Showing 126001 words to 129000 words out of 247770 words

Chapter 43 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10421

muskutawa, sannan ya fara magana.


"Ah Hajiya munji dalilin zuwan ki gidan namu, a haƙiƙanin gaskiya munji daɗi kuma mun yaba, duk wanda yayo tattaki daga nesan duniya yazo inda kake, da kuma ƙoƙon barar soyayya, kuma irin ta aure, a gaskiya ya cencenci yabawa da kuma karramawa, saboda haka ne muke cewa mun gode. To saidai kuma akwai wani hanzari ba gudu ba, ban sani ba ko an shaida maki yarinyar marainiya ce? Ni ne nan nake zaman mahaifinta, wanda kuma anan gidan aka haife ta, saboda wasu dalilai ne ya sanya bata tashi a gaba na ba, wanda duk da haka na yaba da tarbiyyar da ita Maryamar ta bata, sannan kuma shima yaron na wajen ki lallai mun yaba dashi kuma munyi na'am dashi. Idan dai har kun yarda da hakan, to ta ɓangaren mu babu wani damuwa, zai iya zuwa su daidaita kansu, zuwa wani lokaci bayan sun gama fahimtar juna sai a turo manyan nashi maza domin suzo mu sake tattaunawa"


Tinda malam ya fara magana Ammi ke sakin murmushi, lallai ita kanta babu Abunda zata iya cewa da wannan zuri'a saidai fatan Alkhairi. Godiya ta shiga zubawa tana cewa wannan ai ba matsala bane, Allah ya bar zumunci kuma ya ƙara haɗa kawunan su yaran.

Nan malam ya tashi ya shige ciki ya bar su, duk da ummata ta ɗan sha jinin jikin ta, bamu sani ba ko sarakutar ce ta fara?

Da haka suma suka miƙe suka shiga ɗaki domin kwanciya, ummata ta gyara ko ina tsaf, dama kasancewar ta mace mai tsafta, sai ta shimfiɗa ma Ammi manyan barguna masu taushi a ƙasn ta ajiye mata matashin kai da kuma marar nauyi na lulluɓa.

Saida Ammi ta cenza kaya zuwa doguwar rigar bacci sannan ta kwanta, tana mai yima ummata sai da safe.


Cikin dare umman tawa ta farka domin yin ƙiyamul laili kaman yanda ta saba, saidai ga mamakin ta, Ammi ce tsaye tana salla, lamoo umman tawa tayi tana ta ƙare mata kallo duk ba tare da ta lura da ita ba.

Ta Kai kusan awa guda tana sallar sannan ta tsagaita, gami da ɗaga hannu ta dinga kwararo addu'a cikin harshen larabci da ƙanƙan da kai wajen Allah. Tabbas ta burge ummata ta ƙayatar da ita, sai taji ta sake amincewa da lamarin matar, tabbas indai haka ne abunda ta gani, Allah yayi ma Suhan ɗin zaɓi mafi alkhairi, saidai fatan nasara da dacewa.

Saida taga Ammin ta koma ta kwanta ne, sannan itama ta miƙe domin gabatar da tata, wanda itama Ammin tana kula da ita, itama hankalin ta ya sake kwanciya da auren yarinyar matar, saboda ummata mace ce mai dattako da kamala, sai taji hakan ya matuƙar taimakawa wajen ƙara amincewa da mahaifiyar yarinyar.


Washegari ma babu ƙyama ba komai aka kai mata ruwan wanka tayi, duk da har yanzu ummata bata ƙara sakin jiki da Hajiya Khaltum ba, saidai hakan bai dameta ba, tabar hakan ne a rashin sabo da basu yi ba.

Sai da tasha ruwan koko da ƙosan da aka ajiye mata ne, sannan sai ga su Sir Salim Sun dawo domin tafiya da Ammin.

Kaman kar ta rabu da gidan take ji, rayuwar tasu a sauƙaƙe ta burge ta, ga karamci ga dattako, a haka sukayi sallama harda Malam da bai riga ya fita ba, ya bari sai yaga tafiyar ta.

