Showing 111001 words to 114000 words out of 247770 words

Chapter 38 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10424

suka zo suka ƙare muka cinye.

Ganin hakan ne, kullum ummata cikin tunani cikin damuwa, don watarana idan malam ɗin baiyi sa'ar kasuwa ba, mu kan kwana bamu zuba ma bakin salatin mu wani abu ba, saidai ruwan da tin inasha ina amai, a haka har na daure ma rayuwa ta.


Wannan ce ta sanya ni cema umman tawa ko zamu fiddo kayan provision ɗina na makaranta, saidai ta gane ni, a cewarta in yau aka zo aka ce in fito da me zamu siya?

To dole nima dai na haƙura, saidai fa inayi masu ɗauki ɗai-ɗai, duk da umman tawa tana kallo na, amman ta kan Gaza ceman uffan, saboda wani irin tausayi na da ya kan ratsa ta, har kwalla take yi a kai-kaice bataso in gani, saidai fa nima ɗin wani lokaci idan abun yayi yawa ya isheni nakan shige banɗaki inyi kuka mai isa ta, in wanke fuska ta in fito don kada umman tawa ta lura, amman fa ance yaro yaro ne, koda kuwa ɗan giwa ne, tana lura tsaf dani, saidai bata tankawa, saboda tasan komai mai wucewa ne.

Sana'ar wankuu ta fara yi, ta kan je bakin rafi ta wanko ta dawo gida ta shanya akan danni. To saboda ƙauyen ba wani babba bane ba, bata cika samun wankin ba, bayan haka da wani ya bada wankin gara ta auno shinkafa ƴar hausa ya watsa wake ko dawa a ciki an dafa ansha shagali.

Hakan ce ta sanya ta haɗawa da surfau, a ranar da ta fara surfau ɗin kuwa, ba irin kukan da ban sha ba, abun ka ga fara, fuska ta tayi suntum kuwa, tayi jajur, kaman ka taɓa jini ya ɓalle, tausayin ummata nake ji da irin rayuwar da muke ciki, tabbas idan guri na ya cika babu abunda zai hanani gina ma ummata gida a Abuja in ɗauke ta, muje cen muji daɗin duniya, saboda irin wahalar da muka sha a rayuwa.


Da wannan ɗan aikin da ummata take yi, nakan taya ta kullum, wani lokacin harda hajjo ɗin, saboda ƙauyen ana bala'n sarrafa dawa da gero da masara, kusan ma ince sune abincin nasu, wasu ma ko surfawa ba'a yi, a haka ake cinta datsa, wai tafi auki. To da wannan ƴar sana'ar ce muke samu mu ɗora tukunya kafin fa malam ɗin ya dawo.

Malam yana matuƙar sona, yana ji dani kaman shi ya haifeni, haka tsakanin shi da ummata sai girmamawa da mutuntawa, ya ɗaukemu kaman wasu jinin shi, duk da na kula babu abunda ya haɗa shi da umman tawa ta fannin ƴan uwantaka.

Sai ince mun samu so da ƙauna, da tattashi a inda basu dashi, basu da abun bamu, ko don saboda suma ɗin talakawa ne kaman mu? Oho...


Nima saboda haka na fara yin ɗan kitso haka, ana bani naira ashirin ko shabiyar idan yara nayi mawa, manya kuma har talatin, ko a bani sabulu ko omon wanki, ko kuka ko kuɓewa, to dai mun gode, mun i-iya dasu tinda abun kuɗi ne, muma sai mun siya. Tini kayaaa suka fara dafewa, saboda tsabar rashin kyaun ruwan wankin da sabulu, dama wuta kuwa tinda muka je ƙauyen ban ganta ba, da idanuna kuwa.

Haka muke ta ƙundunbala, rayuwa fa babu daɗi, matsatsin yayi mana yawa, a ƙauyen kowa da Hauwa yake kira na, saboda dashi Malam da Hajjo ke kirana, ita kuwa umma saidai tace man Mamana.

