Showing 15001 words to 18000 words out of 332834 words
ma wata rana uwar wasu ce, kuma yaranta ba za su dauki abun da kake mata ba, kamar yadda a yanzu kake jin rashin dadi, and tell me, you take your Mom side”
Talba ya sake yin murmushi.
“No Daddy kullum ai ina side dinka, amman dai ina son Momy ta daina bacin rai please”
“Shikenan zan kirata ta zo nan na bata hakuri”
“No Daddy ka tafi dakinta mana, zata fi daukar abun da muhimmanci Please”
Daddy ya masa kallon mamaki.
“So that's mean kasan yadda ake lallaba mace, duk abun da kake yi da gangan kake yi kenan?”
Talba ya mike tsaye yana dariya kamar ba shi ba, Daddy ma murmushi yai mai sauti yana binsa da kallo cike da kauna irin ta Uba da D'a.
Bangaren Momy ya dawo, kai tsaye ya nufo dakin Leila, be tsaya knocking ba ya tura kawai ya shiga, sai ya same ta zauna gaban mirror tana duba fuskarka. Tsaye yai cak kamar an dasa shi, ta ina zai fara? Me zai ce mata? Sorry? Shi da kansa? Yace mata sorry? After ta kira shi wani? Taya ma zai ce mata haka? For the sake of Daddy, wata zuciyar ta raya masa, but duk da haka be jin zai iya ce mata sorry.
“Idan wani abu ya faru a tsakaninmu, ki bar shi a tsakaninmu ba zai wani ya ji ba”
Ya fada sannan ya juya, sai kuma ya juyo.
“And if you need something, lemme know”
Yana fadar hakan ya juya ya fice ba tare da ya rufe mata kofar ba. Tabe baki tai ta mike tsaye ta isa gurin kofar ta rufe ta juyo ta dawo gaban madubin ta zauna. Har ga Allah tana son Talba, kuma ta san yana sonta amman abun da yake mata is yayi yawa, girman kansa da jin kansa yayi yawa, that's why dazun ta fadawa Daddy cewar bata shirya aurensa a yanzu ba sai nan gaba, Momy kuma ta goya mata baya ganin kullum ita ake kwaruwa, but this time around Momy ta goyi bayanta.
Jin wayarta ta yi kara alamar sako yasa ta mike tsaye ta isa gurin da wayar take ta dauka ta duba sakon.
“Good Night”
Shine rubuce da number Talba, ba shiri ta zauna tana mamaki. Da gaske shi ne ya turo mata sakon ko wani dai? Dan murmushi.
“Duk sai na rama abun da kai min, it's my turn”
Ta fada tana jin wani irin dadi, juya ido tai.
“Ya kamata ya san ina da tsada”
Ta fada sannan ta kwanta saman gadon.
*** *** ***
Kamar jiya Saturday, yau kuma Sunday, kowa yana zaune a teburin cin abinci ban da Daddy da zai karya bangarensa da kuma Leila da take dakinta.
“Ina Leila?”
Talba ya tambaya yana kallon Amal.
“Tace zai ba zata fito ba”
“Why?”
“Just”
“Hada nata breakfast din na kai mata dakinta”
Ba Momy da Kabir ba, ko Amal har Baaba mai aikinsu sai da ta kalleshi.
“Kamar dai ba kai Talba”
Kabir ya fada, sai Talba yayi murmushi kadan.
“Sounds funny, right?”
“No sounds new”
Momy ta yi murmushi.
“Ban fada muku ba? Wata rana Talba zai canja”
Ya mike tsaye ya shiga hada ma Leila nata abun karyawa.
“I didn't change, ina yi ne for the sake of you and Daddy”
“So na dan ra'ayin kanka kake ba, kenan baka farinciki da abun da kake, doesn't make sense”
Kabir ya fada yana tabe baki. Talba dai be sake ce masa komai ba har ya cirewa Leila komai ya dauka ya nufi upstairs. Amal ta mike da sauri ta bi bayansa ta rigashi karasawa gurin kofar ta bude masa saboda hannayensa duka biyu suna dauke da abu ne. Yana shiga Amal ya janyo kofar ta rufe, har gefen gadonta ya aje mata komai sannan ya dago ya kalleta.
