Showing 33001 words to 36000 words out of 332834 words
ba hujja bace Momy idan ma da gaske ne”
Tabe baki tai ta cigaba da abun da take, har suka ci suka shude Talba be ce komai ba, daman shi ba komai ke saka shi magana ba, ko da kuwa abun ya dame shi.
“Momy zan tafi aiki”
“Yau da wuri?”
Ya daga mata kai.
“Allah ya tsare”
“Ameen”
Ya amsa sannan ya fito daga bangaren yana wani irin kamshi turare mai jan hankali yan mata da saukar da natsuwar mai shakarsa. Kai tsaye bangaren Daddy ya nufa sai da yai knocking sannan ya tura kofar sai ya jita a rufe, door bell din ya danna sannan yaja ya tsaya. After few minutes aka bude masa kofar. Sai da suka gaisa da Amal da ta bude masa kofar sannan ya karasa can ciki gurin Daddy. Sai ya same shi zaune rai a bace yana kallon wayarsa, domin labarin harin da aka kai ya karadi kafofin sada zumunta musamman Facebook.
“Wa'alaikassalam”
Daddy ya dago yana amsa masa sallamarsa, Talba ya zauna kusa da shi yana karantar bachin ran daya bayyana a fuskarsa.
>>>>>><<<<<<
Sauran page daya mu gama free page, if you want to subscribe pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank and sent the evidence via 08036126660. Yan nijar kuma za ku biya ta wannan number +227 90 16 59 91 sai na yi adding dinku a group.
________
Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata.
Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.
Serious Buyers please, idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.
*💔 BAKAR WASIKA 💔*
By Khadeeja Candy
Page -1️⃣0️⃣
Talba ya mikawa Daddy wayar bayan ya gama dubawa.
“Daddy ku da kuke kusa da gobnati ya kamata ace kuna fada musu halin da ake ciki mana, mutanen nan suna cikin bala'i, kamar ni ne, kana zaune kana rayuwarka sai a iskoka a koreka daga gidanka a akashe yayanka kuma a keta haddin matanka, Wallahi tausayi suke ba ni matuka”
Cewar Talba cikin wani irin bacin rai da jin zafin abun da yake faruwa. Daddy yayi murmushi yana gyara zamansa.
“Mu'az kenan, waya fada maka gobnati bata san halin da ake ciki ba? Sun san komai, wannan matsalar tsoro tana kawo kudi sosai, fiye da yadda kake tunani, duk jihar dake fama da matsalar tsaro kudin da ake ware mata dabam, idan har aka magance matsalar to abinci wasu zai tsaya, kuma duk jihar da kaga suna fama da matsalar tsaro to suna da cigaba da ake bukata”
“Amman Daddy basa tsoron hakkin rai?”
“Wannan kuma ai sai lahira, Allah dai ya kyauta kawai amman matsalar tsoro a yanzu abu ne mai wahalar magancewa, domin an fi samun kudi ta gurin tun daga manya har kanana, na mu dai addu'a ne, da kuma taimaka musu da abun da Allah ya ba mu”
A hankali Talba ya busar da iskar bakinsa ya kalli Amal data doso inda suke sanye da uniform dinta na makaranta.
“Na yi magana da PA zai yi list din abubuwan da zamu siya mu kai musu soon”
“Maa Shaa Allah, hakan na da kyau”
“Wa za a kaiwa? Baaba?”
Amal ta tambaya tana aje fular abinci. Daga Daddy har Talba kallonta su kai, ta san ba maganar Baaba ake ba, kawai ta dauko maganar ne saboda tana son fadawa Daddy abun da ya faru ne, daman ita ce yar gulmar gidan komai akai a bakinta za aji.
“Wace Baaba kuma? Yan gudun hijira ake magana”
“Au na dauka Baaba za a kaiwa, Allah yasa dai ta ji sauki”
“Miya same ta?”
Daddy ya tambaya, a nan Amal ta zauna gefensa ta labarta masa irin abun da ta fadawa Talba.
