Showing 54001 words to 57000 words out of 247770 words

Chapter 19 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10410

yaran masu kuɗi da faɗa aji a faɗin duniya suke so su samu, ba ma nigeria ba, yo wannan ko a India yaga wata yace yana so ai wallahi ba zata yi mashi musu ba, balle waɗancen talakawan"
Hajiya Kubra ce ta nisa gami da cewa " Humm bari dai Sa'a, wallahi kina ganin shi haka shegen tarin kai ne dashi kaman mahaifin shi, ba yanda banyi ba Amman abun yafi ƙarfi na, dama da dukiya nake taƙama, tau duk kansu daga shi har mahaifin nashi babu wanda bai fini ba a halin yanzu, nayi ƙoƙarin nuna ƙarfin uwa akan shi, Alhaji yana man ba razana da aure na, ni kau kjnga ba zanyi sake in rasa alhaji ba, samun kaman Alhaji a yanzu zai yi mani wahala... " Hajiya Laila ce ta katse ta da cewa ki bar mana komai a hannun mu Kubra, ba zai gagara ba, me aka yi a kayi Maryama balle wata ɗiyar ta cen, bari a gama hidimar nan zamu san abun yi, in ance ya ƙara kallon su ma ba zai kalla ba ko da kuɗi, kuma beside ma ni bana tinanin son ta yake yi, kinsan fa waɗannan miskilan yanda suke, nafi tinanin dai yana so ya kulle maki baki ne akan zancen aure da kike mashi" duk kansu sun gamsh Sa da hakan sun kuma sha alwashi ɗaukar mataki bayan kammala bikin Saudat da Nihal ɗin da yake saura sati biyu ayi.

Kai tsaye sashen shi ya koma, baya jin ma mararin fitar, idan ma ya fita ba inda za shi, shi ba mutum bane mai yawo, Shiyasa ma ko abokan kirki baya dasu, sau tari yafi buƙatar ya zauna gida yana aiwatar da dukkan muhimman abubuwa a cumputer ɗinshi akan ya fita ya ɓata lokacin shi ga banza wajen abokai, duk kuwa da yanda samari da dama ke fatan ace shi ɗin abokin su ne, koda kuwa na wucin gadi ne.

Bilal ya kira suka sha firar su, yake sanar dashi shigowar shi satin sama, domin su fara tsara yanda tashi hidimar zata kasance, "Abokina kayi ƙoƙari kaima ka fidda matar aure, duk da na san kai mata basa ga anka, Amman ai ba zaka ci gaba da zama haka ba, ko so kake yi ne sai mun haɗa ka da abie ne sannan zaka yi auren, ka kuwa san lokacin ka tsufa babu wadda zata gani ta ƙyasa"

Murmushi yayi irin wanda ke ƙara ƙawata mashi kyakkyawa fuskar shi, sannan ya shiga maida mashi da amsa "Ai sai kazo kayi mani malan, na lura kaima team ɗin Mom kake, Kaga mubar maganar nan sai kazo zamu tattauna, bari in tashi in fita wajen mata san cen da na sanya a tattara mani zamuyi meeting dasu da ƙarfe biyar na yammaci kasan yanda abubuwan suke yanzu wallahi, ina tinanin zan basu hutu ne har agama hidimar nan ta bikin yaran nan, kada kwalwa ta ta buga hakanan" "Is ok Friend sai kunyi magana" Bilal ɗin ya amsa mashi ta ɗaya ɓangaren, sallama sukayi yayin da ya tashi ya fice hannun shi ɗauke da ledar wayar nan.

Muɗi driver ya ba, ya umarce shi da ya kawo mani, shi zai fita ne sai ya dawo mmanka kula.

Cikin hanzari kuwa ya russuna ya amsa yana mai cewa "To yallaɓai" kai tsaye motar shi ya nufa, yayin da mudinya nufi sashen namu ba tare da ya damu da ya san menene acikin ledar ba.


Sallamar mudin ce ta katse ni daga shirya mana kaya da nake ta faman yi a wardrop, amsawa nayi gami da zura hijabina na leƙa ina mai gaida shi, amsawa yayi yana mai miƙo manledar dake hannun shi, "Gashi inji Alhaji ƙarami yace in kawo maki" amsa nayi ina mai cewa tou Mudi an gode, juyawa yayi ya bar wajen tin kafin wani ya gashi, yayin da na koma cikin ɗaki ina mai nuna ma umma ta dake zaune bisa darduma tana karatu.

