Showing 81001 words to 84000 words out of 332834 words

Chapter 28 - Bakar wasika Complete Hausa Novel

06 Oct 2024

65626

ya fito ya ja motar da karfi, suna ganin ya kunna motar suka bude masa gate. Cikin saurin ya fice daga gidan, yana driving zuciyarsa na raya masa Leila zata iya yin yunkurin kashe yarinyar saboda ta tambayi Ali akan ta, wata kila zata iya zargin wani abu ne a tsakaninsu idan ma bata yi da kanta ba zata iya saka wani yai.
Yana isa asibitin ya faka motarsa ya fito ya mufi hanyar da zata sada shi da office din Ali, kamin ya karasa Office din Ali ya fito daga ward din, yayi mamakin ganin Talba sai dai kamin yace komai Talba ya ce.
 
“Ali ya yarinyar take?”
 
“Ba dadi, but she's still alive”
 
Wani deep breath Talba yai sannan ya bude office din suka shiga.
 
“Ya akai abun ya faru?”
 
Ali ya rufe kofar yana fadin.
 
“Nurse Karima dai ta fada min cewar tana shiga dakin ta same ta a sume, robar a zagaye da wuyanta kuma an fisge robar hannunta jini ya zuba, yanzu haka sai da muka saka mata robar jini, daman jinin be isheta ba”
 
Talba ya zauna saman kujera yana dan tunani kaminnya kalli Ali daya kai hannu ya dauki wayarsa yana dubawa.
 
“Ali lokacin da Leila take tambayarka akan yarinyar nan ta tambaye inda take?”
 
“Tace dai wace yarinya ce na fada mata tana asibitin mu”
 
“Ka fada mata number dakin?”
 
Alinya dago ya kalleshi.
 
“No miya faru?”
 
“Ali Leila can do this yarinyar nan bata da zuciya mai kyau....”
 
“Noooooooooooooooo”
 
Ali yayi saurin dakatar da shi yana daga masa hannu, domin maganar ta masa nauyi sosai har sai da ya runtse ido ya bude ya kalleshi.
 
“Look Talba yanzu na fahimci baka son Leila, and it fine, ka ji baka son mutum normal ne amman kokarin dora mata sheri ba zai amfana maka komai ba”
 
“Na san dalilin daya saka na fad....”
 
Talba be kasara Ali ya daka masa tsawa.
 
“Baka da wani dalili, and karka manta Leila yar'uwarka ce ko da babu alakar kauna a tsakaninku be kamata ka jefe ta da wannan ba”
 
“Ali ba zaka gane ba ne, Leila can do this”
 
Talba ya sake maimaitawa with full confidence, abun da ya kara fusata Ali.
 
“Enough Talba, enough. Leila tana da damar da zata yi kishi, ta nuna bakincikinta ko bacin rai akan ka damu da wata, amman for now ka bar Leila ta ji da damuwarka karka kara mata wata”
 
Ali ya fada cikin tsawa jijiyar wuyansa har tashi take. Talba ya mike tsaye yana kallon Ali cikin wani irin zafin nama.
 
“So you're shouting at me...?”
 
“Yes me ke damunka Talba? Why Leila? What if ita tai kokarin kashe kanta? What if kila ta akan wani abu dabam ake kokarin kasheta?”
 
Talba ya matsa kusa da shi yana kallon idonsa.
 
“Don't fool me, haka nan kawai zata yi kokarin kashe kanta saboda bata son kanta? Bayan ta samu ta fito daga daji? And you already told me babu wanda ya taba zuwa ganinta how could someone know tana a nan? Ali Let me tell you this, zan bincike yarinyar nan and if i find out Leila ta aikata abun nan, sai na bata mamaki”
 
“And before you do this let me show you something, daga yau ba zan sake kula yarinyar nan ba, and i swear sai ta bar asibitin nan yau, ba zan zuba maka ido ka bata alakarka da matar da zaka aura ba kuma yar'uwarka saboda wata bare ba, kuma a dalilina ka san yarinyar nan and now na fahimci halin da Leila take ciki akanka”
 
Talba yayi murmushi irin murmushin na bacin rai da mamaki a lokaci daya.
 
