Showing 39001 words to 42000 words out of 247770 words
Laila cikin sauri
"Gaskiya ne Hajiya ta, ai wannan maganar ba ta waya bace, anya ma kuwa ba asiri sukayi mashi ba? Kin san fa tin lokacin da kika kula da shisshige masun da yake yi ya kamata ace kin taka ma abun burki, Amman son da kike mashi ya hana"
"Hajiya Laila wallahi nayi ƙoƙarin hakan tin lokacin, Amman ɗan banzan yaron nan yaƙi bani haɗin kai, kin dai sanshi da shegen zurfi ciki, da kuma miskilanci, ni kaina rasa gane kanshi nake yi"
Hajiya Laila ce ta tari numfashin hajiya kubran da cewa, "ba kince su keyi maku girki ba?". "Eh kwarai kuwa hajiya, in ba girkin su ba baya cin na kowa wlh" humm, Hajiya laila ta numfasa gami da sakin wani ɗan guntun murmushi ta cen ɓangaren, sannan ta ɗora da faɗin
"To wallahi ina mai tabbatar maki a nan suka samu, suka samu abin da suka barbaɗa mashi yaci, yanzu abin da nake so dake ki kwantar da hankalin ki, abun zai zo mana da sauƙi, kedai kiyi ƙoƙarin dawowa akan lokaci"
Nisawa Hajiya Kubra tayi cikin ƙunar zuciya da tsanani ɓacin rai, kaman zata haɗiyi zuciya ta mutu, sannan ta cigaba da cewa
"Shikenan Hajiya Laila, ina so please kiyi tinanin neman mafita, saboda ni duka ma kaina ya ƙulle wallahi, gabaki ɗaya yaron nan so yake ya birki ta mani lissafi, na yarda dake ne, insha Allahu kuma zanyi ƙoƙarin ganin na dawo akan lokaci, yanzu ma zuwan maneman su suhan ne kawai zai tsaida ni"
"Is OK Hajiya Kubra, baki da damuwa ki kwantas da hankalin ki, ina mai tabbatar maki da maganar nan zata sha ruwa, ko shi Alhajin da ya goya mashi baya, ba zai ma ƙara tada maganar ba, balle wani Alhaji Auwalu cen, da zaki ɗaga hankalin ki aka shi;To ko Isuhun ma bai isa ba balle ƴaƴanshi"😒
Hajiya Kubran ce ta murmusa mai cike da yaƙe, "Humm Hajiya Laila kenan, baki da dama, haka nake so, Shiyasa nake son ki nafi yadda dake akan kowa cikin ƙawaye na, na mayar dake aminiyata ta hannun dama ta, wuƙa da nama na hannun ki, a fara komai kafin in dawo, zan tura maki duk abin da za'a buƙata"
"Ba damuwa Hajiya Laila, ke dai sai kin dawo dai, ƙibar komai a hannuna, sai mun yi magana"
"OK shikenan a huta lafiya Hajiya Laila, sai Naji daga gare ki" ta faɗa tana mai datse kiran gami da zama cikin ɗan samun sassauci, saboda sanin halin hatsabibancin ƙawar tata, komai take so mai sauƙi samu ne, indai tabi ta hannun amini yar tata.
**************
"Look Friend kayi gaggawar yanke hukunci, aure ba abu bane da akeyi mashi hawan ƙawara, yarinya r zaka iya taimako ta, ba sai ka aure ta ba, ina so ka sani aure babu soyayya ba abu ne da ke ɗorewa ba, masalan yanda zaka yi manage na zama da ita, a yanda na san ka yarinyar bata yi daidai da ra'ayin ka ba, beside ma mahaifiyar ka...... "
Dakatar dashi Al'ameen ɗin yayi, ta hanyar ɗaga mashi hannu," Bilal! Please mubar maganar haka, kayi man addu'a kawai" abin da ya faɗa kenan, ya miƙe a hankali ya zura kayanshi, gami da zarar keys ɗinshi na mota ya fice daga gidan ma baki ɗaya.