"Wai Ya Ameen ne yace ya kawo mani" na faɗa ina dire ledar gabanta, ba tare da na damu da sanin menene ciki ba, duk a zato na Abunda ya danganci karatu na ne.

"Ki buɗe mana kiga menene a ciki" cewar umman tawa, tana mai ɗan ɗaure fuska haka kaɗan bansan menene dalili ba.

Kwalin dake cikin ledar na fiddo, gaba na ne ya faɗi, na ɗan ɗago na saci kallon umma ta da ta tura mani idanu taga yanda zanyi, hannu na kuma Sanyawa na zaro ƴar mitsitsiya waya ta da Naji tana vibrating a cikin ledar.

Saƙo ne ya shigo, number ce ban damu da in buɗe ba balle inga Abunda aka rubuta, durkushe nake gaban umman tawa kawai ina so inji hukuncin da zata yanke a kaina game da amsar kyautar waya daga hannun yaya Al'ameen ɗin.






~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._


*Page ~20~*


°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

Sai faman zare idanu nake yi, kaman wadda tayi ma sarki ƙarya, hukuncin umman tawa kawai nake jira inji me zata yanke akai.

Shiru tayi na tsawon minti biyar, nazari ɗiyar tata take yi, fatan take ace ba ita ce ta roƙeshi ba.

Nisawa tayi kaɗan a hankali ta muskuta, tana mai ajiye littafin dake hannun ta, har yanzu bata ɗauke idanun ta akai na ba.

" Suhan! Ina fatan dai ace ba kece kika roƙeshi waya ba, ba zaki iya haƙuri da wadda Allah ya baki ba" na tsinkayo muryar ta kwatsam cikin kunne na.

Girgiza mata kai na cigaba da yi, ina cewa "a'a umma wallahi ban roƙeshi ba" kwashe yanda muka yi da yaran nan nayi a makaranta kwana biyu da suka wuce, har zuwa kan inda ya ɗauki wayar bai bani ba, Amman ban gaya mata ya goge man ƙwalla ba, balle ince ya kama man hannu, don na san tashin hankalin da zan fuskanta.

Shiru ta sake yi sannan tace "Allah shi kyauta, an gode, Amman ina so ki riƙe talaucin ki, ki dinga juya ma abun duniya baya, wannan ƴar ƙaramar ta isheki, sai dai bazan hana ki amfani da wannan ba, saboda zamani ne yazo da ita"

Cikin ɗan murmushi nace "to umma nagode" sake kallo na tayi da wani irin yanayi, sannan ta shiga cewa "sai ki kira shi kiyi mashi godiya ko? Sannan ki kula ba zan gaji da cewa ki kula ba, kindai san zaman da mukeyi a gidan nan"

"Eh umma haka ne, to zanyi mashi godiya insha Allah" na faɗa murya ta fal farin ciki, sai dai cen ƙasa zuciya ta, wani irin tsoro ne da fargaba, me zai faru idan aka ce maganan Afnan ce ta fara tabbata?, me ne ya sanya shi share man hawaye Wancen lokacin? Me hakan ke nufi?"

Jikina ne yayi sanyi ƙalau, komawa nayi na zauna, ina mai zaro wayar daga cikin kwalin ta, waya ce mai matuƙar kyau da tsada, ko a cikin ƴaƴan masu dashi ɗin ba kowa ne ke riƙe irin ta ba.

Gashi tana da girma, har ina jin tayi ma hannuna mugun girma wajen riƙewa, saidai ko babu komai nayi farin ciki, ɗan chatting ɗin nan da kowa keyi nima zan fara, zan ga me duniya ke ciki, lokaci ne nima da zan fita daga cikin wannan duhun kan zama waje ɗayan.

Ban mantawa, lokacin da nake secondry school, dukka kusan ƴan ajinmu na da waya, kasancewar ta makaranta da ƴaƴan manya, wasu ma biyu ne suke da ita.

