Showing 54001 words to 57000 words out of 332834 words
harabar gidan sai rantse da Allah yau ya fara ganin gidan, sai hankalinsa na can wani gurin daban ya dade a tsaye sannan ya karasa entrance din ya murda kofarsa ya bude. Yana shiga yai wanka ya fito ya shirya cikin shadda milk color ya saka hula sannan ya saka wallet dinsa da wayarsa aljihu da ya fito rike da makulli mota ya ja kofar.
Leila na tsaye jikin window dakinta tana kallonsa da murmushi a fuskarta har ya shiga motarsa ya danna horn aka bude masa ya bar gidan.
Sai ya fara biyawa ta shagon da yake siyen sweet da chocolate din da yake zuwa da su gidan marayu sannan ya wuce gidan abokinsa Ali domin a tare suka saba zuwa, wani lokacin Ali zai zo ya dauke shi wani sa'in kuma shi yake zuwa ya dauki Ali kamar dai yau. A bakin gate din gidan ya faka motarsa sannan ya ciro wayarsa ya kira Ali, Ali na yin picking sai ya kashe wayar ya aje. After like 5 minutes Ali ya fito ya bude motar ya shiga, Talba yai reverse sannan suka hau titi.
“Ina yara?”
“Lafiya Kalau Gwauro”
Ali ya amsa masa yana kallonsa fuskarsa da dariya. Talba be sake cewa komai ba har suka kusa isa sannan Ali ya dauko masa zancen Aminatu.
“PA ka ya turo kudi dazun Allah ya saka da alheri”
Nan ma Talba be ce komai ba, har sai da Ali ya dauko masa zancen kiran da Leila tai masa dazun yana murmushi, sannan ya kalleshi.
“Da kai tai waya da safe kenan?”
“Yeah kishi take wai ba zata iya daukar ka kwana da wata a rai ba”
“And...”
Ali ya kalleshi.
“And she's right”
Tabe baki Talba yai be sake cewa komai ba har suka isa gidan marayun, tun kamin ya karasa harabar yaran suka nufoshi a guje suna murna da zuwansa, murmushi ne ya cika fuskarsa farinciki marayu na daga cikin abun da yake faranta ransa, musamman kananan domin Talba mutum ne mai matukar son yara. Da sauri ya bude motar ya shafa kansa yana tambayar lafiyarsu, sannan ya mika hannunsa ya dauko alawar daya siyo musu ya bude ya fara raba musu.
“Uncle ni dai chocolate nake so”
Wata yar karamar yarinya ta fada, sai ya amsa mata in a funny way yana dariya kamar ba shi ba.
“Noooo chocolate dai anjima idan zan tafi”
Ali ya bude dayan side din ya fita yana amsa waya.
“Subhanallahi gani nan zuwa”
Ya fada sannan ya saka wayar aljihu ya zagayo side din da Talba yake zaune a motar.
“Zan barka nan na tafi asibiti”
Wani kallo Talba yai masa wanda ke nuna alama ce ta tambayar lafiya.
“Wai yarinyar nan aka samu ta suma hannunta nata zubar da jini kuma robar karin ruwa murde a wuyanta kamar an shaketa”
Shiru Talba yai fuskarsa da mamaki sannan ya fito cikin motar gaba daya.
“You can go with my car”
“Thank you”
Ali ya fada sannan ya shiga motar da sauri, Talba ya bude baya ya dauko ledar chocolate din sannan ya rufe har lokacin fuskarsa dauke take da mamaki, bin motar yai da kallo har sai da Ali ya fita gate din sannan ya maida dubansa gurin yaran sai dai gaba daya hankalinsa ya tafi akan dalilin da zai saka yarinyar ta aikata haka, he don't even think zata ma iya aikatawa kanta haka sai dai idan wani ne ya kashe ta ko kuma yake kokarin kasheta.