Da kallo abokin nashi ya bishi dashi, "Hooo Al'ameen kenan, ko sai yaushe zai cenza? Kaman bashi bane yanzu yake neman way out, yaro kaman mai bira'izai? Wannan ko auren yayi wahalar da yarinyar kawai zai yi, bai iya wata soyayya ba, balle ya tsaya bata kulawar da ta dace, kullum kai kenan a murɗe? A baibai? Humm" ya faɗa a fili yana mai miƙewa shima ya fice daga ɗakin zuwa cikin lambu.
***********
Da sallama ya shiga sashen nasu, fuskar shi a matuƙar ɗaure, ko babu komai ya san bata kyauta mashi ba, a gaban kowa ciki har da iyayen shi ma, Amman taso tayi jayayya dashi, har tana ɗaga murya akan kowa da ficewa ma baki ɗaya daga perlour ɗin, dole ya nuna mata ɓacin ran shi, alwashi ne ya sha shi aure sai anyi, zai ga wanda yake gaba, cikin shi da ita; ko ɓangaren da take bai kalla ba, ya wuce kai tsaye zuwa bedroom ɗinshi domin wanka da shirya ma zuwa sallar magariba da ta gabato.
Haka yazo ya sake wuce ta, tana zaune tana kumburin ta da kaɗa ƙafa ɗaya dake kan ɗayar, Hajiya Kubra kenan, ai shi duk abin da Allah ya tsara baki da kuɗin da zaki cenza ikon shi akan komai
Itama tana kallon shi, Amman yanzu kam duk son da take ma Alhajin, zata danne shi ne, ba zata taɓa bari da girman ta, da ajinta ba, ta tozarta, to ai ajinta ma ya zube in har ta bari ƙawayenta suka ga wadda ɗanɗan nata yake son auro mata a matsayin suruka, yarinyar ƴar ƙauye da babu abin da ta iya sai bauta, sam Suhan ɗin ba ajin *Moh'd Al'ameen Al-Mustapha Dambulan* ɗin nata bace.
Wannan ce tasa har ya kuma fitowa ya fice baki ɗaya daga gidan bata kula shi ba, tasha Alwashin yi ma abun tufkar hanci, ba Alhajin ne yake taƙama dashi ba? To wannan karon har shi ba zata ƙyale shi ba.
-----------
Haka kuwa aka yi, washe gari da wuri maneman auren su Nihal ɗin suka iso, masha Allah yara ne ƴan gayu, ƴaƴan masu faɗa aji, kaman yanda hafsat ɗin take kamila da sanyin hali haka shima saurayi nata yake, kowa yayi mamakin shi duk da, da alama naira ta jiƙa shi sosai, Amman baya da jin kai irin na sauran masalan saurayi Nihal ɗin, ahaf, ai kowa yana samun daidai dashi ne, basu jima ba sosai bayan sun gabatar da kansu, iyayen na su saudat suka ga, ai iyayen nasu ba baƙi ma bane a wajen su, umurtar su sukayi da su turo su domin tsaida lokacin aure,
Abun Alkhairi sosai suka ba yaran su Goggo Aisha, sukayi ta Sam barka da sanya alkhairi, basu tafi ba sai da Kaka zuwaira ta zo ta zazzaulaye su, cikin wasa irin na kaka da jika, hakan ya ƙara faranta ran su, domin su ɗin dama sangartattun ƴan gata ne, sun saba zaulayar granny ɗinsu at any moment.
Atare suka koma zuwa Abuja gabaki ɗaya, bayan kammala zumuncin irin na wannan lokacin, da yazo da saɓani da abubuwan farin ciki da dama.
Ta ɓangaren Hajiya Kubran kuwa, har yanzu sama sama suke da Alhajin, domin ya sha Alwashin gargaɗar ta da kuma yi mashi katsalandan acikin Al'amari auren yaron nashi.