Tin daga murmushn da Ammin tashi keyi, ya tabbatar da nasara da dacewa a al'amarin.

Wannan ce ta sanya shi jin kunya da ta sanya dole ya dinga duƙar da kai lokacin da yake gaishe su cikin girmamawa. Sun sake saki da al'amarin ko ba komai suna kyautata zaton ƙila lokacin fitar Suhanan ne yazo daga ƙuncin da take ciki.

Basu bar wurin ba, saida aka buɗe but suka dinga shiga da kayan abinci kala kala da kayan amfanin gida, sai kuɗi da umman ta ajiye masu rafer ta ƴan 1k guda ɗaya.

Dakyal suka amsa, ummata kuwa komawa tayi gefe akan fir ita ba wannan suke buƙata ba, sai da magiya da komai ne ya sanya Hajjo amsa ta shiga yi masu godiya da addu'a

Basu bar wurin ba har saida suka ga ficewar motar su Ammin daga Layin sannan suka koma gida cike da al'ajabin wannan mata mai cike da abun ban mamaki


*********************


Saida ya gama juye juye da tunane tunanen shi, sannan ya kira waya akan a kawo mashi mota zuwa a hotel ɗin da ya sauka.

Aiko sai ga mota sabuwa dal tear ledar, mai masifar kyau, an mata glass tint sosai ta yadda ba zaka iya fahimtar wanda yake ciki ba.

Bayan ya fito ya gani ne, ya koma ɗakin shi, saboda baya so su haɗu da idon sani, labari ya bazu a gari akan shigowar tashi ƙasar, tinda shi mutum ne na mutane, gashi matasa kowa ya san da zaman shi yanzu, tin bayan da akayi mashi naɗin babu inda hotunan shi basu zagaya ba a sassan ƙasar.

Laptop ɗinshi ya jawo ya shiga bincike sosai, saidai ya manta ƙasar tamu, ba ko ina bane ba ma wireless ke shiga ba, iya binciken shi da neman shi a yanar gizo, bai iya gano komai ba, har dai ya haƙura ya ajiye ya shiga wanka.

Shiryawa yayi cikin ƙananan kaya, sannan ya ɗauko wata baƙar jacket mai hula ya sanya gami da rufe kanshi da hular, face mask baƙi ya sanya ma baki da hancin shi, sai sun glass daya ɗora ma idanun shi, Sam ba zaka taɓa shaida shi ba, in har ba kyakkyawan sani kayi mashi ba.

Cikin salon tafiyar shi ya taka zuwa bakin mirror, saida ya gama kalle kanshi tsaf, yaga ba ta inda ya kuskure wajen barin wata alama da zata sanya a gane shi, sannan ya ɗauki makullin motar tashi ya fice haɗi da jan trolly ɗin kayan shi.


Kai tsaye yabar cikin hotel ɗin, bayan ya maida masu da makullin ɗakin nasu.

(To Su Ya Ameen Ko Ina Kuma Aka Nufa?)

********************


Yanzu wata irin kunyar Sir, Salim nake ji, duk da dai nasan cewa bana jin komai game dashi, saidai kuma akwai nauyi tattare dani, yanzu dai bana da matsalar komai, har mun gama zana jarawar mu, da yake hutun semester ɗin ba mai tsawo bane, ya sanya ban koma gida ba, da taimakon kuɗin da Ammi ta bani, da kuma hidimar da Sir, Salim yake yi mani, ya sanya karatuna na sanya a gaba.

Yanzu dai na samu ummata tana da ƴar wayar hannu, itama saidai duk in zata kira ni, sai taje tabhau cen bisa wani dutsi sannan zamuyi waya, amman idan ni na kira ta bana samu.

Matsala ɗaya ke damuna, yawan text da nake samu daga Ma'un Sir Salim, tana man barazanar shiga gidan ta, saboda taji labarin cewa har aure an je nema kuma iyayena sun bada.

