Showing 231001 words to 234000 words out of 247770 words

Chapter 78 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10426

ɗaga su, da gani ya sabar masu da hakan, da alamu baya ƙyamatar su, suma sun fahimci hakan, da kallo nake binshi da nake tsaye cen baya, sun matuƙar burge ni, masalan Yariman nawa da yake da zuciya ta kwarai irin wadda ake so dukkan musulmi mawadaci ya samu.

Nan fa suka shiga kai mashi koken su, duk da sun san cewa ko ba komai zasu kwashi tsawon kwana goma suna cin abinci mai rai da lafiya, harda shanu ake yankawa, duk lokacin da Yariman ya kawo masu ziyara.

Kuɗi ya koma mota ya fiddo ƴan bandir bandir ɗin dubu dubu, nan ya shiga rarraba masu, sosai sukayi murna da jin daɗi, hatta da tsofaffin da suke kwance basa lafiya sai da ya shisshiga ya gansu, suma ya masu alheri mai yawa, sannan ya buƙaci da a kira likita zasuyi magana dashi.

Koda likita yazo sun tattauna abubuwa masu yawa, ciki harda kai marasa lafiyar zuwa asibiti mai kyau, da kuma zasu ɓullo da har kar samar da magunguna kyauta ga mazauna sansanin, muddin rashin lafiyar bata yi tsanani ba. Sannan yana so zai gina masu asibiti mai rai da lafiya, zai ɗauki ma'aikatan da zai dinga biyan su albashi cikin aljihun shi, tare da kawo waɗanda zasu dinga koya masu sana'o in hannu ga masu buƙata, domin dogaro da kansu.

Aikau kaman su rungume shi, saboda tsabar murna, wasunsu kuka suke yi, Abunda nima ya ƙaryar mani da zuciya kenan na shiga rera nawa kukan, Allah na gode maka, Allah na tuba, rayuwar da nayi sai nake ganin babu wanda ya kai ni shan wahala, ashe akwai waɗanda suka fini, wasu an kashe masu mazaje, wasu sun rasa ƴaƴan su, wasu sun rasa iyayen su. Kuka nake rerawa mai cin zuciya. A hankali ya shiga takowa zuwa inda nake tsaye, ba wanda ya kula da kukan da nake ta faman yi ma, su kansu fadawan hankalin su ya ɗauku wajen rage cunkoson mutanen dake son kai hannun su ga jikin Ya Ameen ɗin da har suna mai neman kada shi, jikin shi kuwa yayi futi futu, masalan ma ƙafufun nashi dake sanye cikin takalma masu lanƙwasar kalar na sarauta. Amman haka yake daurewa yana ta sakin murmushi yana raba masu kuɗi.

Tabbas zuciyar Ya Ameen mai kyau ce, yana da imani sosai, ga tausayn na ƙasa dashi, tin fara soyayya ta dashi, ban ci karo da Abunda ya ƙara sanya ni alfaharn samun shi a matsayin mijin nawa ba kaman yau.

Tausayin su ne ya kama ni, ashe ni ina cikin aljanna ne, ko ba komai zanyi aikin da za'a biya ni, kuma a cida ni, zan ɗinka ma kaina sutura, su kau wasunsu yagaggun kaya ne jikin su, wasu ma kusan kana kallon tsuraicin su, ga rashin ruwa, wasun su yunwa duk ta busar dasu, ga ƙazantar makewayi, "Ya Allah Na tuba Allah ka yafe mani"

Abunda nake furtawa kenan, har zuwa lokacin da naji ya rungume ni yana lallashi na, ai sai na sake sakin wani marayan kukan, "ya Ameen sun bani tausayi, don Allah ka cigaba da taimaka masu" Abunda nake furtawa kenan cikin kukan nawa.

Gyaɗa mani kai ya shiga yi, yana mai ɗan bubbuga baya na, cikin shigar lallashi."I promise u my wife"

Tsaye sukayi suna mai kallon mu. Ganin hakan ne ya sanya shi bayyana masu cewa nice wadda zai aura.

Nan fa wuri ya sake ɓarkewa da hayaniya, ƙoƙarin ƙarasowa suke inda nake tsaye su taɓa ni.

Ban hana su ba, kaman yanda shima bai hana su ba.

Wata yarinya ce ta ruga sosai zuwa jiki na, tana mai faɗin *Inna jaki tafi dani gidan ki?*

Tausayi ta bani, zuƙunnawa nayi sosai na ɗago ta zuwa saman kafaɗa ta, ba zata wuce shekara uku da rabi ba.

"Ina maman ki?"

Na tambaye ta.

"Bana da Mama"

Ta furta cikin maganar da bata ida kwarewa ba.