Ɗan murmusawa nayi, tinowa da nayi yanzu fa har afnan zamu dinga magana da ita kullum, ga wata ƙawata tin ta makaranta mai suna khairat, ta soni sosai, tana tausaya mani, ita gidan su masu hali ne, har wayar taso bani, nice dai na ƙiya don na san halin umma ta, yanzu gashi da nayi haƙuri na samu irin wadda ban zata ba ban tsammani ba.

Kunna ta nayi, aiko ta ɗauka kaman jira take yi, nayi mamakin da layi ciki guda ɗaya, saidai babu komai a kanta sai Numbers guda biyu an masu saving da AMD bansan me hakan ke nufi ba.

Niyyar goge su nayi, sai kuma wani tinani ya ɗarsu a zuciya ta, in shi ya ajiye su da? In suna da muhimmanci fa? Share wa nayi ban ko taɓa mashi abun shi ba, na jawo waya ta ina maida numbobi na ciki, har da ta khairat ƙawa ta da na janye mawa kusan shekara nawa? Itama ganin hakan sai ta haƙura ta ƙyale ni, kada ta jaza man matsala, fahimta da tayi umman tawa bata son tarayya ta da ita. Ko tana ina ma yanzu haka?

Dukkan motsi na umma ta na kula dashi, tausayi na ne fal acikin ranta, tana addu'a Allah ya kawo lokacin da nima zan zama wata abu, lokacin da zamu fita a halin ƙuncin da muke ciki, lokacin da muma zamu zama mutane masu cikakken ƴanci kaman kowa.

Sallamar Hafsat ɗince ta katse mana zaman shirun da muke, niko ina ta faman jujjuya waya a hannu, mamaki ya cika ni, ta yadda naga kuɗi tsababa cikin wayar, yanzu ko na tabbata wayar tashi ce, ƙila siyan ta yayi yana amfani da ita ya bani, bata san shine ya siya domin ita ba, ya zuba kuɗi domin ita, saboda harga Allah cin mutumcin da aka yi mata yayi mashi ciwo, ace kaman wanda yake gidan su ace ana ci mashi mutumci saboda wani abu wai waya, menene amfanin arziƙi nasu in har ba zai kare mutumcin mutanen dake rayuwa cikin shi ba?

Da murmushi na bita ina mai cewa "A'a Hafsy ce? Shigo mana" na faɗa ina nuna mata gefen katifa inda nake zaune, alamar ta zauna, murmushi tayi ta ƙara so ta zauna tana gaida umman tawa, itama cikin dakin fuska ta amsa tana mai sake tambayar ta maman su, duk suna lafiya tace, a hankali suka shiga fira da umman tawa, yayin da ni kuma hankali na na kan waya, har umman tawa ta miƙe ta shiga ban ɗaki, sai a sannan ne ta maido hankalin ta kaina.

Hannu ta sanya ta amshi wayar, tana murmushi take faɗin "Ya Suhan, wannan mai zafin fa? Yaushe kika shiga yayi ban sani ba? Domin dai ina da number ɗinki, Amman naga ko WhatsApp bakyayi kuma kina da irin wannan babbar waya haka, ko ni fa bana iya riƙe irin ta" ta faɗa fuska cike da murmushi, ta ƙara she da zaulaya.

Hafsat ɗin dai kaman yanda kuka sani ɗiya ce ta yayan Alhaji mustapha Dambulan, watau Alhaji Auwalu da yaje zaune cen Katsina, tana zuwa gidan akai akai, in suna ƙasar, saboda iyayen su masu zumunci ne akai akai, suna yawan tura ƴaƴan su gidajen nasu, hatta su saudat ɗin ana tura su Katsina, duk da dai basa so, suna cewa takura suke yi wai basa walawa a gidan yayi masu ƙarami, duk da kuwa irin girman gidan nan da kayan more rayuwa dake cikin shi shima, domin yanzu Alhaji Auwalun ya kai matsayi director a ma'aikata tasu,ya samu rufin asiri daidai gwargwado, duk da kuwa bai ko kama ƙafar Alhaji Mustaphan ba. Bana hafsat kaɗai ba, dukkan in ƴaƴan Alhaji Auwalun da hajiya zainab, yara ne masu sanyin hali, girmama naga a dasu, da kuma kawaici, basa da girman kai Sam, wannan ce ta sanya tamu tazo ɗaya da Hafsat ɗin da ko zata girme mani tau fa da kaɗan ne. Ita dai ba'a isa a hana ta zuwa sashe namu ba, hasali a In tazo ba wani damuwa da al'amarin ta suke ba, ba ta ita suke yi ba, lokutta d adama ma haushin ta suke ji, suna cewa duhun kai yayi mata yawa, itama ta gama karatun ta tsaf a makarantar ummaru Musa ƴar adu'a dake jihar Katsina dabon.