“And remember you said yarinyar bata da kowa”
 
“I don't care, idan ma mutuwa zata yi tai mutu, she's not my responsibility...”
 
“And for now on she's my responsibility har sai ta dawo hayyacinta ta fada min komai... And believe me with or without you yarinyar nan zata rayu Doctor Aliyu Muhammad Bukar...”
 
Talba na fadar hakan ya juya ya nufi kofa a mugun fusace, da mugun karfi yake taka kasar kamar zai fasata tsabar bacin rai, rabon da ya samu kansa cikin irin wannan bacin rai har ya manta. Har ya fito daga ward din sai kuma ya juya ya koma ciki, kai tsaye ya nufi gurin da sauran nurses din suke, mostly sun sanshi domin yana yawan zuwa asibitin gurin Ali kuma gashi sanannen mutum kuma dan babban mutum wato Alhaji Mu'azu Shimkafi, sai dai ba zai iya shadar sunansu duka ba musamman a yau da yake weekend ne ba faces din daya sani ba ne a gurin.  
 
“Who's Karima a nan?”
 
“Ni ce”
 
Ta amsa tana kallonsa.
 
“Ali ya ce ki dauko yarinyar ki saka a motana zan canja mata asibiti”
 
“Okay”
 
Ta mike tsaye ta kira mutun biyu da za su rika mata ita, a gurin ya tsaya har aka fito da ita suka turota a kujera idonta a rufe. Yana gaba suna Karima na biye da shi wata mai aikin shara da dauko files tana rike da file din Aminatu, suna isa gurin Motar Talba ya bude gidan bayan Nurse din da matar suka rikata suka sakata ciki sannan suka rufe motar. Shi kuma ya karbi file din ya bude side dinsa ya shiga ya aje file din a front seat, hakan kawai ya samu kansa da juyawa ya kalli fuskarta, sai tausayinta ya kara kama shi, abun da Ali ya fada masa akanta ya dawo masa, ga kuma wanda yake tunanin Leila na kokarin kara mata.
 
“Leila...”
 
Ya furta bayan a dauke kansa daga barin kallon Aminatu, yana jin tsanar Leila na kokarin dasuwa a ransa. Key yai ma motar yai reverse, ya kama hanyar ficewa daga asibitin.
 Wata expensive private hospital ya nufa da ita, yana shiga ya nufi emergency, duk da kasancewar yau weekend ne ya samu ma'aikata da yawa a asibitin saboda private hospital ce da suka san aikinsu, sai dai ba kowa yake iya kai kansa ko wani nasa a can ba, sai ya tsaya da kafafuwansa.
Sun karbi Aminatu da gaggauwa da kuma kulawa suka shiga da ita ciki domin bata taimakon da take bukata.
Shi kuma ya tsaya daga waje ya ciro wayarsa dake aljihunsa tana ringing, ganin number Daddy yasa shi saurin picking.
 
“Hello Daddy”
 
“Mu'az kana ina? Mun ci abincin rana ba tare da kai ba?”
 
Ya daga jikin motarsa yana kallon harabar asibitin.
 
“Daddy ina asibiti”
 
Sometimes idan yana gurin Ali a asibitin ya kan cewa Daddy yana asibiti, hakan yasa Daddy yai zaton ko yana tare da Ali ne?
 
“An bata maka rai ne? Could we talk?”
 
“No Daddy ina wata magana ne mai muhimmanci, bata shafe ka tsakanina ne da Ali”
 
“Okay”
 
Daddy ya fada sannan ya kashe wayar, Talba ya cikawa bakinsa iska ya busar a hankali yana kallon Nurse din data doso inda yake.
 
“Dan Allah kai ne mijin yarinyar nan? Ko dan'uwanta?”
 
Tsaye Talba yai kamar an dasa shi ya kasa amsa mata.
 
“Tana bukatar jini da gaggauwa”
 
“A ina zamu samu?”
 