“Taya Doctor zata yanke wannan hukunci bs tare da sani na ba? Tafi ki kirata”
Daddy ya fada rai a bace. Sai ta mike tsaye gabanta na faduwa.
“Ya sai ka ce ni kai ka fada”
Talba yayi murmushi, ita ma murmushin tai ta fice, bayan ta wuce Daddy ya kalli Talba.
“Ka san da maganar ne?”
Talba yayi shiru ba tare da ya amsawa Daddy da eh ko aa ba. Wanda hakan ya tabbatarwa da Daddy cewar ya sani kenan, domin idan be sani ba kai tsaye zai fadi cewar be sani ba.
Daddy be sake cewa komai ba har sai da Momy ta shigo dauke da wasu manyan kulolin abinci ta aje a gabansa, sai da Momy ta kalli Talba sannan ta kalli Daddy tana karantar yanayinsu.
“Lafiya dai engineer?”
Daddy ya kalleta irin duban da ke fassara mata bacin ransa.
“Baaba ta fado, har kun kaita asibiti amman baki sanar da ni ba”
Dagowa Momy tai ta kalli Talba da kansa ke kasa.
“Ina ganin kamar karamin abu.... ”
“Karamin abu? Da gaske? Amina kin san abun da kike fada kuwa? Mutum ya fado daga sama zuwa kasa ki kira shi karamin abu? Idan har karamin abu ne yayanta zasu dauke ta su tafi da ita ne? Ko da ma karamin ciwo ne tun da har a nan ta samu matsalar ai ya kamata ki sanar da ni, kuma be kamata a bar yayanta su tafi da ita ba, a nan ya kamata a dauki nauyin komai na ta, shekara biyu tana aiki tare da mu”
“Ranka ya dade, ba wani ciwo ne sosai ba, kuma na kaita asibiti sun bata magani sai ta kira yayanta tace zasu tafi da ita, babu yadda ban yi ba amman suka ki yarda, kuma ina da niyar fada maka anjima da dare idan ka natsu”
“Yanzu idan wata ce a cikin yayanki ta fado zaki mata haka ne? Balle tsohuwa? Sometime kina abu kamar damuwar wani ba damuwarki ba ce”
“Allah ya huci zuciyarka Engineer, amman be kamata damuwar wani ta dame mu ba, mu ma yanzu idan muka shiga cikin wata matsalar babu wanda zai damu da halin da muke ciki”
“Okay, yayi kyau daga yau ba zan sake biyan mai aiki ba, indai zan dauki mai aiki ta taya yaranki aiki ne ba za a sake ba, idan har damuwar wani be kamata ya dame mu ba, karki sake gabatar min da wata matsalar yan'uwanki balle kawaye”
Yana kaiwa nan ya mike tsaye a fusace ya nufi hanyar dakinsa. Momy ta rutse ido ta bude ta kalli Talba da shi ma kallonta yake domin ya san shi zata dorawa laifi.
“Karamin abu ma, sai ka tasa mahaifinka a gaba kana tsegunta masa? Talba wacce irin rayuwa ce wannan? Mun yi fada hankalinka ya kwanta? Kuma zai fita be karya ba, ina tunanin haka kake so ai? Kai na ya fara kwnacewa da lamarinka”
Uffan Talba be ce ba, har tai ta gama ta mike tsaye ta fice, mikewa yai tsaye ya ciro wayarsa dake ringing.
“Ali”
Ya fada bayan ya danna picking.
“Talba ka fita office ne?”
“No ya akai?”
“No ina son magana da kai ne, na dauka kana office na biyo”
“No yanzu zanje, yau da wuri zaka je aiki kenan?”
“Eh muna da patients da aka kawo mana, kasan sojoji sun samu kwato wasu daga cikin wadanda yan bindiga suka tafi da su, akwai wadanda suka samu rauni sosai an kawo mana su”
“Eh na ji an kai hari abun ba dadi Wallahi”
“Sosai an kawo wasu shekaran jiya wadanda suka harba abun ya kazanta”
“Allah ya kyauta, We can talk later”
Ya sauke wayar, sannan ya nufi kofar fita yana kiran Jahid.