Da kallo na bi sauran matan dake tsaye gefe, gyaɗa man kai sukayi suna kai shaida mani wani hari da aka kai ƙauyen su Bomb ya tashi da Mamar tata, ita kaɗai ta tsira a gidan.

Kayan dake jikin yarinyar sun yi dauɗa duƙun duƙun, ga zarni haɗi da wani irin wari dake tashi daga jikin yarinyar, kaman zanyi amai, haka na daure na rungume ta ina mai sake sakin wani kukan.

"ya sunan ki?"

"yaaagana"

Ta furta itama a hankali, tana ta zaro idanu, ganin bata san me nake ma kuka ba, lokaci guda ta shiga ƙoƙarin sauka tana faɗin "kiyi haƙili Inna bansan zakiyi kuka ba, nima kullum sai nayi, saboda Mamana bata nan ba mai bani haƙuli"

Ai bansan lokacin da na kuma rungume ta ba tsam tsam a jiki na, har yanzu kuka nakeyi, Amman mara sauti, kuma har yanzu ɗin ya Ameen yana tallafe dani a jikin shi.

Ajiye ta nayi ina mai zaro kuɗi a jikka ta, na shiga cewa "Wa zan ba amana, kullum a siya mata wani abu mai ɗan daɗi taci?"

Nan fa aka fara turereniyar cewa "Ni, ni ni zaki ba hajiya"

Wata mata dake tsaye cen baya, duk abun nan da akeyi bata ko motsa ba, tayi shiru, ga dukkan alamu akwai Abunda ke damun ta sosai.

Ita na yafito da hannu.

Damƙa mata kuɗin nayi ina mai cewa "gashi ki ajiye mata, don Allah ki kula da ita sosai kafin in dawo"

Sannan na zuƙunna na riƙo hannun ta ina mai Damƙa ta ga matar nake ce ma Yaganar "ga Maman ki nan daga yau, zata dinga kula dake, zan dawo in tafi dake kinji?"

Cikin murna da tsalle take ta cewa "yaaaa nima znaci bickin kaman su Baba gana"

A hankali Ya Ameen ya janye ni, ganin ina shirin sakin wani kukan, nan mukayi masu sallama muka baro su cike da farin cikin kuɗin da Ya Ameen ya basu, ya sanar dasu cewa su kiraye shi nan da kwana biyu, domin cika masu alƙawurran daya ɗaukar masu.

Ko a cikin mota kukan nake yi, tabbas yau zuciya ta ta sosu, imani da tsoron Allah ya ƙara kama ni, ban taɓa sanin haka sansanin ƴan gudun Hijira yake ba sai yau, duk da gwamnati na iya nata ƙoƙarin, Amman wasu ne suke samun na abinci a wurin, suna sama da faɗi da kusan duk wani taimakon da zai je masu, masalan na ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Lallashi na ya shiga yi, yana faɗin in da yasan haka zan kasance da bai je dani wurin ba.


Nan nake roƙon shi da ya taimaka ya ƙara sama masu da ruwan sha ɗana amfani, ya ƙara masu yawan makewayi. Da kai ya shiga amsa mani, cikin shigar lallashi

Haka muka koma masarauta, duk yanda yaso ganin walwala ta, saidai kaɗan.

Mai martaba ya yaba mashi, ya jinjina mashi, fada tayi alfahari da samun suruki kaman shi, masalan da labarin abun alherin da yaje yayi masu ya iso kunnen mai martabar tun ma kafin mu dawo.

Haka mukayi sallama dashi yana mai ƙara bani haƙuri, Baisan haka nake da kararriyar zuciya ba, da bai je dani ba, kuma tabbas yasan hakan ne, duk wanda yaje wurin nan sai imani ya kama shi, ko shi lokacin farko farkon da ya fara zuwa, gagara bacci yake yi, hakan ce ta sanya kusan lokaci lokaci yana hanyar zuwa wajen nasu, hakan ce ma ta sanya sukayi sabo har haka dashi.

Duk da naji ba daɗi tafiyar tashi, Amman bana da yanda zanyi, idan da rabo dai yau saura kwana sha biyar komai ya kammala. Ko yaya Ummata take? Ina buƙatar fa in kira ta, domin jin lafiyar ta, haka na juya cikin gidan, baya na haɗiman da suke mani hidima ne biye dani.



*********

Umma na zaune a falon nata ita da Hajiya Zainab suna kuma tattauna yanda abubuwa zasu kasance, basa so ko alama hidimar bikin nan a samu matsala, masalan ta ɓangaren hajiya Kubran, ita da so tayi ma ba zata yi taron komai ba, kawai zata tattara ta tafi gidan nasu kaman yanda Mai martaba sarki baffan nata ya buƙata. Hajiya Zainab ɗince ke ce mata aiinsha Allahu ba abunda zai faru ma, masalan yanzu da kowa idan yaji ita ɗin wacece dole ne a jinjina mata, kuma itama Hajiya Kubran matsalar asali ne ta fake dashi tana ta wannan hakan, to yanzu zata fasu kowa ma yaji.