Be wani dade sosai kamar yadda ya saba yi ba domin hankalinsa gaba daya ya tafi gurin yarinyar, and baya son azahar tai masa a nan saboda a tare suke cin abincin rana da duka Family kamar yadda suke yi da safe on every weekend sai dai idan akwai wani uzuri. After like 2 hours da wucewar Ali ya turawa direbansa sakon inda yake. Sannan ya bude chocolate din ya shiga raba musu yana Murmushi kamar ba shi ba.
Bayan ya gama yai musu bankwana suka rakoshi har gurin da direban ya faka motar, domin ya dade a zaune cikin motar yana jiran Talba. Kamin ya karaso direban ya fito ya bude masa motar bayan ya shiga ya rufe, ya ya zagaya da gudunsa ya shiga driver side ya ja motar suka nufi gida.
Tafiyar minti talatin suka iso unguwar
shimkafi Quarters, Talba na hakimce cikin motar har direban ya faka motar a kusa da entrance din kofar Momy. Kamar ya bude baki ya ce ma direban ba bangaren Momy zai fara shiga ba, sai kuma ya ji ba zai iya ba, sai da direban ya bude masa motar sannan ya fito ya nufi bangarensa.
Yana shiga ya bedroom dinsa ya bude bathroom yai alwala ya fito yana rike da agogon hannunsa, a inda ya saba aje shi ya aje sannan ya nufi inda Capet dinsa ta sallah take shimfide yai ikama ya fara gabatar da sallah nafila. Kamin ya sallame limamin gidansu ya fara kiran sallah hakan yasa yana sallamewa ya fito daga bangarensa ya nufi masallaci gidansu inda dukansu suke sallah da kuma ma'aikatan gidan.
Bayan saukowa daga sallah azahar ya nufi bangaren Momy sai kamshi turare yake kamar wanda ya lullube jarkar turaren a jikinsa. Sai da ya danna door bell din sannan kuma yai knocking sai ga Zulai da gudunta ta bude masa.
“Sannu da zuwa ranka ya dade”
Kai kawai ya daga mata sannan ya nasa kafarsa cikin falon, saman sofa ya zauna yana kallon Plasma dake ta aikinta, babu kowa a falon sai Leila dake zaune a dinning rike da waya, yana shigowa sai duk hankalinta ya tattara ya koma kansa. Be yi minti biyar da zaman ba aka sake danna door bell din, Mairo dake kitchen ta fito da gudu ta nufi kofar ta bude, daman idan ba yan aikin gidan ba ko Kabir sai Amal sune kawai suke iya bude kofa idan ana kwankwasa, Leila tana ganin ta fi karfin haka, Talba kuma jin kai ba zai bar shi ba.
“Baaba na nan?”
“Ban santa ba gaskiya”
Shiru yai yana kallon sabuwar yar aikin domin be taba ganinta ba, duk kuwa ba da yawan zuwa yake gidan ba amman dai akan aikoshi daga kauye gurin Kakarsa Baaba dake aikin gidan, hakan yasa police din dake gadin gidan suka san shi basa hana shi shiga a duk lokacin da ya zo.
“To Hajiya fa?”
Ya sake tambaya, sai Mairo ta amsa masa.
“Eh tana nan wa za a ce mata?”
“Ki ce mata Shamsu ne jikan Baaba”
“Toh”
Ta saki kofar falon dake bude ta nufi hanyar upstairs. Leila a hango shi ta mike tsaye da sauri.
“Ki ce masa Baaba bata nan”
Ta fada kamar wanda ya rikice. Mairo ta juya da sauri da zimmar fada masa, sai Talba ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu. Mikewa yai tsaye ya nufi kofar Leila na ganin haka ta nufi upstairs da gudu.
Shamsu na ganin Talba ya dan risina masa yana gaishe shi.
“Shamsu”
“Na'am ranka ya dade ya gida?”
“Alhamdulillah, lafiya dai?”
“Lafiya Kalau, daman daga can gida ne suka ce na zo na duba Baaba ko lafiya kwana biyu ba a samun wayarta”
Kamar an dasa ice haka Talba ya tsaya jikin kofar yana kallon Shamsu da mugun mamaki, kwakwalwarsa ta cika da tarin tambayoyi, sai ma ya rasa abun da zai ce wa Shamsu.