Kowa da Abunda yake saƙawa cikin zuciyar shi har ƙarasowar su zuwa cikin gidan, wannan ce ta sanya bamu san da labarin dawowar tasu ba, kowa part ɗinshi ya wuce kai tsaye, duk da suna farin cikin gabatar da masoya nasu ga iyayen su, Amman ta ɓangaren guda, ƙudirin yayan nasu ya kasa barin zuciyar su, haƙiƙa wannan labari ne mai muni, labari ne mafi ƙona zuciya da suka taɓa ji tin bayan mallakar hankalin kansu.
Al'ameen kuwa, Daurewa kawai yake yi wajen amsa ma abokin nashi duk maganar da yayi mashi, ziyara ya kawo mashi, baya so yaga kaman yana wulaƙanta shi ne, ta ɓangaren Bilal ɗin kuwa yayi mashi uziri, ya san damuwar abokin nashi, ya sani sarai, ya yanke hukunci ne cikin fushi, gashi abun yazo daga baya yana damun shi, kuma shi ba irin mutanen da suke amai su lashe bane, ya sani, koda za'a dinga yankar naman jikin shi, ba zai koma yace ya fasa ba, ba zai warware nuƙatar tashi ta auren Suhan ɗin wajen iyayen shi ba,koda kuwa hakan na nufin faruwar mummuna abu ne a gareshi.
*****
Tura ƙofar aka yi, gami da shiga cikin ɗaki kai tsaye, wucewa tayi i zuwa ga bakin gadon ta samu ta zauna, sanye take cikin kayan bacci irin masu mugun tashin nan, sai walƙiya take, Hajiya kubra kenan, ikon Allah,
"Alhaji nazo ne muyi magana da kai"
Shiru yayi mata kaman ma baya cikin ɗakin
Bata saurare shi ba, ta cigaba da faɗar Abunda ke cikin zuciyar ta.
"Alhaji ina so ne fa ka sani, ina nan kan baka na, lamarin auren Al'ameen da yarinyar cen ta sashen masu aiki, ban yarda dashi ba har yanzu, bana kuma tinanin zan yarda har abada, ni ce na haife shi, baya da ikon yin abun da ban yarda mashi yayi ba, mu ne gaba dashi, ba shine gaba damu ba, mune muka haife shi, ba shine ya haife mu ba, ina so ka sani muddin ya sake ya auri yarinyar nan, zan mugun saɓa mashi, bana so ka bashi goyon bayan auren baiwar mu..... "
" Ya isa Kubra, ya isa hakanan nace"
ya katse ta cikin tsanani ɓacin rai, da tsawar da ta gigita ta, har ta miƙe tsaye bata sani ba, to ita ai bata ma san lokacin da ya miƙe zaune ba.
"Idan baki son in saɓa maki ƙibar maganar nan, ina so ki sani muddin baki bashi damar auren yarinyar ba, to fa lallai ne ki bashi dama ya zaɓi wadda tayi mashi, namiji ne, mata ma bamuyi masu dole ba balle maza, namijin ma kaman Moh'd Al'ameen, Kubra me yasa baki tinani ne wai in zakiyi abu?kin gama tozarta ni gaban ƴan uwan nawa da ƴaƴan nawa, shine kika biyo ni nan ki sake ƙarawa? Yaushe har abun naki ya kai haka ban sani ba? Toh ina so ki sani, duk hukunci da na yanke nan gidan akan ƴa] a na ya yanku, ni ne sama dake acikin gidan nan, kuma dole kema kibi abin da nake so, ina so ki sani, maganar sake yin aikin Maryama da yarinyar ta acikin gidan nan na haramta shi, kaman yanda na faɗa maki acen baya, ban barsu sunyi aiki ba, ada cen saboda lafiya su, balle yanzu da suka zama *Surukkai na"*
A razane ta kalle shi, "Alhaji Surukkai fa kace? Yaushe har suka zama surukkan ka?"
"Ah to nadau faɗa maki, kuma abin da nace kenan, na gama magana, zaki iya cigaba da faɗar dukkan Abunda ke ran ki, ruwan ki ne ki ƙyale yaro yayi Abunda yaga ya fiye mashi, ko kuma ki sanya ya fara bijire ma umarnin ki, da biyayyar da yake maki" yana gama faɗar haka ya koma ya kwanta, gami da jan bargo ya lulluɓe jikin shi, sannan ya sanya hannu ya kashe dumlight ɗin ma gaba ɗaya, ɗakin ya gauraye da duhu.