Umman saidai tayi murmushi, ta lura tin lokacin da suka fahimci ita ɗin wacece, wani girma na musamman suke bata, harda Dad kuwa, shi da yake ma mai gidan ta, shi kau ta ɓangaren shi wani girma da ƙimar ta yake gani, Sam ya kula abun duniya baya gaban ta, domin idan da yana gaban ta, ba zata taɓa tsallake masarautr tasu da take da ɗinbin girma da kuɗi ba.

Suna tsaka da tattaunawa ne, mama Talatu tayi sallama.

Karo na farko kenan da ta taɓa shigowa sashen Umman, domin suna jin tsoron Hajiya Kubra ta ga shigar tasu ta kore su, masalan Mama saude da take so ta shisshigi ma Umman, domin yanzu ta kula Alhaji yana matuƙar jin maganar ta.


Gefe ta samu ta raɓe ƙasa, kaman yanda take yi sashen Mom.

Da hannu Umma ta nuna mata bisa kujerar dake gefen ta.

"Haba Talatu meye na zama ƙasa kuma? Ki zauna saman kujera mana" umman ta faɗa cike da girma.

A hankali ta ɗan ɗosana.

"dama masu haɗa kaya ne suka ce a sanar naku an kammala"

Ta faɗa tana ɗan bin sashen da kallo haka kaɗan, cikin ran ta Allah kaɗai yasan me take rayawaa.

"Kije ina zuwa" cewr Hajiya Zainab, domin ta kula Mama talatun munafuka ce, bata so take shiga hidimar Umman, domin yanzu ita ba sa'ar su bace, dama cen tsautsayi ne ya kai ta shiga cikin su munafukai suna ƙuntata mata.

A hankali ta miƙe tana faɗin "to Hajiya a fito lafiya"

Da kallo su duka suka bita, nisa wa Hajiya Zainab tayi, "umman Suhana sai fa kin kiyaye mutanen nan, kin san fa irin zaman da kika yi dasu, kuma ni nasan har yanzu akwai wani abu a cikin zuciyar tasu"

"Ba komai Hajiya, ni da zuciya ɗaya nake zaune dasu, Allah na nan, kuma ba abunda suka isa suyi mana" ta faɗa itama cike da ƙwarin guiwa tana ɗan nurmusawa.

Hajiya zainab ɗince ta miƙe tana faɗin bari inje wajen mutanen cen, domin Bilal ya fita tin ɗazu, kinga kuma ya kamata ace an sallama su kinsan nan da sati ɗaya ƴan kankiya zasu iso, to suma Alhaji ya bada kuɗin gyaran sashen nasu"

Da to Umma ta bita, tana maida hankalin ta kan wayar ta da ta ɗauki tauwwa.

Hajiya Khaltum ce. A hankali Umman ta ɗauka tana mai sakin murmushi.

"Ran Hajiya ya daɗe" cewr Umma tana mai sakin dariya.

"Wannan taku ce Umman Suhan, ya guda ya hidima?"

"Duk lafiya lau wallahi, ya yara ya jama'a da su Eesher?"

"Duk suna nan lafiya lau Umma, na kira ne akan maganar da mukayi dake, lokaci yayi da ya kamata in turo mai gyaran jiki ga amarya fa"

Ɗan murmushi Umma taja tana mai cewa "Hajiya na maki laifi fa, gaskiya ai mamana ɗin ma tana nan garin ku, ba zata dawo nan ba ma sai an ɗaura aure"

Hajiya Khaltum cikin mamaki take faɗin "kaddai kice Adamawa?"

"Eh Hajiya nan Adamawa dai"

Ɗan murmushi Hajiya Khaltum ta saki, tana mai cewa "shikenan kinga ma ta kwana gidan sauƙi, ki kwatanta mani kawai gobe sai muje da mai gyaran da kaina, kuma insha Allahu zuwa gobe kayan zasu iso, indai kina gida"

"Ina gida Hajiya nagode Allah ya bada ladar zumunci, babu Abunda zan ce maki saidai Allah ya biya ki abinda kike mana, nagode, insha Allahu zan maki text ɗin address ɗin inda take ɗin"

"To ba damuwa, ai ba godiya tsakanin mu Umma, kun wuce nan, Allah ya basu zaman lafiya" cewr Ammi.

"Ameen Ameen, shima Salim Allah ya bashi wadda ta fi Suhan komai a rayuwa" cewr Umman itama, da Ameen Ammi ɗin ta bita tana mai cewa to shikenan sai na saƙon.