Yawun bakinsa ya hade a hankali yana kallon Shamsu har ya bude baki zai yi masa magana sai ya ji muryar Momy dake saukowa tana kiran sunan Shamsu da far'arta, abun da bata saba yi ma talaka ba musamman wanda yake karkashinta.
*Khadeeja Candy*
Ko kin san kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin sa kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya domin siye ko sari ku tuntu Ramla incense ta wannan number +234 703 839 2576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa
*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min! Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*
“Shamsu ne?”
“Eh Hajiya ina wuni?”
“Lafiya kalau shigo mana”
Talba ya juyo tana kallon Momy dake amsa masa da far'arta kamar ba ita ba. Sai kuma ya juya ya kalli Shamsu dake kokarin shigowa.
“Baaba ka zo nema...?”
Kamin Shamsu ya ce komai Momy ta daka masa tsawa.
“Talba ka barshi ya huta ya sha ruwa mana, Mairo akai shi karamin falo a kawo masa ruwa”
Momy ta karasa tana kallon mai aikinta Mairo, sai Mairo ta amsa a ladance.
“Toh Hajiya”
Ta wuce gab Shamsu ya bi bayanta, Momy ta gyara tsayuwarta tana kallon Talba.
“Bangaren Mahaifinku zaku yi lunch”
Ya gyada mata kai yana bin Shamsu da kallo.
“Zulai ta kai komai a can Engineer kai kawai yake jira”
Ta fada tana juya wayarta a hannunta, yanayin yadda tai maganar yana nuna masa son take ya bar mata falon. Ya san ba zai iya nufar falon ta ce akai Shamsu ba, idan ma yaje ba zata bari yai magana da shi ba, idan kuma ya ce zai musa mata zata yi korafi.
Juyawa yai ya fice daga falon gaba daya zuciyarsa cike da tambayoyi kala kala, a entrance ya tsaya yana kallon harabar gidan, sai kuma ya nufi gate din ya fice daga gidan gaba daya.
Yana fita falon Momy ta rufe kofar da kanta tana sauke ajiyar zuciya. Lumshe ido tai ta bude tana kai hannu ta dafa kirjinta dake mugun bugawa da karfi, sannan ta bar jikin kofar ta nufi karamin falon inda Shamsu yake zaune, yana ganinta sai ya sauka daga kan kujerar ya zauna a kasa abun ka da mutunen kauye akaai girmama mutane.
“Shamsu ya gida ya kowa?”
Ta tambaya bayan ta zauna.
“Lafiya kalau Hajiya”
“Maa Shaa Allah, fatar su Baaba ma suna lafiya?”
“Eh... Ai ita aka ce na zo na duba, kwana biyu an ta kiran wayarta baya shiga”
“Ah ah Subhanallahi, Baaba ai yau kwananta tara ko takwas da tafiya gida”
Shamsu ya kalleta da sauri.
“Gida Hajiya? Wallahi bata je gida ba”
“Subhanallahi Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, lallai tabbas ni ma nayi ta kiran wayarta bayan tafiyarta ban samu ba, amman ban saka ran komai ba saboda na san kauye wani lokacin akwai matsalar network ko nepa, kaga ai shiyasa binciken yake da dadi Allah yasa ba mugun hannu ta fada ba, amman ka bincika aka ce bata je ba?”