“Lab amman for now za mu bincika mu ga ko za'a samu jinin da zai dace da nata”
 
Ya gyada mata kai a hankali cike da natsuwa, sannan ya bi bayanta suka nufi cikin ward din, ita ta nuna masa dakin da suka saka Aminatu. Ita ta fara shiga shi kuma ya bi bayanta ya tsaya jikin kofar yana kallon fuskar Aminatu dake ta bachi kana gani kasan bata san inda take ba. Nurse din ta yi abun da zata yi ta fita Talba yana tsaye jikin kofar idonta akan Aminatu, takawa yai a hankali ya karasa kusa da gadonta still ya kasa kauda idonsa akanta.
 
“You need to survive”
 
Ya furta yana jin kamar ya tashe ta ya tambaye ta waya mata haka, kuma ayi sa'a ta amsa masa cewar Leila ce. Yana tsaye akanta har na kusan mintuna talati, sai ga nurse din ta dawo tare da likitan daya karbi Aminatu a dazun.
 Sake dubawa yai sannan ya kalli Talba.
 
“Ba mu da kalar jininta a yanzu, sai kaje babbar asibiti ko kuma ka samu wani daga familynta idan zai iya bada jinin”
 
Uffan Talba be ce ba har sai da Likitan ya nufi kofar fita.
 
“Ko zaka iya gwada nawa? O ne”
 
Likitan ya juyo ya kalleshi.
 
“Yes why not amman zamu fara maka test mu tabbatar baka dauke da kowace irin cuta gudun samun matsala”
 
Ya daga masa kai kamar an masa dole, sannan ya bi bayan Nurse din dake nuna masa kofa.
 
“Bismillah Malam”
 
 
 
LEILA POV.
 
Wani irin kuka take wanda ita kanta ba zata iya fadar dalinlinta na yin kukan a yanzu ba, na zargin da Talba yake mata ne ko kuma na laifin ne da yake kokarin dora mata? Taya zai zarge da da abun da bata san wanzuwarsa ba? Miyasa ma zai yi maganar wata yarinyar a gabanta? Ko kuma dai tana kukan ne saboda zuwan Shamsu? For now she can't tell, all what she know is dukansu is painful, daga zargin har zuwan Shamsu har zancen yarinyar da Talba yake.
 
“Tun dazun kike ta kukan nan? Haka zaki yi ta yi a gaban mutane ki daure kanki?”
 
Momy ta fada cike da tausayin yarta.
 
“Wai wace yarinya ce ma yake magana akai?”
 
A take ta amsawa Momy hawaye ma sauko matan
 
“Wata ce, wata yar gudun hijira ce”
 
“Yar gudun hijira kuma? Shine har zai zarge ki da kashe ta? Ke kin santa ne?”
 
Ta daga kai tana goge hancinta.
 
“Na santa amman Wallahi ban ma taba ganinta balle har na yai yunkurin kasheta? Miyasa zai zarge ni?”
 
“Ke kika bashi fuska ai! Kina ta son bada kofar da za a zarge ki, koma dai miye ai be kamata yai wannan tunanin ba, and ko da kin aikata be kamata ya sameki kai tsaye da maganar ba!”
 
Momy ta fada a fusace, sannan ta mike tsaye yana wani kashe ido.
 
“Karki fito cin abinci, saboda Daddynku zai tambaye dalilin danuwarki, so ki zauna a nan zan fada masa kanki yana ciwo”
 
Leila ta daga kai, sai Momy ta juya ta fice daga dakin tana mamakin yadda Talba yake son sauyawa.
after like 40 minutes da fitar Momy wayar Leila tai ringing, hannu ta kai ta dauka tana duba number Ali dake kiranta, da kamar ba zata daga ba sai kuma ta daga wayar ta kara a kunnenta tai shiru tana sauraren abun da zai fito daga bakinsa.
 
“Kuka kike yi ko?”
 
Ta daga masa kai kamar yana gabanta, wasu hawayen na sauko mata. Be damu da yaji abun da zata fada ya sauke ajiyar zuciya daga can cikin wayar.
 