Ƙutawa tayi, gami da tashi ta fice daga ɗakin zuwa nata, tana mai ƙudurce abubuwa da dama acikin ranta.
*********
"Son" Alhajin ya kira sunan yaron nashi da yake zaune bisa kujera mai cin mutum ɗaya, hakan ce ta sanya shi ɗago kyawawan udanun nashi ya ɗora su akan dad ɗin nashi, shigowa shi kenan part ɗin mahaifi nashi domin har yanzu ya kasa tun ƙarar mahaifiyar tashi,
"Ina so ka ƙara tabbatar mani da maganar da ka faɗa a cen kankiya kan yarinyar nan, shin da gaske kana so ta?" Alhajin ya jefa mashi da tambayar bazata da ta ƙara ruɗa shi, ƙasa yayi da kanshi yana mai murza yatsun hannun shi, ya ma rasa me zai faɗa ma dad ɗin nashi.
" Eh Abba, da gaske nake, ina so ta, kuma a shirye nake da in taimaka mata. "
Ya faɗa ciki-ciki, sai dai duk da haka Alhajin ya ji shi,
"OK Son, Abunda nake so da kai, kabar maganar nan for now, saboda hajiya ta huro wuta, hakan zai sanya ta matsa ma zaman su acikin gidan nan, akwai abubuwa da dama gabanmu, na san mahaifiyar ka ko wacece, hakan zai sa tayi tinanin mun bar maganar ne, to sai dai zamu shirya dukkan Abunda zai yuwu ne bayan mun gano asalin ita yarinyar, talauci ko rashin mahaifi ba zai sanya in kasa barin ka ka aure ta ba, ina so ka sani, ni ba kaman mahaifiyarka nake ba, kuma itama ina mata addu'ar Allah ubangiji ya shirya ta, ta gane gaskiya" da ameen ya amsa iya maƙoshi, sannan Alhajin ya ɗora da faɗin
"Maganar karatun yarinyar, ina so kayi dukkan mai yuwuwa ta tafi makaranta, hakan zai bamu damar bincike na haƙiƙa, dole kuma sai da haɗin kan mahaifiyar yarinyar, sannan kaje ku daidaita da mahaifiyar ka, ga nemi gafarar ɓata mata da kayi, hakan ba yana nufin ka janye maganar auren naka ba, ina so kuma ka cire dukkan wata damuwa da ke cikin ranka, komai Kaga ya yuwu yi ne na Allah, na san dalilin ka na son auren yarinyar, nima na bada goyon baya ɗari bisa ɗari, Allah ya tabbatar mana da Alkahirinsa.
Nan ma da ameen ya amsa cikin zuciya, Alhajin ne ya wayance ya shiga janshi da firar kasuwanci, da shirin buɗe sabon estate ɗin su mai suna *Dambulan estate* da za'ayi zuwa ƙarshen shekara, wadda take mallaki Al'ameen ɗin.
Da haka ne ya samu ya saki jiki dashi, nan suka karya su uku, har da Bilal ɗin da ya shigo daga baya gaishe da Alhajin, bayan sun gama ne suka fice atare da Alhajin kaman wasu abokan shi.
Jikin Ummantawa yayi sauƙi sai Sam barka, hankalinmu a kwance, saboda ƴannkuɗaɗen da ya Ameen ɗin ya bamu, su ne muke riritawa da siyan abubuwan da likita ya gindaya ma umman tawa cinsu, tin bayan tafiyar su hajiya da kwana ɗaya bamu sake jin ɗuriyar shi ya Ameen ɗin ba, sai bayan dawowa su ne, saƙo ya iske mu, na dakatar damu daga aikin gidan gabaki ɗaya da aka yi daga bakin mama talatin, a cewar ta wai saboda jikin umman tawa, to mu dai duk da haka jikinmu yayi sanyi kwarai matuƙa, sai dai gudun sanya zargi wani abu, ko damuwa ya sanya muka kauda dukkan wani shakku a cikin ranmu game da hakan.