“Wallahi bata je ba, ai idan tana can dole zan sani saboda a gidan nake, kuma bata fada miki dalilinta na zuwa ba”
“Eh to gaskiya bata fada min ba, na san dai kamin ta tafi tana dan jin jiki, domin da kaina ma na dauke ta muka je asibiti aka ce zazzabi ne da hawan jini, bayan mun dawo da kwana biyu tace min tana son taje kauye ta ga kowa hankalinta ya koma can a yanzu, ta inda nai kuskure ban tambaye ta me take tunani ba, domin hawan jini baya tasowa haka siddan sai da damuwa ko bakinciki har ma nake cewa ba zata kira ta fada a kauye ba tace bata son ta tashi hankalinsu”
Wani kalar tashin hankali ne ya cika Shamsu, jin cewar Baaba bata gidan ga wayarta ma idan an kira ba a samu, Momy kuma ta fada masa cewar yau kwananta tara da tafiya. A gabansa Momy ta nemo number Baaba ta kira ta saka wayar a speaker, daga ita har Shamsu suka ji cewar wayar a kashe take. Shamsu ya mike tsaye
“Wallahi haka nima suke ce min idan na kira, su ma can haka suka ce wayar a kashe take, amman yanzu zan kira na fada musu halin da ake ciki”
“Gaskiya kam kara a dage da addu'a kuma a saka cigiya, ni ma Inshallah zan bada sanarwa gidan radio ko Allah zai saka a dace”
“Zan tafi Hajiya”
“To Shamsu bari na baka number na duk yadda kake ciki sai ka kirani”
Ta fada tana karanto masa number ya saka sannan ita ma ta mike tsaye.
“Bari na kawo maka wani abu ka hau mota”
Tsaye a falon cikin tashin hankalin kamin Momy ta kawo masa 5k din har ya matsu domin hankalinsa gaba daya ya koma gurin inda yake tunanin Baaba zata iya zuwa. Ya karbi dubu biyar din data bashi yana godiya ya fice da saurinsa kana ganinsa kasan bayan cikin natsuwa. Har bakin kofar babban falon Momy ta raka shi tana ta masa addu'ar Allah yasa a gane ta ya amsa da Ameen sannan ya fice ta maida kofar ta rufe. Sannan ta hau sama da sauri ta nufi dakin Leila, Momy na turo kofar Leila ta zabura ta mike tsaye da sauri tana hawaye jikinta har rawa yake.
“Miye haka? So kike idan ya gani ya fara zargin wani abu”
Leila ta kama hannayen Momy ta rike tana kuka.
“Momy tsoro nake ji”
“Ki daina jin tsoro, babu abun da zai faru, idan kina nuna irin wannan hallayar sai ki tonawa kanki asiri, amman idan kika cire komai a ranki sai ki samu kwanciyar hankali”
“Momy har yanzu ina mafarkinta Wallahi, kuma ina jin kamar asirina zai tonu”
“Idan ma asirin ki ya tonu sai mu zuba miki ido akaiki gidan yare? Ko ayi miki wani hukunci? Noooo babu abun da zai same ki, je ki kwanke fuskarki ki shafa hoda ki same ni a bangaren Daddynku”
Ta gyada kai wasu hawayen na sauko mata.
“Momy akwai CCTV a gidan nan, Talba zai iya bincikawa, kuma idan ya gane zai iya cewa ba zai aure ni ba”
“No kul bakinki ya daina furta wadannan kalaman, Talba ba shi da mata sai ke, ki kwantarta hankalinki zan saka a cire CCTV cameras din, je ki wanke fuskarki”
Ta saki hannayen Momy ta nufi bathroom dinta Momy kuma ta fice daga dakin, tana saukowa ta nufi kofar da zata sadata da part din Daddy.
Kamar zai tashi sama haka Shamsu ya nufi gate yana ciro karamar wayarsa ya ciro karamar wayarsa domin kiran yan'uwansa ya sanar musu halin da ake ciki, police din dake gadin gate din ya bude masa ya fita hankali a tashe. Talba dake tsaye wajen gate din ya kalleshi yana karantar irin tashin hankalin da yake ciki.
“Ka fito”
“Eh ranka ya dade, zan je can gida na fada musu halin da ake ciki”
Talba ya masa kamar ya san abun da yake magana akai.
“Oh ba su sani ba”
“Eh Wallahi shiyasa suka ce na zo na bincika ai, ita ma Hajiya tace tana ta kiran wayar sai ta jita a kashe, Allah yasa dai ba mugun hannu ta fada ba”
“Ameen”
“Yanzu zanje can na fada musu, Hajiya ma tace yau kwananta tara da tace mata zata je ganin gida, ka ga ita bata san bata isa ba, mu kuma ba su san da zuwanta ba”
“Haka ne, Allah ya bayyanata”
Shine abun da Talba ya fada zuciyarsa na bugawa kamar zata fasa kirjinsa ta fito saboda bacin rai, zuciyarsa na ta dawo masa da abun da Ali ya fada masa akan halin da aka samu Aminatu.