“Good Morning”
Ya sake gaisheta duk da kasancewar ya aika mata da sakon gaisuwa da safe kuma bata masa reply ba, which is pain her. Bata amsa masa ba sai kallonsa take.
“Ga breakfast dinki, idan kina bukatar wani abu ki fada min”
Yana fadar hakan ya juya, sai da ya kusa isa kofa sannan ta ce.
“Anjima zaka kai ni shopping”
“Idan kin shirya ki kirani”
Ya fada ba tare da juyo ba, sannan ya fice ya ja mata kofar. Yana saukowa downstairs be koma dinning din ba sai ya nufi kofar fita, yana fitowa ya tsaya bakin kofar falon ya kira Ali. Kamin Ali yai picking Kabir ya fito ya tsaya daidai inda yake tsaye.
“Kasan mi ye Talba?”
Talba ya kalleshi yana kokarin yanke kiran Ali da yake.
“Kai dan'uwana ne, ba zan so ka cutu ba, kamar yadda ba zan so Leila ta samu matsala, ni shawarar da zan baka karka auri macen da baka so, domin zaku yi ta samun matsala ne kawai, ji abun da kake yi a yanzu saboda Momy da Daddy kake yi ba wai dan ka faranta ranta ba, kuma ba dan kana so ba, hakan kuma zai haifar da kiyayya da tsana a tsakaninku”
Talba ta saka wayar aljihu yana kallon Kabir.
“Ina sonta Kabir...”
“No, maybe dai kana sonta saboda baka san miye so ba, ko kuma kana sonta saboda baka son ka bawa Daddy kunya, ko kuma kana sonta saboda kana son ka yi aure, amman na san wata rana zuciyarka zata so wata wata kila Leila ce ko wata dabam, a lokacin da zata maka laifi kuma na bata hakuri Wallahi baka ko sani ba, wanda zaka so faranta mata a karan kanka, idan tana cikin damuwa kai ta kokarin ganin ka cireta, idan tana kuka karika jin hawayenta kamar mutuwarka ne, duk wannan shan kunun da kake yi ita zaka sake mata ka rika neman tai maka murmushi kana mata dariya, idan zuciyarka ta fara wannan son, duk son da biyayyar da kake yi ma Daddy ko Momy idan suka muzantata sai ka ji ba dadi kamar kai aka yi ma, daga lokacin ne rayuwarka zata fara canjawa...”
“Noo Kabir, you know i don't believe in love, so wannan daren ba zai taba zuwa ba balle har na kwanta na yi wannan kalar mafarkin, ku ne da kuke karance karance da kallo fina finai kuke dauka irin wannan soyayya gaskiya ce, even if gaskiya ce ma ni bana cikin irin wadannanhawayen mazan...”
Yana fadar hakan ya fara sauka entrance din. Kabir ya bishi da kallo yana murmushi.
AMINATU POV.
Sai da haske ya fara bayyana sannan mutane suka leko gidan, duk da kasancewar kowa yana fama da nasa jimamin. Duk wanda ya shigo ya tararda gawar su Amadu sai ya zubar da hawaye, daman can kowa ya saka ran sai ayi musu ta'asar da tafi ta kowa saboda suna da yan sa-kai har biyu da da barayin yankin suke matukar tsoronsu, domin basa yi ma barayi da sauki musamman idan sun hadu da su a wani gurin. Da taimakon yan tsirarun garin da suka rage aka dauko zage aka rufe gawarsu, Sanusi kuma aka dauke shi kan babur zuwa babbar asibitin shimkafi, a lokacin ne Inna ta fahimci har da Musa aka kashe, kuma aka tafi da matansa biyu bayan matar matar Amadu, cikin yaranta da suka tsira Aminatu ce kawai ita ma dan ba su ganta ba ne, sai kuma Isa da ya tafi kai Baba gurin ganin Gwaggonsu, sai kuma Bashiru dake kasuwancinsa a birni tare da iyalansa.