AMINATU POV.
Labarin harin da aka kai ya karade ko'ina a Nigeria, gidanjen jaridu da kuma kafofin sada zumunta. Hakan yasa aka turo jirgin sojijin tun daga jihar Lagos har zamfara.
Kwashe gari aka bi su da danyen dankalin hausa a hannu duk wanda aka gutsawa sai yai sauri ya cinyewa, bayan sun gama ci kuma sai a bisu duka musamman wadanda aka akai maganar kudi da yan'uwansu ba su kawo ba. Sun fi dukansu fiye da kowa, duk abun da ake Aminatu na kwance bata iya komai ba, har yanzu bakinta a nauyaye yake, idanuwanta ne kadai abun da suke aiki a jikinta sai numfashi. Tana kwance galala ta daga kanta sama tana kallon jiragen sojoji guda biyu da suke shawagi a sama, kararsu kadai ta isa ta kurmantar da mutu, sun yi kasa kamar zasu saki wuta sai dai ba su saki wutar ba suka gangara can nesa da damarsu suka saki wutar a inda babu mutane.
Bayan ya wuce barayin suka fito daga gidanjensu na bukka dake can nesa da inda aka daure su Aminatu, suna da yaya da mataye a cikin bukokin sai dai akwai tazara mai yawa a tsakaninsu.
Suna isowa inda suke mutunen jiya ya sake rokon su bar shi yai sallah, sai suka hau shi da zagi.
“Kawo shi nan”
Dayan ya fada, sai sauran suka kwantoshi daga inda yake suka nufi wata bushiya inda mutunen yake, suka daureshi jikin icen suka sako kansa kasa kafafuwansa a sama yana ta lilo.
Tun yana kuka yana rokon su kwance shi har ya gaji ya fara kalmar shahada, majina ta fara fitowa ta hancinsa tana zazzagowa kasa tare da hawayensa.
Ba su kwance shi ba sai da su suka tabbatar rai ya bar jikinsa, sannan suka sauke shi kasa, lumshe ido Aminatu tai wasu hawayen suka cika mata ido.
Bata sake bude idon ba sai da ta sake jin karar jirgin, wannan karon da fatan mutuwa take kallon jirgin burinta ya sako wuta kowa ya kone har ita, domin tana da tabbacin babu wata rayuwar jindadi a tare ita ko da rayu! Ta ina ma zata rayu? Taya zata fita a nan? Idan ma ta fita gurin wa zata je? Da wa zata zauna? Wa zai rike ta? A kashe mata kowa, yayyu da iyaye, idan zata nemi yan'uwan uwa ko na uba ta ina zata fara nemansu? Ina zata gansu? Zata fita a nan ma?
‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’
Ta maimaita a cikin ranta, domin bakinta ya mata nauyin da bata iya saka komai ta tauna balle har ta furta wani abu, wata kila kalamanta sun kare wata kila kuma har da rayuwarta, farinciki kam ta tabbatar da ya barta. Bayan sallah isha'i ta dan unkura ta tashi zaune tana jin kamar ba zata iya zaman ba kuma gashi ta gaji da kwanciyar. Hannunta ta kai ta damki kasar gurin ta junke a hannunta da wani irin karfin zuciya, sai dai na jiki kam babu shi ko kadan a kusa da ita, a galabaice ta dago kai tana kallon mutanen da suka doso inda suke da manyan fitulu suna haske su, matasan yan bindigar ne suka kwance matan kusan shiri maza takwas, a cikin mutanen da aka kwance har da Aminatu.
“To ku fadawa sauran dabobi an yi diyya kar sai mun kama hanya su bude mana wuta”
Wanda yai maganar fuskarsa a nade take da rawani babu ta inda zaka iya ganinsa balle ka shaida shi, sauran yan bidigar kuma wasu na sanye da rigar soja wasu kuka wandon suka saka wasu kuma duka biyu sai dai dukansu suna dauke da manyan bindigogi.
