Showing 93001 words to 96000 words out of 247770 words
ɗin zuciyar shi na raya mashi zuwa dasafe zai kira iyayen nashi domin su san ya isa lafiya.
Ban san wa zan tambaya ba game da tafiyar Ya ameen ɗin ba, beside ma ni meye nawa a ciki? Ai yana yin aikin shi ne, ko yaje zai dawo ne, saidai na rasa dalilin da yasa nake jin zuciya ta ba daɗi sam, duk da yace Ya Bilal ɗin zai mani komai na dangane da karatu na, shima na kula yana da kirki don ma zance yafi Ya Ameen ɗin sakin fuska nesa ba kusa ba.
Washegari da tafiya ta Yayan namu koda Afnan tazo mani da maganar cewa suma Yau zasu wuce ban ko wani damu ba sosai, bansan kuma dalili ba, saidai ta yiman Alkhairi kaman yanda ta saba, a bakin ta ma ne nake jin wai Ya ameen ɗin America ya tafi yin wani aiki, Amman wai ba zai daɗe ba zai dawo.
To sun wuce dai, haka ma Hajiya Zainab da Alhaji Auwalun sun koma Katsinan da motar da dangin mijin Hafsat ɗin suka bata.
Su Goggo Aisha ma da Goggo Fatima da iyalan su duk sun koma, tare suka tafi da ƙanen nasu watau Yaya Auwalun, sai ƴan biyu ne aka bari da Kaka zuwairan su sai ƙarshen sati za'a maida su.
Kafin tafiyar Hajiya Zuwairan tayi ma Ummanmu sha tara ta arziƙi, ganin yanda umman tawa ta tsaya mata ka'in da na'in wajen hidimar bikin nasu, duk da ta san ba don abun duniya tayi ba, Amman saida ta bata maƙudan kuɗi da kaya sosai harda ni ma, fafur taƙi amsa har saida tace zata je ta gaya ma kaka zuwairan ne yasa ta amsa suma ba duka ba, a cewarta ai an zama ɗaya.
Gidan ya koma shiru tsit kaman babu mutane, inda ma zaka ji hayaniya shine sashn kaka zuwairan da akwai ƴan yara ƴaƴan su Aunty Hassana da Hussaina ɗin, shima ba wani fita suke sosai ba, in Kaga sun fito to wajen wasa zasu su hau lilo.
Hnakalin ummata ya kwanta ganin babu wanda ya kuma tada maganar da taji ɗin harma mutane sun watse kowa ya koma muhallin shi, bamu da matsalar komai ga kuɗin da ya Ameen ya bamu kwanaki basu ƙare ba, ga kuma sha tara ta arziƙi da Hajiya Zainab tayi mana, ya sanya hankalin mu kwance bamu da matsalar komai.
Kullum sai umman tawa ta sanya ni naje sashn kaka zuwairan na gyara masu, to suma basu taɓa tada man wani zance ba, illa iyaka dai sanya mani Albarka da kullum suke yi tinda Alhaji Mustaphan ya gaya masu yanzu yana kan bincike ne su ajiye maganar gefe.
Ta fannin Hafsat kuwa kullum muna waya sosai, har take sheda mani suma ƙarshen wata zasu wuce don Allah in zo kafin ta tafi, nan nake ce mata saidai yanda hali ya bada, domin yanzu kaman an zareman wata tsoka daga jikina nake ji na kuma rasa dalili.
Duk da umman tawa ta kula da rashin walwalrr tawa, sai ta dangana hakan dankaɗaici, da ke damuna a kwana biyun ga kuma kwazzabar maree da nake fuskanta, ba damar in fita sai an yada man habaici ko an jefeni da kalma mai muni.
Da su kaka zuwairan suka tashi tafiya, bansan inda ummata ta samo daddawa da kuka dasu kuɓewa masu kyau ba taba kaka zuwairan, aikau tasha Albarka kuma taji daɗin kyautar domin su tsofaffi ne basa yi saida tuwo. Har mot amuka rakasu da duka sauran ƴan gidan muma ɗaga masu hannu har suka fice.
Alkhairi daɗi ne dashi wai wannan ɗan abun da ummata tayi ma mahaifiyar Alhajn saida ta faɗa mashi, aikau yana dawowa sai ga wata sha tara ta arziƙin ya aiko mana dasu jin daɗin kyautata ma mahaifiyar tashi da mukayi da kula da ita a ɗan zaman nata a cikin gidan wanda ko ita matar tashi ma bata yi saboda tsabar girman kai da jin ita ɗin wata ce.
Mun samu sauƙi kam ta fannin hajiya Kubran sosai, kwana uku tsakani da tafiyar su Kaka zuwairan sai ga Mama Talatu da saƙo wai daga wajen hajiyar an maida mu bakin aikinmu.