Da ummata hanani fita take yi, duk da bansan dalili ba, saidai nafi alaƙanta hakan da wancen zaman da ummata tayi, a lokacin da akace an haifeni, gudun tsogunguma irin na karkara ya sanya suka shawarta hakan da malam.


Saidai fa ban tsira ba, duk lokacin da na fita, haka zaka ga an hau danni ko ƴar katangar ƙasa, ana nuna ni da baki ana gulma ta, da zunɗena, har saida na samu ummata da maganar, ita kuma ta shawarce ni da kar indamu, dama dole hakan ce zata faru, saidai hakan ba wani abun damuwa bane, idan nayi la'akari da yanda aka yi aka haifeni har zuwa barin Umman tawa ƙauyen, da kuma dawowar ta katsahan..


Ta ƙara sanya ni cikin tunani mai zurfi, saidai banga fuskar tambayar warwara ba, nayi imani dai cewa ko badaɗe ko bajima dole ne komai zai fasu, dole akwai ranar ƙin dillanci, ranar da dukkanin ɓoyon da umman tawa take yi mani komai zai bayyana kanshi da kanshi...


Muna cikin wannan halin ne, wata ranar talata da sassafe, sai ga wani yaro "wai ana sallama da Suhan" tinda naji hakan gabana ya faɗi, don dai a duk faɗin ƙauyen ba kowa ne ya san da wannan sunan nawa ba.


Tin kafin in leƙa tsakar gidan, ummata da take zaune tana iza wutar ruwan kunu, tin jiya taci sa'a aka samo mata niƙan dawar da geron, da yake idan an haɗa su sunfi auki, ba ta daɗi ake ba tukun, niƙan ma da sai afi sati ba'a samo man da za'a tayar da injin ɗin ba, duk kuma ranar da aka samo, tofa ana kai wani lokaci ana niƙan saboda layi.


"Inji waye?" Ummata ta jefa ma yaron tambaya gami da tsattsare shi da idanu, domin jin amsa.


"Oho nima ban sanshi ba, wani ɗan gayu ne dai da mota, yana ƙofar gida"

Yaron ya faɗa kai tsaye, batare da ya tauna maganar ba, ko ya kula da *Yo* ɗin da yace hakan ba tarbiyya bace ba.

"Jeka abin ka" ta faɗa, tana mai zarar hijabin ta da take bisa igiya. Nidai ina tsaye bakin ƙofar ɗaki sai faman raba idanuwa nakeyi, hankalina fa duk ya tashi kar ace Bilal ne ko Ya Ameen suka gano inda muke.

Tsaye ta tadda shi jikin mota, ganin babbar mace da yayi ya sanya shi saurin isa ta inda take tahowa ya durƙusa har ƙasa yana mai cewa "Ina kwana?"

Cikin ƴar sarkin fuska jin daɗin ladabin da yayi mata, da kuma ƴar natsuwa data hanga tattare dashi ya sanya tace "Lafiya lau, wa kake nema ne?"


"Tace mani Sunan ta Suhan" ya faɗa yana mai miƙewa tsaye, saidai har yanzu kanshi a duƙe yake ƙasa, ƙare mashi kallo tayi tsaf, ba manyan kaya ne ba jikin shi, hasalima ƙananan kaya ne, daidai da gani yana cikin hutu, kayan shi ma sun nuna da yanayin shi, da kuma motar da yazo a cikin ta.

Gabanta ne ya tsananta faɗuwa, tana tsoron masu kuɗi, tana gudun su, wasu kuɗin bala'i ne, wasu kuɗin masifa ne, masu kuɗin na zuwa wuta ne, lallai koma minene dole ta daƙile alaƙar nan da take shirin faruwa da ɗiyar ta.

"Yaro Suhan ƴa ta ce, saidai kuma gashi ni ban waye ka ba" ta faɗa cikin manyance da dattako irin nata.