Karfe bakwai da yan mintuna Baba ya iso cikin gidan, domin labarin abun da ya faru ya same shi a can garin da yake gurin kanwarsa, yana shigowa cikin gidan ya kasa rike kansa, tsayi ma ya kasa duk da kasancewarsa namiji sai gashi ya zube kasa yana kuka da idonsa, Inna kam zaune kawai take tana kallon komai, hawayen sun dauke mata. Da dai daya Baba ya fara bin gawar yayansa har hudu yana dubawa, Isah ma kuka yake sosai, ya ga Amadu da ka fashewa kai, sai kuma Rilwanu, da aka takewa wuya da babur, haka Musa na da dutse aka fashe masa kai. Iro kam gawarsa bata wuce ta karamin jariri ba domin gawarsa ta kone kurmus daker aka samu aka hada dan abun da yai saura gudu daya aka lullube da zanen Inna.
Baba ta fadi zaune ya fashe da wani irin kuka yana dora hannu saman kai.
“Allah ka hana zalinci, Allah ka sani mutanen nan ba mu musu komai ba, Allah ka isar mana”
Baba ya fada cikin wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya, sai kuma ya juyo ya kalli dansa Isah da shi ma kukan yake ya ce.
“Isah ka gani an kashe an yan'uwanka...”
Daga inda Inna take zaune ta amsa.
“An kashe su Malam, d'a hudu, ni na haifi yarana kuma a gaban idona aka kashesu, yaran da ba su wuce sa'an yayana ba suka keta min haddi har su goma sha daya, a gaban yata, suka kone muna abinci, suka kora mana dabbobi, saboda kawai zalinci, titin kwarai ba mu da shi a garin nan, ba mu damu da cigaban zamani ba, taki ma sai an ga dama a bamu, duk wani cigaba ko aikin taimako ba mu san shi ba, da hakkinmu muke tara komai, yanzu kuma zaman lafiya da farinciki ya gagaremu...”
Inna na gama fadar hakan ta mike tsaye da sauri jin kamar numfashinta zai fita, ta dora hannunta a kirji tana kuka tana neman agajin Allah.
“Innalillahi, shikenan sun raba ni da murmushi sun raba ni da dariya, kuma sun keta rigar mutunci na”
Safa da marwa ta fara yi cikin gidan hannunta akai tana kuka tana jijjiga. Duk abun da ake a kunnen Aminatu, domin bachin da take son ya dauke ta ta sake farkawa a rayuwar zahiri be dauke ta ba, har lokacin kuma jikinta be daina rawa ba, kamar yadda kunnuwanta ba su daina jin karar binga, haka idanuwanta ba su kawar mata da ganin da tai ana yi ma mahaifiyarta fyade ba.
“Ina Auta? Ko sun tafi da ita?”
Baba ya tambaya yana kuka sosai, sai wata matar dake tsaye kusa da Inna tana kokarin bata hakuri ta ce.
“Aa tana daki”
Duk wanda ya ji ko ya ga ba aje da Aminatu ba ya san da cewar ba su ganta ba ne, yadda suka kwashi matan garin suka tafi da su babu abun da zai hana su zuwa da Aminatu. Baba ya tashi da sauri ya shiga dakin, sai ya same ta a inda ta saba kwanciya tana lullube, ba jikinta kadai ba, har hakoranta kana jin kara yadda suke haduwa da juna tsabar yadda jikinta yake rawa. Baba ya kai hannu ya janye mayafin sai ta tashi da sauri idonta a kumbure ta kalleshi.
“Baba...Baba... Baba... Baba”
Baba ya sake fashewa da kuka.
“Baba wasu mutane ne suka zo.. Ba mu musu komai ba Wallahi, ba mu musu komai ba... Sun... Sun... Sun... ”
Ta kasa fada sai ta fashe da wani irin kuka ganin cewar da gaske ne komai ya faru ba mafarki ba.