“Ai dai hanyar da suka biyo zaku bi karku kuskura sauya hanya, idan ba haka ba zaku hadu da wata dabar, kuma za mu aika musu”
Dayansu ya fada, sannan aka fara dukansu da bulala aka korasu kamar dabbobi.
“Ku wuce yan iska, ni na tsani kado Wallahi”
Cewar dayan yana dukansu, masu kuzarin cikinsu suka tashi suka fara tafiya ban da Aminatu da sauran da akai ma fyade kamar ta, ganin hakan yasa mutumen ya roki a dorasu akan babur, a fitar da su sauran da suke iya tafiya a kafa kuma a korasu a kasa. Wadanda aka kora a kasa suna tafe suna jin tsoro saboda daukin ba dadin da ake da babbar daba, daman can sun fi kowa dauka da zafi, karama daba kudin fansarsu ba su da tsada kuma ba da taurin kai kamar babbar daba, kasancewar karamar daba matasa ne masu tasowa wasu ma duk yara ne, babbar daba kuma manya ne wadanda suka dade a cikin harkar.
Su Aminatu sun riga isa kusan da bakin dajin saboda an dauke su a babur, sai dai zubesu akai a kasa suka zauna a gurin har sai da na kasan suka karaso sannan aka hadasu aka nuna musu hanya. Sauran wadanda sukai musu rakiya kuma suka juya suka koma ana kusan kiran sallah asuba suka fiton daga dajin, Aminatu na tafiya daker tana hawaye, idan ta gaji da tafiyar sai ta zauna a kasa ta yi rarrafe idan ta gaji sai ta unkura ta mike tsaye ta fara tafiya.. Da haka har suka iso bakin gari a inda motocin sojojin suke. Da farko sun tsorata duk kuwa da kasancewar an fada musu akwai sojoji a gaba, sai dai ganin a cikin barayin ma akwai masu uniform din sai ya saka wasu suka tsorata, sai dai kana ganin wadandan sojojin kasan zaratan sojoji ne ba kamar yan bindigar ba. Karasowa sukai suka dauki mutanen a mota, Aminatu kuma da ire irenta suka daukesu suka saka a motarsu, suka kama hanyar gari da su.
Ko da tara na safe ta yi, labarin nasarar da sojojin suka samu a kokarinsu na kwato mutanen da akai garkuwa da su ta kwarade ko'ina, labarin barin wutar da akai ya shiga lungu da sako na nigeria, ya leka gidan jaridu ya cika social media.
Masu lafiya aka tafi da su inda za a buka fuskarsu ayi ado da su a jaridu, marasa lafiyar kuma aka wuce da su asibiti a sirrance.
A tsakanin iskar dake dajin dana cikin gari zuwa na asibitin da aka wace da su Aminatu ko wane dabam, na dajin na tawaya ne da damuwa da bakinciki, shigowa garin kuma samun iskar yanci ne, sai dai shiga asibiti kuma na fata ne, wata kila ta rayu wata kila kuma rayuwar ta zaba mata mutuwa.
Mutanen da suka zo da gudu suka karbeta a hannun sojan daya dauko ta, sai su ka yi mata kama da wata halittar da taban kasancewar suna cikin farin uniform ne na aikinsu. Lumshe ido tai tana sauraren yadda aka dagata sama aka dorata saman gadon asibiti ana turata.
FARUQ POV.
A gurin mai shagon ya karbi wayarsa, ya saka line sa ya kira number Baturiya ya jita kashe. Hakan ya saka ya kira ta kanwarta sai da ta kusa tsinkewa sannan ta yi picking.
“Hello Raliya ya kike?”
“Lafiya Kalau Ya Faruq”
“Yayarki ta zo?”
“Aa, tana Kano fa”
“Kano?”
Ya maimaita cikin tsananin mamaki.
“Eh Napep ta hau shi ne...”