Tana kashe wayar kira na ya shiga wayar.

To na gaji, daga kwanciya sai wanka da cin abinci da sallah, komai yi mani akeyi, latsa waya shine babban aiki na, gashi Ya Ameen hidindumu sunyi mashi yawa, inma kinga ya kira ni, ko ni na kira na samu to dare ne.

Gaida ta na shiga yi, ina mai tambayar ta lafiyar ta.

Cikin murmushi take amsawa, tambaya ta take ya sabon wuri? Shiru nayi bance ƙala ba, na ma rasa ta inda zan fara, ce man tayi "kinga Mamana nasan dama zaki kira, saboda haka nake so da ki adana tambayoyn ki, yanzu ba lokacin su bane ya zuwa yanzu dai na san kin gansu da cewa kina da asali da kuma gata, saboda haka ki cigaba da yi mana biyayya Allah yayi maki albarka"

Da Ameen na amsa, murya a dusashe, ban ɗauka haka zata ce mani ba, har yanzu ina cikin ɗan duhu fa, ban gama tantance komai ba. Abunda nayi ƙoƙari dai shine ganin na saki jiki da haɗiman dake man hidima, inda su kuma basa samun damar yin hakan, saboda tsari irin na gidan sarautar, ko su Fulani sau ɗaya nake ganin su idan naje gaishe su da safe, mai martaba ma haka. Saidai babu abunda na nema na rasa, komai akwai shi enough ba matsala, kawai dai kaɗaici ke dake damu na, gashi a gidan babu wata yarinya mace tsara ta. Su Raihana na kira na lallaɓa su akan cewa su taimaka su taho da wuri, saboda wannan amaryar dai ita kaɗai ce kullum a ɗaki, sai Afnan da kan kira ni akai akai tana zaulaya ta wai amaryar Yaya.


Umman ce ta sanar dani cewa wai Ammi na nan tafe gobe inda nake da mai gyaran jiki.

Nayi mamaki, gaskiya kirkin Ammi har yayi yawa, ace yaron nata ma bai samu auren nawa ba, Amman tsaye take kyam akan hidimar tawa, kaman dama cen ta samu ne.

Al'ajabi na shiga yi Umman na taya ni, sai sanya ma Ammin albarka take yi, nima ina jin daɗin hakan, wata irin ƙima da darajar Ammi da Sir Salim nake gani a idanun nawa. Da "to" na amsa mata tana mai kashe wayar tace in da wani abu in kira ta.


*******


Fulani ce ta shigo tana mai shaida mani cewa an shirya yin kamu ranar Alhamis saura kwana biyu ɗaurin aure, saboda haka sai in shaida ma angon nawa domin ya sanya shi cikin programme, saboda suma duk zasu taho cen ne ayi kamun.

Kiran Ya Ameen ɗin nayi bai ɗaga ba, hakan ce ta sanya na tura mashi saƙon text,bai bani amsa ba, sai cen da marece ga kiran nashi yana bani haƙuri, ayyuka ne suka taso shi gaba, ga shirye shiryen ɗaurin aure, anan ma ne yake shaida mani wai ba za'a kawo mani lefe ba, ga Abunda masarauta tace. Da "to" na bishi ina mai sake jinjina ma ƙoƙarin da yake yi, da murmushi akan fuskar shi yake sanar dani cewa "babu Abunda ba zan iya yi a kanki ba mai kuka ta"

Nima dariyar nayi ina mai cewa "na gode ma Allah, ko nayi ina da mai share man hawaye na, ya kuma lallashe ni"

Yaji daɗin maganar tawa kuwa. Nan ya biye mani muka yi ta fira cike da shauƙin so da kuma ƙaunar juna.

Washegari sai ga Ammi, nayi mamakin yanda kai tsaye na ganta cikin gidan, har ɗaki nawa ita da Fulani, sai a lokacin ne na fuskanci inda kaman da nake gani a fuskar Fulani ta fito.

Itama da mamaki sosai tazo ta kama ni tana mai rungume ni, duk ƙoƙarin da nake na zamewa daga jikin nata kuwa in durƙusa, ta riƙe ni gam a jikin nata, tana ta salati da tasbihi ga Allah.

Tun jiya da Umma ta mata text ɗin address ɗin ta kira ta domin taji haƙiƙanin gaskiyar Abunda ya kai Suhan masarautar su ɗin. Saidai bata samu ba, haka yau tin da wuri take doka ma Umman kiran, Amman still bata samu ba.

"Suhan ashe ke tamu ce? Ashe ke jini na ce Suhan? Gaske Naji ƙaunar da nake maki har cikin jinin jiki na" ta shiga furta wa, tana mai zaunar dani gefen gadon, itama Ammin ta zauna.

Su kau haɗiman

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login