Ummanmu baiwar Allah sai jin daɗi take yi, tana kimtse kimtsen komawa bakin aiki, domin ita kanta Hajiyar ta sheda cewa Mahaifiyar tawa ta iya girki ba kaɗan ba, Sam basa jin daɗin girkin kukun nan masalan ma Alhaji.
Lokacin da ta sheda mashi maganar son a maida mu aikin bai musa mata ba, sai a cewa yayi hakan yayi daidai.
Nikau a cikin zuciya ta Sam banji daɗi ba gani nake yi kaman za'a daƙile mani maganar karatu na ne, saidai kuma a ranar ne sai ga kiran Bilal ɗin wai in miƙo mashi takaddun na, saboda ayyuka sun rincaɓe mashi ne ya sanya bai amsa ba saida ya gama daidaita komai a office sannan.
Tambaya ta ya shiga yi bamu da matsalar komai dai ko? Babu kam na bashi amsa gami da juyawa na nufi cikin sashen namu, ko ba komai hankali na ya ɗan kwanta, naga alama kaman Bilal ɗinma zai tsaya mani kaman Ya ameen ɗin, to nima dai dama Abunda ya dameni kenan, bana son dukkan wani abu da zai yi mani katanga da cikar nawa burin.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
Baya buƙatar tambayar abokin nashi komai akan lamarin karatun Suhan ɗin domin ko ba komai ya san amini nashi zai riƙe amana yayi mata dukkanin Abunda ya dace. Hakan ce ta sanya bai kuma tambayar shi ba akan lamarin nata, ko waya sukayi tau fa zancen da ya shafi kasuwanci ne da ma'aikata sai kuma Abunda ya shafi gida, tinda Yanzu Bilal ɗinne mai yin komai, shi ma Alhajin hidimarshi tasha kanshi da yawa sosai, gashi mai girma shugaban ƙasa ya bashi Ambasador a ƙasar ta Ƙatar, saboda yanda ƙasar take da arziƙin man fetur ya sanya yake ayyuka biyu ga aikin da yake yi ga kuma hidimar mai da ya shiga ka'inbda na'in nan fa likafa ta cigaba arziƙi ya linka nada, tini ya cema Hajiya Kubran ban wuri, duk da itama ba zaune takeba Business ɗinta kawai take yi hankalinta kwance.
Hankalin Al'ameen ya ɗan kwanta tinda yau Bilal yayi mashi maganar an samu admission ɗin Suhan ɗin, tinda ya baro Nigeria ɗin yau tsawon wata biyu cikin na uku kenan Bilal ɗin bai taɓa mashi maganar ta ba sai yau, har ya fara tinanin anya kuwa yana yin alƙawalin da ya ɗauka? Saidai ya san dole ne yayi mashi uziri tinda ya san irin tarin ayyukan da suke gaban shi, wannan ce ma tasa Bilal ɗin ya roƙu su iyayen yarinyar da zai aura ɗin akan A ƙara mashi wata biyu ya gama settling duk wasu muhimman abubuwa dake gaban shi, lallai shi kanshi ya jinjina ma Al'ameen ɗin ga irin ayyukan da yake fama dasu kusan yana running kamfanoni kusan aƙalla bakwai a faɗin nigeria kuma yana da ma'aikata ba iyaka wanda kullum fama yake da tarin jama'a matasa da kuma ƙorafe ƙorafe su.
Yaji daɗin jin wannan kalamn saidai shi inda yaso ta samu ABU zariya, sai gashi ba cen Allah ya cida ita ba, ansha daga da Umman akan nisan da suhan ɗin zata yi da ita kuma ba mai kula da ita ce sai Allah, Bilal ɗinne ya tausheta yace ta bara Allah ɗin, atafau tace ita in karatu ya wuce nan Abujan ba zata yarda ba, dole tasa ya kira Alhaji Mustapha saida fa yace mata zai sa masu kula da ita ne yasa ta yarda saboda ganin girman Alhajin, Amman shi Al'ameen Sam baisa baki ba ganin Alhajin nashi ya sanya, kai shi fa tinda ya tafi bai ƙara ji daga garesu ba, dama Suhan ɗin ba number ɗin shi ta cen ƙasar take da ita ba, balle ta kira ta samu, ko a WhatsApp ɗinma ta dena ganin ɗuriyar shi sai ta bar ma kanta cewa ayyuka ne sukayi mashi yawa in ba haka ba ai Al'ameen ɗin na wajensu ne, ta san haka kurum ba zaiƙi sanya baki akan a shawo kan umman tata ba.
Hafsat tini sun wuce, dakyal na samu naje mata sau ɗaya tin bayan bikin.