Ajiyar zuciya ya sauke bayan ya gama sauraren abun da Raliya ta fada masa, sannan ya sauke wayar yana jin babu dadi. Ya sani ba dan komai Baturiya take masa haka ba sai dan talauci, da yana da arziki da bata isa ya mata umarni ta saba ba, daman ai ta fada idan yana da kudi ba zata taba gujewa umarninsa ba, tabbas da yana da arziki da iyayenta sun nemi inda yake sun fada masa halin da matarsa take ciki, sai dai ba su yi hakan ba saboda ba kowa ba ne a idonsu, wannan dalilin ya saka a duk lokacin da ya kai kararta akan abun da take masa sai du bata gaskiya su goyi bayanta. Cire line yayi ya ya mika masa wayar ya juyo ya dawo cikin gida cikin yanayi na rashin dadi ya maida gidan ya rufe.
BATURIYA POV.
Washe gari mutanen gidan suka bata wani tsohon Hijab ta saka ta talkami, Bayan ta karya suka rakota har bakin titi suka tara mata Napep zuwa tashar mota. Su suka biya mata na napep din, tana ta musu godiya, idonta har yanzu be warware daga kukan da tasha ba, babu abun da take ji kamar wayarta, domin samun wata wayar a gareta yanzu abu ne mai matukar wahala a halin da suke ciki, har kara ma a gidansu wata kila mahaifiyarta zata iya taimaka mata da wani abu, yayanta ya cika mata sauran ta siye wata wayar, amman ba daga bangaren Faruq ba kam.
Tun daga yanayin hausarta suka gane yar zamfara, abun ka da kanawa sai dariya suke mata ita kam bata ma bi ta kansu ba gaba daya hankalinta yana kan wayarta data bata yadda zata samu wata wayar kawai take tunani, gashi hanyar samun kudinta ta facebook ne inda take yaudarar maza, yanzu kuma babu wayar yaudara ma.
“Kai Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Ta furta wasu hawayen na cika mata ido.
‘Dan Allah aljanuna idan kuna jina ku taimaka min da wayata ku dauki kudin na bar muku’
Wannan karon a cikin zuciyarta tai maganar hawaye na sauko mata.
“Malama Lafiya dai?”
Wani matashin saurayi dake kusa da ita ya tambaya yana kallonta. Banza tai masa ta ta juya masa fuska, sai yai murmushi ya cigaba da danna wayarsa. Sai da motar ta cika sannan suka kama hanyar Zamfara suna tafe suna addu'a saboda yanayin hanyoyin nigeria kowa ya san yadda tafiya take a yanzu. Sai da tafiya tai nisa sannan aka kira saurayin a waya, Baturiya ta kashe kunne tana sauraren yadda yake amsa wayar a cikin har da amsar da yake fadawa cewar motar haya ya shigo saboda motarsa ta tsaya ya barta a nan Kano.
Baturiya na jin haka sai ta juya ta kalleshi sai a lokacin ma ta lura da shaddar jikinsa babbar shadda ce, haka zalika wayarsa ma.
Tun da suka kama hanyar direban be tsaya ba har suka iso Zamfara.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Baturiya ta fada da muryar kasa kasa tana fashewa da sabon kuka. A nan ma kallonta yai ya tambayeta.
“Lafiya...?”
Kai ta girgiza ta share hawayenta ta fada masa abun da ya faru da ita, sai dai ta canja cewar tana da aure, sai ta fada masa cewar mahaifitarta ta aiketa.
“Subhanallahi, ki gode Allah ma be kai ki wata kasar ba”
“Haka yan gidanmu suka ce, ni daman Allah ya sani gidanmu bama hawan Napep duk inda zamu je a mota ake kai mu yanzu ma tsautsayi ne”
Ta fada kamar gaske, kallon lace din dake jikinta yai kamin ya kalli kyakkyawar fuskarta.
“Allah ya tsare gaba”
“Amin”
“Amman miyasa kike kuka?”
“Haba Malam dubi tufafin dake jikina fa? Ban taba kwana a