Gaskiya yaji daɗi, ko haka aka tsaya ya fahimci tabbas yarinya ce mai gata da galihu, yarinya ce mai natsuwa, ko a sadda ya ganta wancen karon ya kula da haka, saidai ƴan matan na yanzu ba tuƙwane bane balle a kwankwasa su aji.

"Eah mama, wato nayi mata alƙawarin cewa duk sanda aka koma makaranta zanzo in faɗa mata, gashi anyi sati da komawa wani uziri ya riƙeni, ni malami ne a makarantar da take, na kula ita sabuwar zuwa makarantar ce, shiyasa gashi kuma ga dukkan alama batasan kowa ba, ko hanya ma bata sani ba, shine nazo in faɗa mata, in ba damuwa ku bani izini in tafi da ita, gudun faruwar wani abu a hanya ko kuma a cen makarantar, nayi alƙawalin cewa da izinin Allah babu abunda zai faru, Amman fa in kun amince"

Tinda ya fara magana bata katse shi ba, har ya kai aya, sannan ta jinjina kai, tana mai gyara tsayuwar ta, bayan ta ƙara nazarin shi.


Ba ƙarya ko alamar rashin gaskiya a tattare dashi, duk da yanzu mugu baya da kama a fuska.


"Tabbas ta faɗa mani hakan, kuma lallai batasan makarantar ba sosai daga nan, to saidai bana jin zan iya barin ta ta bika, alhalin kadai san ba muharramar ka bace, sannan ba sanin daga ina kake mukayi ba, kuma bamu da tabbacin kai ɗin malamin ne, saboda haka kayi haƙuri don Allah, mun gode da Alkhairin ka a gare mu baki ɗaya. Ka gaida gida"

Tana gama faɗar haka ta juya zata shige gida, shima ganin hakan ne ya sanya shi saurin shan gabanta yana faɗin


"Mama don Allah kiyi haƙuri, wallahi hanyar bata da kyau, naji idan ba zaku iya barin ta ita kaɗai ta bini ba, a haɗa ni da wani sai ya raka mu, alabasshi shi sai in sanya shi mota ya dawo nayi alƙawari"

Dakatawa tayi ga barin shiga gidan da take da niyyar yi, sai kuma ta juyo ta fuskance shi

"Kasan girman alƙawari kuwa?"

Ta jefa mashi tambaya, gyaɗa mata kai ya shiga yi, ba tare da ya iya furta komai ba, zuciyar shi nata faman duka, sai kai komo take yi. Ko ba komai ya ƙagara a barta ta fito ko ya samu sa'ida, akan tunanin da yake wuni da kwana nata.

" To shikenan tinda kace haka, Suhan zata fito yanzu ku tafi, na baka amana, kai da Allah kuma idan kaci, sannan inaso ka shige mata gaba wurin samun transfer da take so tayi, zuwa wata makarantar, ina so kayi mani wannan alfarmar"

Gabanshi ne ya tsananta duka, shi yaushe ne zai iya barin ta ta samu transfer, yana kallon ya dace ya samu daidai inda yake so, burin shi ya cika, yaushe yana kallon ruwa kwaɗo zai yi mashi ƙafa?


"Mama banyi katsalandan ba, ki gafarce ni, amman ba abune mai yuwuwa ba, duk kuwa da nake malami a jami'ar, saidai idan zaki iya faɗa mani dalilin ko damuwar, nayi maki alƙawarin zan san yadda aka yi aka kauce ma faruwar al'amarin"

Ya faɗa cike da zullumin ko zata yarda da hakan.

Saidai ga mamakin shi yaji ta fara cewa.

"Eah, duk da bansan dalilina na yarda da kai ba, inaso ne ta samu canjin makaranta saboda bana so kowa ya gane tana makarantar, kuma koda wani zai zo ya binciki inda take, ba zai samu bayanin komai ba"


Ɗan murmushi ya saki, duk da kanshi ya ƙulle sosai, to ta yaya za'ayi ace wani yaje neman yarinyar da take wannan surƙuƙin, ta yaya ma aka yi ya santa? Kenan akwai wani bayan shi? Lallai dole duk yanda za'ayi ya ture gwamnatin wancen ya kafa tashi, kai inaaaa, ai bama zai yuwu ya cire yarinyar a rayuwar shi bb,tayi mashi, kuma ya san irin zaɓin Ammin shi ce.