Nima yanzu abubuwa sunyi mani yawa shirye shiryen tafiya makaranta ta nake yi, bani da matsalar komai, saidai kula da nayi har yanzu umma ta jikin ta baya bata tafiyar tawa, idan na lura da hakan nima jikina kanyi sanyi, albarka nake so ta sanya mani ba wasu wasu ba, hakan ce ta sanya na zauna na nutsar da ita a hankali, tau ta dai ɗan saurareni kuma ta ɗan fahimce ni harma addu'a tayi man da fatan samun nasara akan Abunda zanje nema ɗin, kunsan a koda yaushe addu'ar iyaye itace abun so ga ƴaƴan nasu ba addu'ar banza ba ko Kaga uwa tana ta ƙunduma ma yaron ta ashar tana la'antar shi cikin zagi kuma tana so ace ya girma yayi albarka kuma ya jiƙanta ya sota, ai da wuya Kaga uwar da take la'antar yaron ta kuma ya girma yayi albarka, saboda addu'ar uwa ƙarɓaɓɓiya ce ba shamaki.
A kulliyaum sai Nihal tazo gidan nan, itace bata tafiya sai dare, kai in taƙaice maku tin bayan bikin nata da kwana biyu ta fara sintiri a cikin gidan, kuma Hajiya Kubran na kallon ta, ta kasa kwaɓa mata, a cewarta ai ba kurkuku ta kai yaran nata ba balle ace ba zasu fita ba, Saudat ɗin cema mai yin kwana biyu bata zo ba, Amman in ta kama suka zo ɗin har kwana suke yy. Ba wadda bata da jarin kanta take juyawa, hasali ma yanzu duk kansu suna aiki ne a wasu kamfanoni da aka buɗe suna jagorantar shi, saboda ɗimbin ilimn dake kansu, da yake Allah yayi ma yaran na Alhaji Mustapha ƙwaƙwalwar, Abie Kuwa tini ya koma ƙaro karatu cen ƙasar ta america tare suke da Al'ameen lokuttan da baya da lecture ya kan bi Ya Ameen ɗin Office yana taya shi ayyuka.
Bikin Bilal ɗin ya matso, duk a gidan su Ya ameen ɗin ake komai, saboda shi iyayen shi ba anan ƙasar suke zaune ba suma, babu Abunda ba'a aiwatar ba na Al'ada, nayi mamaki da ya Ameen ɗin bai zo ba, bashi har ina daf da tafiya makarantar.
A cikin estate ɗin da 'ameen ya gina wadda ya sanya Bilal ɗin yin lunching ɗinta kwanaki ba daɗewa ya ajiye matar tashi, Ummi ɗin yarinya ce mai hankali sosai da sosai, ga fara' a da son mutane kaman mijin nata, lokutta ya kan roƙi umman tawa akan ta barni inje gidan nashi wajen matar tashi, da yake yanzu sun saba da ummata sosai harma dani ɗin, na ɗauke shi kaman ya yana ne komai idan ina da buƙata na kan tunkareshi kai tsaye ne, ba don kar ace nayi butulci ba sai ince yafi Ya ameen ɗin daɗin mu'amala, domin shi akwai sakin fuska da faram faram, ba kaman Ya ameen ɗin ba da lokutta da dama magana ko murmushi ma sukan yi mashi wahala, duk da ba wai yafi Al'ameen ɗin kirki bane da hangen nesa.
Mun saba da Ummin Matar Bilal ɗin domin idan tazo kusan ma ince sashen mu take yini, saboda Hajiya Kubran yanzu bata cika zama ba, sai mu yini muna fira, har kitso na kan yi mata wani lokaci da yake na iya, sai kusan marece mijin nata kanzo ya ɗauke ta.
Wani abu ɗana kula dashi shine, yawan zuba man idanu da Ya Bilal ɗin kanyi lokutta da dama, masalan ma idan ya tadda ni ba hijab, gashi ni kuma ganin sabon d a mukayi dashi ne ya sanya ni bana ganin hakan a matsayin wani abu, ashe ban sani ba kuskure nake yi, ɗana kula da hakan ne sai na fara janye jikina ko in sanya hijab idan ya shigo ɗakin namu, ko gidan shi na rage zuwa, shima bansan dalili ba sai naga ya rage kawo Ummin tashi gidan namu.
Ban damu da hakan ba, illa iyaka dai bana yarda wani abu ya haɗa mu, ko maganar shirye shiryen makaranta ta ni nake yin abuna bana tsayawa jira, Tinda yanzu ina ɗan samun kuɗin aiki na, kuma an koma bamu abinci a gidan.
Ko ya kula ne shima? Sai naga duk ya sha jinin jikinshi, sai dai fa a zuciyar shi wani abu kan bijiro mashi a duk lokacin da yake tare da suhan ɗin, ba don yana so ba, tinda sai a yanzu ne ya ƙara yarda d a maganar Abokin nashi, Suhan ɗin nada wasu abubuwa da suke kaman maganaɗisu ga maza, duk namijin da zai ɗora idanu akan fuskar ta to fa abun nan zai ja shi har zuwa gareta. Sau da dama abokan shi kan mashi maganar Suhan ɗin saidai bai san dalilin shi na rashin ba maganar tasu muhimmanci ba.