Har kirana takeyi a waya bana ɗagawa ne, text ɗinma in tayo mani saidai in goge kawai bayan na karanta, ban taɓa faɗa ma Sir Salim ba, kullum Ammin shi kan kirani ta haɗa ni da yaran shi mu gaisa, zuwa yanzu dai Ma'un ta koma gidan Sir, Salim ɗin, wannan ce ma ya sanya yake zuwa weak end, amman ba wani kwanciyar hankali ko jin daɗi, yaran ma duka suna hannun Ammin shi, har yanzu ba'a maida ma Ma'un su ba, to bata tsaya ta kula da kanta ba ma balle yaran?

Duk wannan abun dake faruwa bai sanya naji ko ɗar cikin zuciya ta ba, miji dai ne na samu kuma ba zan taɓa wasa wannan damar ta kufce mani ba, tinda banga amfanin zaman haka ba, bayan Allah ya riga ya kawo mani mai sona da ƙaunata da zuciya ɗaya.

Sir Salim irin mutanen nan ne masu shiga rai farat ɗaya, yana da yawan fara'a, gashi baya da girman kai duk da kasancewar shi mai abun hannun shi, sannan yana da kyauta, ga iya mu'amala da mutane, wannan ce ta sanya ko a cikin makarantar mutane da dama suke girmama ni, kasancewar ya zuwa yanzu kusan kowa ya fahimci alaƙar dake tsakani na dashi.

Dogo ne daidai misali, don zamu iya cewa yafi ya Ameen da kaɗan, yana da ƙira irin ta cikakkun maza, ba baƙi bane cen wuluk, hasken shi daidai misali, yana da haiba da dattako. Ya iya shiga kala kala, hakan ce ma ta sanya mata da yawa macewa a soyayyar shi, acikin makarantar baya da kula ƴan mata, kuma baya son wasa da karatu, dalili kenan daya sanya ya tsaya man kai da fata, wajen ganin ban samu wata matsala ba.


A wurina soyayya ba abu bace da akan iya samu farat ɗaya, saboda ƙakubalen rayuwa da nasha fuskanta, idan ma ba yanzu ɗin ba, ai ni soyayya wurin mutane uku zuwa huɗu na santa tin tasowa ta a rayuwa, ummata sai Ya Ameen, sai kuma Afnan da Hafsat, waɗannan mutanen komin yanda na kai da son in manta dasu a rayuwa ta, ba zan iya ba, saboda sun taka muhimmiyar rawa a rayuwa ta, ba kuma kaɗan ba.


Wannan ce ta sanya na Gaza manta Ya Ameen ɗin, sau da dama in muna tare da Sir Salim na kan yi imagining cewa da ace Ya Ameen ne ya zata kasance a rayuwa ta? Duk da shima Sir Salim ba baya ba a wajen komai, cikas ɗinshi ɗaya matar shi, shima kuma bana ɗaukar hakan a wata matsala tinda ba'a kanta zan zauna ba.


Ammi na gwada man tsantsar Soyayya, butsu-butsu tayo mani aike ta hannun yaron nata, kai hatta da Abban shi Sir Salim ɗin Alhaji Bawa Bala, wanda ba ɓoyayye bane a ƴan siyasar ƙasar nan, saida Ammin ta haɗa ni dashi a waya na gaida shi, na yaba da yanda yake amsa gaisuwar tawa, don ga dukkan alamu na samu karɓu wa a cikin wannan family ɗin.


*Ikon Allah kenan. Inda wani yake ƙi da yini, nan wani ke so da kwana*



Hankalin Bilal ya gaza kwanciya, masalan ma idan ya kira wayar Aminin nashi yaji ta a kashe, idan kuma ya tambayi Abie, ya kan ce mashi yana lafiya, basa tare, ko yace yana office ko yace ya fita cikin gari, ko yace ya baro shi a gida.