"Insha Allahu umma, ai bama bada wani imformation ga wani na waje a cikin makarantar, akwai tsaro sosai, kuma nayi alƙawarin yin iyakar iyawata ta a kauce ma hakan, ita kuma ta samu Abunda taje nema insha Allah"

Jinjina kai ta kuma yi tana mai cewa "Mungode kwarai, ina jaddada amana a hannun ka, marainiya ce, idan kaci amanar ta Allah ba zai barka ba kaima"

Baisan lokacin da ya haɗe hannayen shi ba don daɗi, ai tini ya fara zuba godiya, duk son ya kauce ma fiddo farin cikin shi a fili, saboda wani zargin gazawa yayi. Itama ta ɓangaren umma ta tinanin hakan ta juya ta shige gidan, zuciyar ta na ta saƙa mata wannan farin cikin da ta gani akan fuskar shi na menene? Kauda mugun tinani tayi, tare da maye shi da na alkhairi, ta cigaba da addu'a har zuwa shigar ta gidan.

A bakin ƙofar ɗaki dai ta tadda ni tsaye, sai zaro idanu nakeyi,


"Jeki shirya ki fiddo kayan makarantar ki, malamin ku ne"

Ta faɗa tana mai wucewa kai tsaye wurin tukunyar ta, da ta riga ta ta fashe tuni.

Cikin murna da ɗoki na juya zuwa cikin ɗakin, ai ko ba komai ma, na ɗaga ma wannan ƙauyen da ya zame mani ƙarfen ƙafa, ba ruwa ba wuta, ba abinci mai daɗi, ba wurin kwanciya mai daɗi.

A haka na shirya tsaf, na fidda kayan tsakar gida, ko ruwan kokon ban tsaya sha ba, saboda zumuɗin makaranta. A haka ummata ta har haɗa dubu uku da take ta maƙalo maƙalo da ita, gudun faruwar hakan, miƙo mani tayi gami da yi mani addu'a. Har tsakar gida ta biyo ni tana mai jaman kunne gani da cewa in kula.

Hajjo da malam ma da bai tafi kasuwa ba, suma sun man ihisann su, na kuma ji daɗin shi, suma har waje suka raka ni, suna mai tayani ɗaukar kayana.

Yana ganin fitowar mu, ya zabura ya buɗe mana but muka saka kayan ya kulle, ya zagaya ya buɗe man gidan gaba, na shiga gami da maida ƙofar ya kulle, shima zagayawa yayi ya shiga bayan ya gaishe da malam ɗin.

A haka motar tayi ribos, ina ɗaga ma ummata hannu da take ta faman share kwalla da bayan hannuwan ta, nima ai sai naji kwallr ta cika mani idanuwa har bansan ta fara zuba akan fuskata ba. Har motar ta ɓace ma ganin su Umman sannan suka juya zuwa gida, yayin da ni kuma na sauke hannun ina mai sake rushewa da kukan da nagaza gane ko na menene, shin na rabuwa da ummata ne? Ko na murnar cikar buri na? Ko na halin da na bar umman tawa a ciki ne? Ko kuma mikin su Ya Ameen ne ya taso mani.


(Hummm Suhan kenan)



*******************

Cikin kwana biyun kuwa da aka ɗibar mashi jikin yayi sauƙi, haka aka lallaɓa dashi aka koma gida, duk da yanzu babu abunda ke damun shi, sai rashin ƙarfin jiki.

Tin da Alhaji Mustapha yaga haka, yace zaman da su Nihal ɗin suke yi ya isa hakanan, su wuce kowacce ta koma ɗakin ta, haka duk ya tarkata su ya fafutuka su gida, ya rage daga shi sai Bilal da Abie sai Hajiya Kubra.