“I know na san abun da ya faru, can we talk? Gani a hanyar gidanku akwai maganar da nake son fada miki, please ki daure ki fito zan tsaya a gate”
 
“Okay”
 
Ta amsa masa tana jin wani sabon kuka na taso mata, sannan ta aje wayar ya lumshe ido, fuskar Baaba ce ta fara mata gizo, hakan yasa tai saurin bude idon ta mike tsaye ta nufi gurin windows din dakinta dafe kai wasu hawaye na sauko mata.
 
*Khadeeja Candy*
 

Ko kin san kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin sa kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya domin siye ko sari ku tuntu Ramla incense ta wannan number +234 703 839 2576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa
 
*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min! Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*
 
Madina ta jimmm bayan da Leila ta gama labarta mata abun da ya faru, gaba daya sai ta ji jikinta ya mutu.
 
“Yanzu dai ki fita ki ji abun da Ali zai fada miki”
 
“Zan je yanzu”
 
“Ki kwantar da hankalinki komai zai wuce, amman da zaki dauki shawarata da kin fadawa Talba gaskiyar komai, barin kashi a ciki baya maganin yunwa Leila, kuma yanzu zaki yi ta samun rashim fahimta a tsakaninku ne”
 
“Madina wannan sirina ne, Momy ma bata san na fada miki ba, amman na fada miki ne saboda na yarda da ke”
 
“Babu wanda zai taba jin wannan maganar daga gareni Leila, amman ina baki shawara ne akan abun da nake ganin zai zame miki masalaha”
 
“Yanzu dai bari na tafi Ali yana jirana”
 
“Okay”
 
Leila ta aje wayar sannan ta sauka saman gadon ta dauki wani karamin mayafi ta rufe kanta, sannan ta saka talkaminta ta nufi kofar fita idonta a kumbure saboda kukan da ta sha.
Ko da ta sauko falon babu kowa, dukansu suna bangaren Daddy, yan aikin Momy kuma Momy bata basu damar zama a falonta hakan yasa idan ba wani aikin zasu ba abu ne mai wahala ka gansu a main house din kullum suna BQ. A hankali ya bude kofar falon ta fita gabanta na faduwa, domin ji take kamar zata yi arba da Talba ne, domin a yanzu bata son ganin fuskarsa, ba dan bacin rai ba sai dan bata da amsar tambayar da zai mata. Tun kamin ta karasa gurin gate din police din ta bude mata karamar kofar ta fice, tana fitowa ta ga motar Ali fake sai ta nufi inda motar take. Ali na zaune cikin motar yana kallonta har ta karaso gaba daya sai ya ji tausayinta ya kama shi, a da can yana bata laifi kamar yadda yake bawa abokinsa sai dai a yanzu ya fahimci abokinsa ne mai matsala ba ita ba. Bude motar tai ta shiga sannan ta rufe ta kalleshi da idonta da suka kumbura.
 
“Ali”
 
Sai da ya sauke wani dogon numfashi sannan ya amsa mata.
 
“Na'am Leila, ya kike?”
 
Tambayar ya take da yai sai ta ji kamar ya tsokano mata kukanta, a take hawaye ya cika idonta.
 
“Ba Kalau ba Ali, ba Kalau ba”
 
“Na sani, abokina yayi rashin tunani, amman ban dauka zai miki magana ba, a thought ya bar abun a ransa ne kawai, sai dai faga lokacin dana kira ki na ji yanayinki, sai tausayinki ya kama ni, and now na fahimci irin halin da kike ciki”
 
Ya karasa yana kai hannu ya ciro tissue ya mika mata, sai ta karba ta share hawayenta.
 
“Sometimes ina kasa fahimtar waye Talba, abokinka yana da wahalar sha'ani Ali, taya wanda zaka aura zai zarge ka da kisa? How? And Why? Saboda na nuna kishina? Talba be dadin zama wani lokacin”
 
“Na sani, amman ban dauka abun zai kaishi haka ba”
 
Cewar Ali yana kallonta gaba daya zuciyarsa ta cika da tausayinta, domin gani yake Talba baya sonta ita ce kawai sonsa ke dawainiya da ita.
 
“And i respect your decision na cewar ba zaki auri Talba ba har sai ya canja”
 
Juyowa tai ta kalleshi da kyau.
 