Ya san halin Aminin nashi sarai, ba ƙaramin ƙyalle bane, wannan duk ɓoye ɓoyen da yakeyi mashi ma, ta ita yuwuwa ya fahimci komai, wannan ce ta sanya shi shirya faɗa mashi gaskiya, to saidai ta ina? Ta yaya zai ganshi? Idan ma ya ganshi to ta ina zai fara yi mashi bayani?

Yana cike da kunya da nadamar amsar wannan amanar da ya gaza cikawa, hakan ce ta sanya shi shirya tafiya American domin yaje ya samu abokin nashi, domin a samu mafita.

Ko a cikin jirgi ma wasi-wasi yake ta faman yi,ji yake kaman ƙasa ta tsage ya shige , bai shirya amsar duk wata ɓaraka daka iya aukuwa a tsakanin shi da Aminin nashi ba, a karon farko tin tasowar su daga ƙuruciya.


**********************

Hajiya Kubra likafa taci gaba, yanzu akai akai tana zuwa cen ƙasar ta Turkiyya wajen Alhaji nata, ganin basu kuma tada mata maganar ba, ya sanya hankalin ta ya kwanta, bata da matsalar komai, yanzu komai nata sai ƙara bunƙasa yakeyi, ta zama hajiyar da duk faɗin ƙasar ake labarin ta, mafi yawan mata suna ji ace dama sune ita, yawan ma'aikatun ta, da kuma hannun jarin da take dashi a kamfanoni ya sanya kullum shaharar ta ƙara haɓaka takeyi, Alhaji Mustapha ba mutum bane mai damuwa sosai ba, balle yanzu da baya da ko yaro ɗaya gaban shi idan ka ɗauke Afnan da take hannun yayar ta, shi kuma Abie yana wurin Yayanshi acen ƙasar ta amurka.

Wannan ce ta sanya ya maida Al'amurran shi kacokam kam ƴan uwan nashi dake Katsina dama sauran garuruwa, sosai ƙasar ta Nigeria ke amfana da Alhaji Mustapha ɗin dama iyalan shi baki ɗaya. Su kaka zuwaira suna cikin jin daɗi ita da ɗan tsohon mijin ta isuhu, sai dangi da kusan duk ya sanar ma waɗanda suka gama karatu aikin yi, waɗanda kuma basu ƙarasa ba yana taimakawa wajen karatun nasu.

Hakan ce ta sanya hankalin shi bai kai kan kwana biyu da yaron nashi bai kira shi ba suka gaisa, Abie ne ke kiran shi, to shi ɗinma dai kaman yanda yake faɗa ma Bilal ɗin shima haka yake faɗa ma dad ɗin nashi, hakan ce ta sanya bai kawo ma ranshi komai ba, illa iyaka dai ya haƙura da Suhan ɗinne kaman yanda Mom ɗinshi ta buƙata, tinda shima babu irin binciken da baiyi ba, da kuma sanyawa ayi, Amman Allah bai sa an dace ba.


***************


A mota yake tafiya zuwa wasu garuruwan, photon ta dake cikin wayar shi ya sanya aka wanke mashi, matsalar dai da babu wanda take ita kaɗai saidai wanda suke tare dashi, to akan ce mashi dai ita yarinyar ba'a santa ba, amman mafi yawa sukan ce mashi ai wannan shine Yariman Matasa Arewan da akayi ma naɗi watannin baya, ya kan sha mamaki, ashe haka mafi yawan mutane suka sanshi a faɗin ƙasar tashi? Lallai tafiya mabuɗin ilimi ce, a wannan tafiyar da yayi, ya haɗu da ƙauyukan da suke matuƙar buƙatar tallafi koda kuwa ace na ruwa ne kawai, sannan ya ƙudurta a ranshi cewa zai iya bakin ƙoƙarinshi wajen ganin ya taimaka masu, muddin ya koma normal *Al'ameen Almustapha Dambulan* ɗin da yake ada.