Zaman hakan baya mashi daɗi, ya rasa dalilin da yasa tinanin Nigeria ɗin yayi mashi yawa, kuma kullum idan ya tambaya sai ace mashi lafiya lau, idan ya tambayi su Suhan kuma ace mashi tana makaranta, wai me ke faruwa ne?

Wayar shi da number ɗin ta ke ciki kuma ta fashe kwatsa kwatsa bata ma moruwa, tin ranar da abun ya faru, gashi baiyi saving a mail ba, balle ya nemo.

A haka ya tada balli cewa, shifa zai tafi nigeria yaga ya abubuwa suke ciki, hankalin su fa ya matuƙar tashi, Alhajin ne yayi dubarar hanashi, yace Bilal ɗin yazo ya tafi ya gano komai, amman shi da barin ƙasar kuma sai yanda hali ya nuna.

Hikimar Alhajin nayin hakan kuwa shine, don Bilal ɗin yaje ya nemi su Suhan ɗin kafin komawar su ƙasar.

To shima dai Bilal ɗin ya gane hakan, wannan ce ta sanya shi tarkatawa ya koma Nigeria ɗin, wanda tare da Hajiya Kubran suka tafi, saboda ta koma ma harkokinta tinda yanzu jikin yayi sauƙi, ba abunda ke damun shi illa su shegiyar yarinyar nan, to indai don wannan ne ba kuwa zai taɓa warkewa ba, saboda yanda suka sanya ƙafa suka tafi, sun tafi ɗin kenan fa.

Bilal ya sha wahala sosai, duk inda ya san zai je yaje nema, har makarantar yaje lokacin da aka koma yajin aikin, Amman bai samu gamsasshen bayani ba, cewa sukayi har yanzu bata dawo ba, koma suce su basu sake ganin ta ba, da haka ya koma gida, tabbas ya shiga tashin hankali ba ƙarami ba, shi bama ta son da yake ma Suhan ɗin yake yi ba yanzu, ta rayuwar aminin nashi daya kula cewa lallai za'a sha darga idan ya gane cewa ta ɓata, bama asan inda za'a ganta ba, gashi kullum ya gwada layin nata akan ce mashi switche up, baya gajiyawa kullum sai ya kira ta kai sau goma.

A haka ummin shi ke sanya shi gaba da ban baki, da ban haƙuri da kwantar da murya akan al'amarin, shi bai ma san ta yaya zai ɓullo ma al'amarin ba, ko kusan alama, bai taɓa tunanin idan zai iya shiga wannan irin halin ba a rayuwa.

Ko aiki ya dena zuwa, gashi Al'ameen ya matsa akan yaje makarantar su Suhan ɗin ya bata suyi magana, ko ya haɗa shi da umma, idan ita Suhan ɗin tayi nisa.

A haka abubuwa suka taɓarɓare, ba ga aikin kamfanonin nigeria ɗin ba, ba kuma ga na cen american ba, tinda tini shi Alhaji Mustapha ya koma cen ƙasar da yake aiki, ya bar shi daga shi sai Abie.

Ƙarfe goma na safiyar litinin, Bilal ne zaune bisa kujera mai cin mutum ɗaya, ya zabga uban tagumi, ga stool ajiye gabanshi cike da kayan breakfast, so take yaci ko ya samu ya leƙa wurin aiki yau, rabon shi da zuwa office ita har ba zata iya tunawa ba, komai daga gida yake yi, ko kuma yace aje a samu mataimakin shi Peter, itama ummin zaune take gefe ta zuba mashi idanu, tabbas mijin nata yana cikin damuwa, to saidai ya zata yi dashi? Babu wani taimako da zata iya bashi a halin da ake ciki yanzu.

Kaman ance ya latso number ɗin Suhan ɗin, aikuwa sai ta fara ringin, firgigit

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login