Bayan Shamsu ya amsa da Ameen Talba ya kwankwasa karamar kofar gate din suka bude masa, ya doshi cikin gidan, Momy na shiga bangaren Daddy Talba ya danna door bell din, Mairo ta zo da gudunta ta bude masa, kana ganin yanayinsa kasan ransa a bace yake, kai tsaye ya nufi stairs sai dai kamin ya karasa hawa Leila ta fito fuskarta cike da ruwa ko hodar da Momy ta ce ta shafa bata shafa ba, tana ganin Talba ta hade yawu da karfi ta dauke numfashi na tsawon dakika uku.
“Yanzu zan iya sanin abun da kika yi ma Baaba?”
A karo na biyu ta sake hade yawu da karfi a tana kallonsa kamar wanda bata fahimci abun da yake magana a kai ba. Ya kara matsowa kusa da ita cikin wani irin bacin rai sai ta koma baya da sauri tana kallon kofar da Momy ta fito.
“Lafiya na shiga can ban ganku ba, Daddynku yana jira zamu ci abinci”
“Answer me...!!!”
Talba ya fada a tsawace yana Kallon Leila. Cikin karfin hali tace.
“Ni ban gane abun da kake magana a kai ba”
“Miya faru?”
Momy ta tambaya daga downstairs din da take tsaye. Sai Leila ta amsa mata.
“Tambaya yai wai zan iya sanin abun da ya faru da Baaba”
“What? Me kake kokarin cewa Talba?”
Talba be kula Momy ba ya kara yin sama ya matsa kusa da Leila.
“I hope ba ke kika shakari yarinyar can ba, kike kokarin kasheta, saboda zafin zai zame miki biyu wahalar zata miki yawa...”
Hawaye ne ya fara saukowa Leila.
“Talba wace irin magana ce wannan? Me kake son fada?”
Juyowa yai ya kalli Momy.
“Momy kin san me nake magana a kai, I'm not a fool na fahimci komai, and i do hope Leila bata da hannu a kokarin kashe yarinyar nan...!”
Yana kawai nan ya sauka a fusace ya fice daga falon gaba daya, Momy ta bishi da kallo, Leila kam ban da hawaye babu abun da take.
“Wace yarinya yake magana akai?”
Zubewa Leila tai a gurin ta fashe da kuka.
“Momy....”
Sai kuma ta kasa karasa, Momy ta hau saman da sauri ta rika Leila suka nufi dakinta.
TALBA POV.
bangarensa ya nufa wayarsa makalle a kunnensa yana ta kiran Ali, sai dai har wayar ta gaji da ringing ta katse Ali be daga ba, zaunawa yai saman kujera ya sake kiran wayar, wannan karon ma Ali be daga ba. Hakan yasa ya dauki keys dinsa ya fito ya shiga motarsa ya fito ya ja motar da karfi, suna ganin ya kunna motar suka bude masa gate. Cikin saurin ya fice daga gidan, yana driving zuciyarsa na raya masa Leila zata iya yin yunkurin kashe yarinyar saboda ta tambayi Ali akan ta, wata kila zata iya zargin wani abu ne a tsakaninsu idan ma bata yi da kanta ba zata iya saka wani yai.
Yana isa asibitin ya faka motarsa ya fito ya mufi hanyar da zata sada shi da office din Ali, kamin ya karasa Office din Ali ya fito daga ward din, yayi mamakin ganin Talba sai dai kamin yace komai Talba ya ce.
“Ali ya yarinyar take?”
“Ba dadi, but she's still alive”
Wani deep breath Talba yai sannan ya bude office din suka shiga.
“Ya akai abun ya faru?”
Ali ya rufe kofar yana fadin.
“Nurse