“Dan Allah zaka fada min abun da ta faru da yarinyar?”
 
A takaice ya labarta mata komai na yadda aka samu yarinyar, sai dai be fada mata cewar Talba ya dauke ta daga asibitin ba, haka ma be fada mata cewar sun samu tsabani ba, domin yana ganin kamar sirrinsa ne da be kamata kowa ya ji ba.
 
“Amman me zai saka wani yai mata haka?”
 
“Ni ma ban sani ba, kuma a iya binciken da na yi wani be shigo ba, so dole dai sai ta farka zata iya fada mana yadda komai ya faru”
 
“Yanzu tana asibitinku?”
 
“No na canja mata asibiti, and i am here to apologize saboda ni na janyo komai, Talba be san yarinyar nan ba, ni na hada shi da ita da neman ya taimaka mata saboda yarinyar tana bukatar taimako, amman ban yi tunanin abun zai zama na rigima haka ba”
 
“Baka da laifi, na san ka yi ne da kyakkyawar niya, be kamata ka bada hakuri ba”
 
Yayi shiru na wani lokacin kamin ya kalleta ya ce.
 
“Amman Leila kin yi wani abun ne da zai saka Talba ya zargeki da taba yarinyar nan?”
 
“Ban yi komai ba, amman kasan a gurin abokinka kullum nice mai laifi, kawai dai na fahimci wani abu... Talba baya so na ni ce kawai na mutu da kaunarsa, wanda yake sonka ba zai maka haka ba, ko da gaske na aikata zai nemi hanyar kare ni ne, ba ya tunkare da wannan laifi mai girma ba, abun akwai ciwo”
 
Ta karasa wasu hawaye masu zafi na sauko mata, har cikin ranta tana fadawa Ali abunda ta fahimta ne akan zamantakewarta da Talba. Ali ya kawar dai yana jin irin tausayinta na kara kamashi.
 
“Ada can na dauka miskilancinsa ne ya saka yake min abun da yake min, amman a yanzu na fahimci kauna ta ce babu abunsa, kawai ya amince ne saboda ba zai iya cewa Daddy a a ba”
 
Ta runtse tana kokarin fashewa da kuka.
 
“Kabir yana da fada min gaskiya amman na kasa ganewa, saboda kaunar Talba ta cika min zuciya amman yanzu na fahimta...”
 
Ali yayi saurin daukar ruwan dake cikin motarsa ya mika mata.
 
“Please sha ruwa”
 
Sai kuma ya dauko tissue ya mika mata.
 
“Ki daina damuwa dan Allah, kukan nan yayi yawa idonki har ya kumbura, me yasa zaki damar kanki akan Namiji?”
 
Sai ta kalleshi hawaye na sauko mata
 
“Talba be taba min haka ba, na gode”
 
Ta fada sannan ta karba ya share hawayenta ta bude ruwan ta sha.
 
“Ki je ki huta, karki saka damuwar komai a ranki komai zai wuce, kin san idan ya fusata yana aikata abubuwa amman zai sauko and ina tabbatar miki zai baki hakuri”
 
Ta dan yi murmushi irin na bakinciki da kuma kin yarda da maganar Ali cewar zai bata hakuri domin ta san waye Talba, sai dai bata ce masa komai ta bude motar ta fita, Ali ya bita da kallo cike da tausayi har ta shige cikin gidan, sannan ya kai hannu ya dauki wayarsa dake carji a jikin motar ya kira Talba, wayar tai ta ringing har ta gaji ta katse be daga ba ya sake kiransa nan ma shiru, haka ya jera masa kusan 4 miss calls a na biyar ya ji wayar a kashe alamar ya gaji da kiran da yake masa kenan kuma ba zai yi picking ba.
 
“Talba....”
 
Ali ya fada yana jin kamar ace yana kusa da shi yai masa dan banzan duka a yau saboda kukan da Leila ta sha akasa.
 
‘Ina ka kai yarinyar nan?’
 
Shine sakon daya tura masa sannan yai reverse ya kama hanyar gidansa.
 
 
TALBA POV.
 
Be dawo gidan ba sai dare, domin

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login