***************************
Ƙarfe takwas a rabi na safiyar ranar Litinin ɗin da ta kama itace ta ƙarshen wata, wayar Bilal ɗin da take ajiye bisa side drower ce tayi ƙara, Ummi ce ta ɗaga ganin sunan da yake jiki *Friend* taga an rubuta, cikin sallama ta kara wayar a kunnen ta.
Daga cen ɓangaren aka amsa mata cikin sakin fuska da gani fara'a mutumen dake wayar da ita yakeyi
"Friend ya kike? Ina angon naki ne? Ko har yanzu bai tashi ba?
Cikin dariya itama ta mayar mashi, yau kam abun nashi ya bata mamaki wai Al'ameen ɗinne yau da zaulayarta haka?
" Ya tashi Ya Ameen yana toilet ne yana wanka, ya aiki?"
" Lafiya lau Pls idan ya fito ki faɗa mashi ya kira ni" daga cen ɓangaren ya amsa mata, to tace mashi tana mai bashi saƙon gaisuwa ga ameen ɗin.
Baisan dalili ba, yau kam hakanan ya tashi da kewar gida, duk da suna waya da sauran ƴan gidan har ya kan tambayi mudi driver Lafiyr umman suhan ɗin, Amman ita ko da alama bai taɓa tambayar ta ba.
Saidai yau ba zai iya jurewa ba, tin cikin daren ne tinanin ta ya matuƙar damun shi, sai mafarkai marasa daɗi da yake yawan yi kwanakin nan, shi kanshi ya rasa dalilin son tafiyar tashi ƙasar tashi. Amman gaskiya bai jin zai iya tsallake yau bai bar ƙasar ta amurkan ba.
A hannun Abie yanzu da ya riga ya ƙware da komai ya bar office ɗin, har ya haɗa jikka sai kuma ya koma ya zauna ya kira aminin nashi, fuskar shi babu walwala Sam, saidai wani fari daya ƙara, fatar nan ta murje kaman bature don in ba hausa kaji yayi ba babu Abunda zai hana kace mashi ba'indiye, ga gashin nan baƙi siɗik daya kwanta mashi har ƙyeya, ba aski kanshi saidai gyaran fuska.
Sanye yake cikin lallausan yadi ɗan ƙasar Turkiyya mai walwali anyi mashi ɗinkin gudluck, Al'ameen ɗin mutum ne mai kwarjini da haiba, duk wanda ya kalle shi sai ya sake waiwaya wa ya kalle shi.
Wayar shi ne da take cikin aljihun gabar rigar tashi ta ɗauki tsuwwa, ƙirar iphone 11 pro max ce da ko ƙasar tamu ta nigeria bata kai ga shigowa ba, sai faman tallar ta da ake tayi.
Ɗagawa yayi gami da cewa "Friend how far?" Bilal ɗinne ya shiga cewa "Shegen kaya, kayi wuyar ji fa mutumena, na san ayyuka ne sukayi maka yawa"
"Wallahi kuwa, Amman gani na shirya yanzu zuwa Nigeria nan da ƙarfe uku kazo ka ɗaukeni, domin yanzu haka kai tsaye airport na nufa"
"Wat?". Bilal ɗin ya amsa mashi ta ɗaya ɓangaren bai tsaya jin me zai ce mashi ba ya cigaba da faɗin
"Gaskiya bakayi shawara dani ba da ban barka kazo ba, yanzu haka kana dawowa komai zai kwaɓe bros, ina mai baka shawara, gobe ne Suhan ɗin zata tafi makaranta, ka bari har sai ta tafi sannan kazo, kasan yanzu abubuwa sunyi masu sauƙi sosai, sanin da Mom tayi yanzu baka nan, yarinyar na shirin ta a tsanake, domin yanzu babu damuwar komai a ranta, Amman fa ni a ganina"
Shiru yayi ta cen ɓangaren, sai kuma lokaci ɗaya ya koma ya zauna, yana mai sakin ajiyar zuciya mai ƙarfi har saida Bilal ɗin ya jiyo shi, dafe kanshi yayi, lallai fa shi wannan abun ya fara damunshi, yana buƙatar yaga kowa nashi, kusan yanzu wata bakwai kenan fa, lallai ashe ya yaudari kanshi da har yake tinanin sai Suhan ɗin ta gama makaranta tayi aure sannan zai dawo, sai gashi ko tafiya ma batayi ba ya fara kewar su.
Jin da Bilal ɗin yayi Al'ameen ɗin yayi shiru, ya san ya