Ba ko wace gawa ta samu sallah da sutura yadda ya kamata, saboda yawan gawarwakin, ashe ma samun sutura da masu yi ma gawa sallah da kuma binne ta kamar yadda addini musulunci ya tabadar wani abu ne da ba kowa yake samu ba, domin wasu da tufafin jikinsu ake saka su a cikin ramen, wani ramen kuma sai a hada mutum hudu guri daya.
Bayan an binne gawarwarkinsu ne, Bashiru ya iso, hankali tashe, yana shigowa shi ma ya fara nasa kukan, na rashin yan'uwa. Aminatu kam tana can gefe daya zaune ta ki yarda ta zauna cikin mutane ko kallon mutane bata so, kuma ta ki cin komai. Sai da ta ji Baba yana maganar zai tafi asibitin gurin Sanusi sannan ta mike tsaye da sauri.
“Baba dan Allah ka tafi da ni”
Ta fada cikin kuka, wani irin tsoro take ji ganin take kamar sake dawowa zasu yi, gaba daya a firgice take, a dayan bangaren kuma tana son ganin halin da dan'uwanta yake ciki.
“Aa Auta ki zauna a nan, asibi ce fa”
Ta yi saurin rike rigarsa ta fashe da wani irin kuka.
“Dan Allah Baba ka tafi da ni, ka taimaka min dan Allah Baba ka tafi da ni”
Idon Baba ya sake cika da kwalla.
“To saka talkaminki mu tafi”
Ta saka talkamin dake kusa da ita, bata tsaya neman nata ba, haka suka fito cikin gidan tana rike da rigar Baba, Baba ya nuna mata wani babur.
“Ki hau Babur din Buba, ni zan hau na Isah”
Sai ta girgiza masa kai tana kuka ta rumgume shi.
“Aa Baba Baba dan Allah karka sake yin nisa da ni”
Gani take kamar idan yana nan babu abun da zai faru, gaba daya ta rasa gane kan komai, kwakwalwarta ba zata iya dauka ba.
A dole babur daya suka hau ita da Baba, dan motsi kadan sai ta ji kamar zuciyarta zata fado tsabar tsoro, har suka isa idon a rufe yake domin ganin take idan ta bude ido mutanen zata gani.
Ko da suka isa sun tararda asibitin a cike, domin a kauyensu ko a gidansu kadai akai ta'asar ba, an kawo mutane da yawa, wasu sai ihu suke wasu kuma suna zaune suna jiran a gama da wasu a duba su. Baba da Aminatu waje suka tsaya Isah ya shiga ciki, ganin ya dade yasa Baba ya shigo cikin emergency tare da Aminatu, gaba daya ta kara firgicewa ganin yadda wasu ke zubar da jini. Kamin su karasa inda suke zaton dakin da Sanusi yake ne, Isah ya fito yana kuka.
“Lafiya?”
“Baba babu Sanusi, Sanusi ya tafi sai dai idan mun isko shi, Allah ya jikanka Sanusi...”
Ya fada yana kuka, sai ga gawarsa an fito da ita. Aminatu bata san lokacin data saki rigar Baba ba ta ruga da gudu gurin gawarsa, duk ita duk tsoron gawa da take yau ta manta da wannan.
“Wayyo Allah na shiga uku, Ya Sanusi”
Sai kuma ta juyo da gudu gurin Baba dake kuka ta rike shi.
“Baba kai yi wani abu dan Allah Ya Sanusi ya tashi”
Baba ya girgiza mata kai yana wasu irin hawaye masu zafi.
“Ba ni da rayuwa Aminatu, sai hakuri”
Sai ta sulale kasa ta fashe da kuka.
“Wayyo na rasa Yaya mai sani dariya, yayana mai tsokanata, Yayana mai so na”
Baba ya duka kamar zai mata magana sai dai shi ma bashi da zuciyar yin haka a yanzu, sai ya kara fashewa da kuka.
“Allah ya Isar mana Allah ka isar mana”
Isah ya fada yana kuka, duk wani mai sauran imani da tausayi sai da idonsa ya cika da hawaye saboda tausayi. Zunbur tai ta tashi tsaye.
“Baba ku duba kila be mutu ba...”
Rugawa tai zata tafi gurin gawar sai Isah ya riketa, wani irin tsalle tai tana son ta kwaci kanta daga rikon da yai mata amman ta kasa, ta fisgi kanta ta fisga ta sake fisga ta sai fashe da tana jin kamar ace yau akwai abun da zata iya yi ta dawo da rayuwar Sanusi.
>>>>>>
If you want to subscribe pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, and send the evidence to 08036126660, zan yi adding dinki paid group In-sha-Allah.
Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai.
Ga masu bukata za su iya tuntubar number nan 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.
Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.
*💔 BAKAR WASIKA 💔*
By Khadeeja Candy
Page -6️⃣
Bakincikin mutuwa, da damuwar rasa rai, wani irin bakinciki ne da yake ma kansa muhalli a zuciyar bawa, baki yayi kadan ya bayyana yadda zuciyata take ji, haka zuciya ma ba zata iya daukar abun ita kadai ba har sai da taimakon idanuwa da gangan jiki.
Taya Aminatu zata fadawa kowa yadda take ji? Taya zata rasa yayyu biyar maza kuma ta kasa kuka? Taya za a maida garinsu da gidansu kamar kufai kuma ta kasa kuka? Taya za a keta haddi mahaifiyarta a gaban idonta kuma ta kasa kuka?
A tsakanin rasa yan'uwanta da kone musu abinci da keta haddin mahaifiyarta bata san wani yafi wani zafi ba. Anya zata iya dauka?
“Duk ni kadai?”
Ta furta wasu hawaye mazu zafi na sauko mata, kana ganin yanayinta da kuma jin kalaminta kasan bata cikin hayyacinta, ruwan hawayen dake mata zuba har ya canja launin fatar idonta, ya kumbura mata ido, kwayar idon kuma ta mata ja sosai.
“Auta dan Allah ki yi hakuri, haba kowa ba yana da tabon mutane nan a garin nan”
Anty Aina'u matar Bashiru ta fada tana kai hannu ta dafa ta. Aminatu ta kalleta kamar tace mata shiga zuciyata ki gani, sai kuma ta dauke kai ta hadeye yawu.
Har aka yi gaisuwar kwana uku aka watse Amintu bata daina kuka ba, kukan da ta sha ko Inna bata yi ba, domin Inna ta bar komai a zuciyarta ne, idan ta yunkurin kukan ma baya zuwa mata, sai dai bata iya komai ko bandaki zata zagaya sai an rikata. Idan kuma ta zauna ta sanda kai kasa bata iya dagowa sai an rika kan nata an dago da ita. Kana ganinta ka san kukan zuci take wanda ya fi na ido illa.
Washe garin Ranar da aka watse Aminatu na tsakar gida tana wanke wanken kayan abincinsu, sai kawai ta fashe da kuka, rayuwarsu take tunawa kwana hudu zuwa biyar da ya wuce, a da idan tai wanke wanke kowa zubawa ake, amman yanzu daga ita sai Isah da Inna da Baba kawai suke ci, ba kamar da ba. Tunawa da tai da maganganun da mutane suke mata cewar ta yi hakuri ko dan ta karfafawa mahaifiyarta guiwa yasa tai saurin share hawayen. Ta cigaba da wanke wanke bayan ta gama ta dauki kayan ta kai a inda suka saba ajewa ta aje. Sannan ta fara sharar gidan, tana yi tana ta ganin inda aka aje gawarwakin yan'uwanta, ta kasa daina ganin abun a idonta.
Bayan ta gama sharar ta dauko tabarma ta shimfida daga bakin kofar sannan ta shiga ciki ta riko Inna dake kwance.
“Inna muje waje ki sha iska”
Daman zaman dakin