kuma tai shiru, shi dai kallonta kawai yake, as she knows ba zai sake tambayarta ba sai ta soma labarta.
 
“Tana mopping sai ruwa ya zame ta ta fado...”
 
Wani irin kallo tsoro yai mata.
 
“Ta fado ina?”
 
“Daga sama ta fado kasa!”
 
“You're kidding me”
 
“No Wallahi da gaske nake”
 
“Ina take? Ta ji ciwo?”
 
“Momy ta dauke ta sun tafi asibiti tare da Ya Leila tun dazu ba su dawo ba”
 
“Yaushe abun ya faru?”
 
“Lokacin da Daddy ya fita”
 
Ya juya da sauri ya fita zuwa bangarensa domin a can ya baro wayarsa, yana shiga ya koma dakin karatunsa ya dauki wayar ya kira Momy, ringing tai sai da ta kusa tsinkewa sannan ta daga.
 
“Momy kuna ina?”
 
“Gamu hanyar dawowa gida”
 
“Ina Baaba?”
 
Dan Jimm Momy tai kamin ta amsa masa.
 
“Yaranta sun zo sun dauketa, sun tafi da ita, daman ciwon ba sosai ba ne”
 
“Amman...”
 
Be karasa ya lumshe idonsa sosai jin Momy ta katse wayar, hakan nan jikinsa ya ba shi kamar ba iya haka ba ne. Idan har ba babban abu ba ne, babu yadda za ayi Momy ta kaita asibiti da kanta, kuma har Leila ta bi ta su tafi tare.
 
 
 
AMINATU POV.
 
Tun safe take ta wanke tufafin Baba da nata har kusan daya da tabi, abun ka da marar aiki da kuzari, bata da kuiyar aiki kam amman bata da sauri, sai wuni ta kwana tana abu daya.
Bayan ta wanke su fes ta matse ya daurewa ta soma sha shayawa, sannan ta bi tana kwashe wadanda ta shanya da farko suka bushe tana ninkewa, sai ta dora akai da haka har ta gama kwashe ta kai su daki, sannan ta fito ta shanya sauran. Ta dauke kayan da tai aikin da su cike da gajiya ta aje a inda suka saba ajewa.
 
“Inna tashi ki yi sallah”
 
Ta fada tana doso dakin, har zata shiga sai kuma ta juya ta dauki butar Inna ta cika da ruwa sannan ta nufo dakin, bata sake ce ma Inna komai ba har sai da jera tufafin Baba a inda ta saba saka masa sannan ta nufo inda Inna take zaune ta sadda kai kasa ta.
 
“Inna...”
 
Jin bata amsa ba yasa ta risina a hankali ta leketa, sai ta ga idonta a rufe, da sauri ta taba ta abunka da wanda yai nisan bachi sai ta zabura da karfi ta bude ido, da wanin irin karfi Aminatu ta hade yawu ta sauke ajiyar zuciya.
 
“Inna anyi sallah, yi hakuri na tashe ki da karfi tsoro na

Join Our Groups

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login