Hankalinmu bai ƙara tashi ba saida aka dena bamu abinci gabaki ɗaya, mun gane hakan ne ta yau da safe da na kai cooler ɗinmu kitchen a zuba mana abinci, sai mama sauden (mai girkin ma'aikata) tace man ya ƙare, abun ya bani mamaki sosai, sai na share na koma ɗaki na haɗa tea cikin kayan da ya ameen ɗin ya siyo mana kafin ya tafi na sha.
Da rana ma hakan ce ta kasance, wannan karon free ta fito ta faɗi man cewa an dakatar da bamu abinci a cikin gidan, saboda yanzu mu ba ma'aikata bane, abun ya bamu matuƙar mamaki, me hakan ke nufi ne? Ko dai wani ne ya ja mana wani sharri kuma? Umma ta ce ta bani haƙuri, da unurtata kada in sake komawa amso abinci, har saida suka mula, suka sha iska dan kansu suka bamu.
Ɗan Abunda ke gare mu a ɗaki, shi muka dinga ci ni da ni da umma ta, sai gashi nima na koma cin abunda masu ciwon zuciya suke ci; amman ya zamuyi? Dole mu haƙura, babu, ce da zama ƙarƙashin wani ya ja mana. Amman ace a gida irin wannan ya wuce ace ana irin haka ga masu aiki, sai dai in da wani abu a ƙasa.
****************
Da sallama ya shiga cikin ƙayataccen sashen nata, tana zaune bisa kujera tana waya da ƙawarta Hajiya Laila, cewa tayi ta bata minti biyu zata sake kiran ta, kashe wayar tayi tana mai amsa mashi gaisuwar da yake mata ciki ciki tayi, sannan ta ɗora da faɗin "ya aka yi ne Al'ameen?"
"Mom kiyi haƙuri please, babu kyau iyaye na fushi da ƴaƴansu nazo ne in baki haƙuri" ya faɗa a taƙaice idanun shi na bisa fuskar ta don ganin yanda zatayi
Ɗan guntun murmushi ta saki, cikin duniya ci tace "haba son menene haka? Ai ya riga da ya wuce, na san ba zaka yi Abunda zai ɓata man rai ba, Allah yayi maka Albarka" ina so kaje ka yankar ma su Afnan ticket saboda zuwa anjima zasu wuce, hutun nasu ya ƙare kada su rasa flight"
"OK ya faɗa yana mai miƙewa cikin salon tafiyar shi ya taka ya fice daga part ɗin na mahaifiyar shi, da tin dawowar su bai shige shi ba sai yau, saboda bai san abin da zai je ya tada ba, zuciyar shi cike da wasu wasu, me mahaifiyar tashi take ƙullawa ne? Shi fa yayi mamakin sauri saukowa ta, Amman koma minene zai bita ta ƙarƙashin ƙasa in ta san wata ai bata san wata ba.
Ita kuwa a ɓangaren ta, da murmushi ta bishi tana faɗin "yaro yaro ne, koda kuw ɗan giwa ne, kaman yanda ka bari cikin cikina, Al'ameen ka bar maryam da ɗiyar ta har Abadan abada, hhhhh" ta kyalƙyale da dariya shu'umanci, domin kuwa hajiya Lailan ta bata tabbacin hakan, ita kuma ta yarda da hajiya Lailan ɗari bisa ɗari, in tace zata yi, to fa zata yin ne, koda kuwa sama ce zata haɗe da ƙasan.
~Toh fa! Anya kuwa Hajiya Kubra Alkhairi take ƙullawa kuwa 🤔~
~Ya makoma Suhan da Umman ta a Rayuwar da ake ciki na hana su abincin da zasu ci ma?~
~Al'ameen kuwa ya bar maganar auren suhan ɗin? Ko dai irin abun nan yayi mata na yaro bari murna...~
~Oum-Deedat cee~
[9/15, 7:36 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah