Showing 42001 words to 45000 words out of 332834 words
kake sai na ci ubanka, talauci ya matsa shi ne kai kuma zaka kunno mana wata wutar dan kana da shegen tsohon gida”
Ta fada tana ƙwafa.
FARUQ POV.
Ya lalaba aljihunsa ya ciro naira 100 da ta rage masa ya mikawa Aisha.
“Je ki siyo koko ku sha”
Aisha ta saka hannu biyu ta karba.
“Yaya Wallahi ko jiya Mama ba tai bachi ba, yanzu ma jikinta zafi yake”
Ajiyar zuciya ya sauke.
“Jarabawa ce, ga rashin kudi, ga rashin mata ta gari, ga rashin lafiya Alhamdulillah”
Ya fada yana kallon mahaifiyarsa dake lullube bata ma san ya zo ba, karasa yai kusa da ita ya yaye mayafin data lulluba da shi ya taba jikinta sai ya ji shi da zafi sosai.
Mikewa yai tsaye ya fito daga dakin cikin wani irin yanayi na rashin jindadi. Hannunsa ya saka aljihu ya ciro wayarsa ya rike a hannu yana kallo, ya san ko siyar da ita yai kudin ba zai isa ya kai Mama asibiti ba, jinginar daya bada ma daker ya samu ya biya mutumen ya karbo wayar. Bakin kofar dakin ya zauna ya dafe kansa, yana mamakin lamarinsa wani lokacin shi kansa abubuwa suna daure masa kai, ga karatu yayi kuma ya fito da kwali mai kyau amman aiki ya gagareshi, wadanda sukai karatu tare wasu duk sun samu aiki har sun bar kasa, wasu kuma suna Abuja wasu a manyan mukana gobnati wasu a manyan bankuna da kamfani amman shi ya kare a shagon Barber, shi ma daker ya samu wani kawunsa ya bude masa shagon.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Allah ka kawo mana sauki”
Ya furta yana dago kansa ya shiga contact dinsa ya nemo number abokinsa kuma amininsa Nura.
Wayar bata dade tana ringing Nura ya dauka.
“Hello Faruq”
“Na'am Nura ya gida?”
“Lafiya kalau kwana da yawa”
“Sai godiya, ina su Sakina”
“Lafiya kalau”
“Wallahi Nura ina cikin matsala”
“Subhanallahi miya faru?”
“Abubuwa da yawa, yanzu dai wanda ya fi damuna rashin lafiyar mahaifiyata, kudi nake so rance idan zan samu na kaita asibiti”
“Kash.... Wallahi Faruq yau da 500 na tashi na basu su karya, ka san abu ga ma'aikaci idan ba albashi akai ba, ba mu da kudi, kuma gashi albashin na jihar zamfara sai a hankali anki a gyara mana, ga kayan masarufi sai tashi suke, abun da zaka siya da 20k yanzu sai 40k shiyasa albashin baya mana auki”
“Haka ne, Allah ya sauwake”
“Ameen, amman da zaka iya da kaje gidan Alhaji Mu'azu Shimkafa ance suna da Foundation na taimakon marayu da mabukata, amman idan baka jin kunya kasan wasu basa son zuwa irin abu na neman taimako”
“Haba Nura ina zancen kunya ga mai nema, suna nuna mutun a tv ne?”
“No babu ma wanda zai san an maka, amman ance Dattijon yana taimako sosai gaskiya, ban san yadda ake bi ba, amman dai idan kaje can gidansa ba rasa taimakon da zai maka ba, har aurarwa suna yi ga marayu su masu komai”
“Ai ban sani ba, ina dai jin ana fadarsa Tsohon Minister kudi ko? Ban san yana taimakom nan ba Wallahi, amman zan je yanzu Inshallah na gode sosai”
“Allah yasa a dace, ya bata lafiya anjima zan shigo na dubata Inshallah”
“Okay”
Ya dauke wayar daga kunnesa ya mike tsaye da sauri sai a lokacin ya tuna da be tambayi unguwar da yake ba. Hakan yasa ya sake kiran number Nura.
“Baka fada min sunan unguwar ba?”
“Shimkafi Road, kana shiga unguwar kace gidan Alhaji Mu'azu Shimkafi kake nema, za a nuna maka”
“Okay”
Ya saka wayar aljihu be ma koma cikin gidan ba ya nufi titi, da kafa ya taka tun daga gadar gaba har unguwar Shimkafi road, akwai tazara amman a haka yai ta cin kasa saboda babu ko naira aljihunsa.
Kamin ya karasa shiga cikin Quarters din wayarsa tai ringing, yana ciro wayar ya duba, a take gabansa ya fadi ganin number Malam Musa Dillali, hakan nan dai ya daure ya dauka.
“Hello”
“Hello Faruku haka ake daga karbar number sai ka ba matarka ta ciwa mutun mutunci?”
Tsaya yai daga tafiyar da yake fuskarsa da mamaki.
“Wane mutum kuma?”
A nan Malam Musa ya fada masa yadda sukai da Baturiya dazun sannan ya dora da abun da mai gidan ya fada masa.
“Wata kila kiransa tai ta ci masa mutunci, yanzu ya kira ni yana ta masifa wai wata ta kira shi Baturiya ta zage shi, ya baku daga yau zuwa gobe ku tashi ku bar masa gidansa”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Wallahi Malam ban san Matata zata yi haka ba, kuma Wallahi ban ce zan karbi number sa ba”
“To yanzu dai sai ku san abun ba, Baturiya ko balaraba ta ja maka”
Malam Musa na fadin haka ya kashe wayar, Faruq ya dafe kansa.
“Na shiga uku wai me ke damun Rafi'a ne? Ta sake janyo mana wata fitinar kuma? Ina ruwanta da mai gida?”
Wani irin kololon bakinciki ne ya taso masa, sai ya ji kamar na runtse ido ya bude a gansa a kabari ya huta, yana fama da wasu matsalolin yanzu kuma ta ballo masa wani.
“Wallahi yau sai na miki mugun duka, Rafi'a sai kin dawo hayyacinki in ma baki da hankali sai kin yi shi”
Ya fada rai a bace, duk abun da take masa na bacin rai bata taba mata masa rai irin wannan ba, domin be san inda zai je ba idan ya bar gidan haka nan ya cigaba da tafiya ransa a bace. Da tambaya ya aka nuna masa kofar gidan Alhaji Mu'azu Shimkafi, Gate din gidan kadai a abun kallo ne, balle kuma farar ginar da aka kawata da farin fenti ga shuke shuke itatuwa da fulayoyi, idan ka daga kanka kuma sai ka hango gidan sama daga can cikin gidan an kawata ko'ina da gilasai komai a tsare kamar ba za a mutu ba. Faruq ya girgiza kai.
“Allah man yasha'u, ka baiwa bawa ba dan kana son shi ba, kuma ka hana Bawa ba dan baka son shi ba, Allah ka bamu na mu arzikin na halal, yanzu nan gidan mutum daya ne”
Ya fa da yana mamakin tarin dukiyar dake gidan. Karasa yai bakin gate din yana kallon security cameras daka laka hagu da dama na gidan sannan ya kwankwansa kofar gate din. Ba dade wani police ya bude masa yana sanye da uniform dinsa.
“Malam Lafiya?”
Faruq ya mika masa hannu suka gaisa cikin mutumci.
“Dan Allaj ina son ganin mai gidan ne matsala ce da ni”
“To ganin mai gidan a yanzu ai, sai an jira domin be fito ba, idan zaka iya jira a nan wajen idan ya fito sai ka tare shi da matsalarka, duk dai baya son a ana mishi haka amman karka nuna masa na san da zuwan ka”
“Ba Matsala na gode sosai”
Faruq ya nemi wani gurin ya zauna a nan kusa da gate din, shi kuma police din ya koma cikin gidan ya maida gate din ya rufe. Be yi minti talatin da zama ba, aka sake bude gate din sai dai wannan karon gate din gaba daya aka bude ganin mota zata fito yasa yai saurin mikewa tsaye a zatonsa mai gidan ne sai ya nufi motar da sauri, ganin ya nufota yasa ta tsaya ta sauke gilashin motar tana kallonsa.
“Ya akai?”
“Daman na dauka mai gidan ne shi nake son gani”
“Saboda me kake son ganinsa?”
Ya tambaya tana kare masa kallon from head to toe.
“Taimako nake nema”
Hannu ta saka ta cire katon gilashin idonta.
“Okay idan ana neman taimako sai azo har kofar gidan mutum a takura masa? Baka san yadda zaka bi ta Foundation ba? Ba ma taimako a gida sai ta karkashin kungiya, kaje can ka samu kungiya karka sake zuwa nan, Talauci ba hauka ba ne”
“Haka ma Arziki ba hauka ba ne malama, karki nemi fada min maganar banza saboda na zo nema a gidanku, ni ba wulakantaccen ba ne”
“Really”
Ta bude motar ta fito tana masa wani banzan kallo.
“Dubi ka! Ka zo nema a gidanmu kuma kana cewa kai na wulakantacce ba ne? To waye kai? Kai kama isa ka zo nema a gidanmu kuma fada min maganar banza?”
“Maganar banza ana furtata ne a lokacin banza kuma ga mutanen banza irinki”
“Ni...”
Ta nuna kanta Faruq ya daga mata kai cikin bacin rai daman be gama wankewa daga na matarsa ba ita kuma tana neman kara masa wani, hannu ta daga zata mare shi sai ya rike hannun da mugun karfi ya jefar da shi.
“Kika kuskura kai hannunki a fuskata sai na illataki, dan ina neman taimakonku ba shi zai baku damar wulakanta ni ba”
Bata sake ce masa komai ba ta juya da sauri ta isa gurin gate din ta buga da karfi, daman Police din ya rufe gate din a lokacin daya bude mata ta fita, da sauri ya bude sai ta nuna masa Faruq.
“Ku rike mutumen can”
Da sauri ya fito shi da wasu Police din biyu suka nufi inda Faruq yake tsaye suka rike shi, ita kuma ta nufi cikin gidan da saurinta kamar zata tashi sama, Talba dake kokarin tashin motarsa yana kallonta ta danna door bell din kofar be kula ta ba ya ja motarsa zuwa gate ya hanna horn, dai dayan Police din ya dawo ya bude masa gate din ganin suna rike da Faruq ga kuma motar Leila dake bude a kunne yasa shi tsaya ya sauke gilashin motarsa.
“Lafiya?”
“Wallahi ba mu san abun da ya faru ba, Hajiya Leila ce tace a rike shi”
Talba ya kalli Faruq daga sama har kasa, be masa kama da yan ta'addaba, kuma ya san halin yar'uwarsa mafi akasari fadan da take da mutane ita ce bata da gaskiya. Hakan yasa shi tambayar Faruq dake kokarin fisge kansa daga rikon da Police din suke masa.
“Malam Lafiya?”
“Lafiya ce zata saka Police rike ni? Daman idan za ku taimaki mutum sai kun wulakanta shi”
Faruq ya fada cikin fusata, hakan yasa Talba ya bude motar ya fito ya nufo inda suke tsaye.
“Ku sake shi”
Ya fadawa Police din sai suka saki Faruq, Talba ya saka hannayensa aljihu yana kallon Faruq.
“Bari na fada maka wani abu, ba a min tsawa kuma ba a fada min bakar magana, amman na maka uzuri saboda na fahimci kana cikin bukatar taimako ne, and bana son na yi ma mutun wani abun ta dalilin taimako, da ace a hanya na hadu da kai da zan iya maka cin mutunci fiye da kima, now tell me miya faru”
Kalaman da Talba yai yasa Faruq sasautawa zuciyarsa domin ya fahimci ba fada Talba yake son yi da shi ba, idan ma sun yi fadan ba riba zai ci ba.
Cikin bacin rai Faruq ya fadawa Talba abun da ya faru, sai Talba ya girgiza kai ya lumshe ido ya bude, ba dan baya iya bawa kowa hakuri ba, da sai ya bawa Faruq, domin ya fahimci halin da
yake ciki.
“Ka manta da abun da tai maka yanzu fada min wani iri taimako kake so?”
“Mahaifiyata ce ba lafiya”
Faruq ya fada domin yana jin cewar shi ne kawai abun da zai iya fada a halin yanzu, kasancewar shi ya fi damunsa. Talba ya juya ya koma cikin motarsa ya bude ya shiga ciki ya zauna, wani karamin diary ya dauko yai rubutu akai, sannan ya bude wani guri a cikin motar ya dauko 100k ya fito ya nufo Faruq.
“Ga wannan Allah ya bata lafiya, and idan kana neman taimako a foundation din Mahaifina ka tuntubi wannan number, su za su tantance komai su sanar mana”
Ya mika masa number bayan ya bashi kudin. Faruq ya saka hannu biyu ya karba cikin jindadi.
“Na gode sosai Allah ya saka da alheri, ya kara sutura”
Uffan Talba be ce masa ba balle har ya amsa da Ameen, sai juyawa yai ya nufi motarsa, yana kokarin shiga yaji dayan police din na fadin.
“Hajiya tace a rike shi, ku rike shi”
Juyowa Talba yai ya kalli Police din, sai suka fasa rikon Faruq.
“Hajiya Babba ba Leila ba ita ta kira ni yanzu”
Da kai Talba yai ma Faruq alama daya wuce sannan ya shiga motarsa ya danna horn suka sake bude masa gate din yai ribas ya shiga cikin gidan. A harabar Entrance din ya faka motarsa sannan ya fito ya nufi kofar falon kamin ya karasa sabuwar mai aikin Momy ta bude kofar da sauri da alama fitowa za ta yi.
“Yauwa ranka ya dade Hajiya tace na kira ka”
Shiga yai cikin falon hannayensa zube a aljihu sai kamshi turare yake zubawa, tsaye ya samu Momy Leila na gefenta dayan mai aikin Momy Zulai tana tsaye nesa da su, domin wannan karon har masu aiki biyu Momy ta dauka. Yana kallonta ya san ranta a bace yake, can kuma ya kalli Leila da ke hawaye, kamin ya kalli Kabir dake zaune rike da waya yana kallonsa.
“Talba haka zamu zauna mutane suna ci mata mutunci kana daukar side dinsu”
“Ta fada miki Abun da tai masa?”
“I don't care, amman komai tai masa ai be kamata ya rike hannunta ba, har ya fada mata bakar magana alhalin shi yanzo nema a gidansu, har kuma ka bar shi ya tafi”
Talba be ce komai ba, har Mairo ta shigo tare da police din da Momy tasa ta kira daman shi da Talba ta ce ta kira. Yana shigowa Momy ta nuna shi da yatsa.
“Wannan ya zama na karshe da wani zai zo ya takura mana kofar gida, karka sake barin kowa ya shigo mana ba tare da saninmu ba, idan makamancin haka ya sake faruwa a bakin aikinka, ba wai a gidan nan kadai ba, no ka daina saka Police Uniform kenan har a bada mark my words”
“Ayi hakuri ranki ya dade Inshallah zan kiyaye”
Cewar police din sannan ya juya ya fita. Da ido Talba yai ma Mairo da Zulai alamar su fice daga falon sai suka fice da saurinsu.
“Wannan abun yayi yawa Momy, ya kike Leila ta zama? Ba fa Amal bace, taya Leila zata raini yara masu tarbiya idan tana wannan halayyar? Saboda wani ya zo nema daga abun da Allah ya wadata mu da shi sai ya zama abun wulakantawa? And ji yadda kike fadawa Police din nan magana kamar wanda yai wani babban laifi”
“To ya kake son na yi? Haka zamu yi ta zama Leila bata da yanci a gidan nan? Haka zaka rika mata idan kun yi aure ka bar ko wane kare da biri suna cin zarafinta? Shi ne jindadinka?”
Talba ya kalli Leila cikin yanayi na rashin jindadi.
“I wonder what kind of woman zan aura! Akwai karamci tarbiya a tare da ke, ba zan iya daukar wannan halin na ki ba kina bukatar ki canja rayuwa Leila...”
“Kai kake bukatar canja rayuwa ba ni ba...”
Ta fada mishi kai tsaye sannan ta nufi upstairs. Momy ta kara da nata.
“Kana fada min Leila bata da tarbiya ko? An maka dole ka aureta ne? Ko kuma kana son ci min fuska ne Saboda ba ni na haife ka ba?”
Talba ya kalleta da sauri, Kabir ma mikewa yai tsaye sai a lokacin ya saka bakinsa a maganar.
“No haba Momy... ”
Momy ta daga masa hannu.
“Na san abun da yake nufi, duk abun da kake kana yi ne saboda ba ni na haife ka, kuma na sani, daman tsintacciyar mage bata taba zama mage ba, amman karka manta ni na raine ka, ko da ka bude ido baka san mahaifiyarka ba ni ka sani, na raine kamar uwa, so weather you like it or not I'm still your mother, karka manta da wannan...!”
Tana kaiwa nan ta nufi upstairs ya bita da kallo kalamanta na ratsa kowane lungu da sako na zuciyarsa. Leila ma da bata karasa hayewa ba juyowa tai ta kalleshi cikin yanayin da ke nuna bata jidadin kalaman Momy ba, balle kuma Kabir da ya tsaya kamar hoto yana kallon dan'uwansa cikin yanayi na rashin jindadi.
<<<<<>>>>>
Na ce ba? Baturiya ko ba indiya ta taro mach da Faruq yau 🤔
Anya Leila zata ga Annabi kuwa? 😔
Momy ta kyauta a kalaman da tai ma Talba saboda Leila?
Wai ina Aminatun mu ne?
Shin kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin da kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya, domin siye ko sari ku tuntubi Ramla incense ta wannan number 07038392576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa
*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min! Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*
Juyawa Talba yai ya fice daga falon, sai Leila ta sauko da sauri zata bi bayansa, kamar wanda ta tuna wani abu sai kuma taja ta tsaya cikin yanayi n rashin jindad
“Yanzu ai kin jidadi ko?”
Kabir ya tambaya yana gyara shirt din jikinsa. Sai ta kalleshi cikin yanayin damuwa domin har ga Allah bata son Talba ya shiga damuwa duk kuwa da irin son da take ya canja bata son ace saboda ita Momy ta yi masa Wani abun bacin rai domin ba su saba haka.
“Wane irin dadi kuma? Kana jin kalaman da Momy ta fada masa fa”
“Eh ai ke kika ja, ke dai burinki wulakanta mutane”
Yana kaiwa nan shi ma ya nufi kofar fita falon cikin bacin rai, duk irin rashin jituwar da suke samu da Talba baya son wani abun bacin rai ko damuwa ta same shi, kamar yadda Talba ma baya son ganin bacin ran Kabir sai dai dukansu sun san cewa ba a komai na rayuwa suke shan inuwa daya ba, musamman ma Talba da yafi kowa girman kai a gidan.
Juyawa tai ta hau stairs din ta nufi dakin Momy, ko knocking bata tsaya yi ba ta tura kofar ta shiga kamar zata fasa kuka.
“Haba Momy wannan abun har ya kai ki fadawa Talba irin wannan maganar ne?”
Momy dake zaune gaban madubi tana kokarin cire awarwaron hannunta ta juyo ta kalleta da mamaki.
“Ba ki kalmar da yake jifata da ita ba?”
“Da ni yake ba da ke ba”
“No cewa yai baki da tarbiya, kai tsaye na fahimci inda kalamansa suka dosa, tun ba yau ba ai na lura da yadda ya canja kamar mai son yai