Idan KagaYa Ameen a yanzu ba lallai ne ka shaida shi ba, shi mutum ne mai yawan tohon gashi, muddin yayi cikakken sati baiyi aski ba, to baya kalluwa, wannan ce ta sanya yanzu da yake ta faman yawon neman su, bai ko damu da yayi askin ba, indai ya samu yayi wanka ya cenza kaya, salla kuwa daman ƙasaru yakeyi, gashi sosai ya firfito mashi kaman ba shi ba, duk ya yamutse ko abinci bai damu da ya zauna zaman ci ba.

Saidai wannan haiba da kwarjini da yake dasu tin tale-tale tana nan daram babu inda taje, kome yakeyi cikin halin nan nashi da kuka sani yakeyi, hatta da tafiyar shi idan ka tsaya ka kula tsaf bata cenza ba, kuma abar kallo ce, wani lokaci a cikin motar shi yake kwana idan dare ya rutsa dashi inda babu hotel.


Ya gaji matuƙa yana so ya kwanta ya huta, yana so yayi aski, yana son aiwatar da abubuwa da dama.

Hakan ce ta sanya shi neman hotel ya kama ɗaki, tunani yake so yayi, yana so yayi tunanin ta ina zai ɓullo ma wannan yawon gararin neman nasu.


Da daddare ne bayan ya gama cin abinci yayi wanka haɗi dayin sallar shi, gado ya nema ya kwanta, duk ya zura saboda irin wannan wahalar da ba sabawa yayi da ita ba, ko zaman tuƙin ma kanshi aiki ne.

Kaman an kunna mashi redio, haka yaji labarin da hafsat ta bashi yana ta faman dawo mashi tiryan tiryan cikin ƙwaƙwalwar, idan har bai manta ba, yaji tana cewa ranar daren da zata tafi makaranta suka bar gidan, kuma idan ba wai ya manta bane, an riga an gama kammala mata komai, to kenan idan har hasashen shi zai bashi daidai, yanzu Suhan ɗin tana makarantar ta ABU zariya, muddin Umman tata ta yarda da karatun nata, to kuwa tabbas zata kasance a makarantar a daidai wannan lokacin, shine ya rubuta mata course ɗinda ya dace tayi da hannuwan shi, kuma yaji Bilal ɗin yana cewa basu cenza mata shi ba, zumbur yayi ya tashi, haɗi da ɗaukar makullin motar shi, ya ja jikkar shi ya fice, a cikin daren ya sake maida masu makullin ɗakin nasu, ya kama hanyar zariya, duk da irin halin rashin tsaro da ake fama dashi a ƙasa, duk da irin duhun daya mamaye duniya a daidai wannan lokacin, duk da irin hatsarin da yaka iya haɗuwa dashi a tafiyar shi ta wannan daren.


Wannan ba shine matsalar shi ba, wannan ba shine abunda yake ji ba, Suhan ita kaɗai ce damuwar shi, ya sanya ta a idanun shi, ya ganta koda sau ɗaya ne, ta amince mashi, koda ba zata koma gidan su bane, ta amince ta aure shi a hakanan idan hakan ta faru ya cika burin shi kaso 80 a yanzu na rayuwar shi.


Ƙarfe bakwai na safen ranar talata a cikin makarantar tayi mashi, akan idanun shi jefi jefin ɗalibai suka fara fitowa zuwa cikin makarantar, sannu kan hankali har suka yawaita, kowa na hidimar shi, zuciyar shi ce ta tsananta duka, tabbas tabbas idan har abunda yake ji a jikin shi haka ne. To *Suhan ɗinshi tana cikin makarantar a daidai wannan lokaci*



_Hmmmmmmmmmm_





~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._


*YAN UWA MUNA KARA KIRA DA MABIYA LITTAFAN GOLDEN PEN WRITTERS ASSOCIATION DA SU KIYAYE DA WANNAN MAI CUTAR TASU DA SUNAN YANA SAIDA LITTAFAN KUNGIYARMU,TO KARYA

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login