Sai gashi kuma Allah ya bata miji nagari, na nuna ma sa'a, hasali ma dukka mazajen daga na Saudat, har Nihal ɗin babu Abunda zasu nuna ma nata, sai ma shi ya nuna masu tarbiyya da kuma dattako.

Murmushi na ɗanyi ina cewa "Uhm Hafsy kenan, nima yanzu wayar ta iso mani wlh" kasancewar ta mutum da ta san halin da muke ciki, da irin zaman da mukeyi, ya sanya na kwashe labarin yanda aka yi na samu wayar na faɗa mata.

Aiko murna ta fara yi, tana ce an "kinga kada ki damu, rabon ki ne ya rantse, ai Ya Ameen ɗin mutumin kirki ne, Sam shi ba halin su ɗaya dashi ba, yana taimakon na ƙasa dashi, ko bayan dawowar mu Naji ana cewa ya raba ma dukkan in ma'aikatan kamfanoninshi kayan abinci da tufa fi masu kyau da tsada, a bakin su Hajiya Naji da tana waya da wasu ɗazu.

Amsar wayar tayi ta shiga buɗe man abubuwa irin su WhatsApp, Facebook, da wani chat wai shi duo, nice nace ta bar shi hakanan, har sai na iya waɗannan tukunna.

Fira muka shiga yi sosai, har take cewa zata dawo ɗakinmu da zama kafin lokacin tafiyar tata yayi, nake ce mata tayi haƙuri ta rufa mana asiri, kwanciyar ta tayi tana cewa "uhmm, kanki kuma akeji Suhan, KEDAI Allah yayi maki tsoro kaman farar kura"

Koda ta sanar da umman tawa da ta fito daga banɗaki, murmushi kawai tayi, ai kaso mai sonka ka kuma girmama duk wanda yace yana sonka.

"Umma wata Alfarma nake so in roƙe ki don Allah, ki ara man suhana ta taya ni zuwa wajen gyaran jikin, da ƙarashe siyayya har zuwa lokacin da zan koma gida, kinga dai su Saudat ware ni suke yi, bana da aboki ko ɗan uwan da zan tun kara, Suhan ɗin dai ita ce"

Hafsat ɗin ta faɗa tana marairaicewa, kaman wadda zata yi kuka, lokaci guda tana kallon umman tawa.

Ba matsala umma ta tabbatar mata, saidai taja hankalin u akan mu kula da me mukeyi, idan mun fita mu san ina zamu, kuma kada mu sake mukai magariba a waje waɗannan sune sharuɗɗan ta.

Da to muka bita, hafsat ɗin kuwa taji daɗi, dama ko ba komai bata kawo ma ranta umman tawa zata hana, saidai ta san halin umman tawa, wani lokaci kaman mai aljannu take, zata iya hanawa a lokacin da ba'a tsammata ba.

Faɗa mata nayi ina son in kira yayan in mashi godiya Amman ina jin kunya, harara ta tayi cikin wasa tana cewa "menene na kunya Suhan? Ai ya yanki ne yanzu an riga an zama ɗaya, ki kira shi kawai wlh, ko kuma ki tura mashi text ai zai gani godiya daɗi gareta, balle yayan namu da yake miskili yana iya dakin fara godiya ya katse wayar"

Amincewa nayi da gara in mashi text, in mun haɗu a zahiri na ƙara gode mashi, sai dai fa inda gizo ke saƙar, bansan me zan rubuta ba, sai jujjuya wayar nake a hannu.

Hakan da ta fahimta ne ta fizge wayar a hannu na tana cewa "Dallah kawo nan, kai a tukunya, ai gara ma kizo kije makarantar ko kin ƙara wayewa, godiya ma kin gagara yanda zakiyi ta, wannan duk lokacin da kika yi saurayi naga yanda zakiyi dashi" ta faɗa cikin zaulaya da dariya, Nidai bance mata komai ba, sai a kishingiɗawa da nayi ina mai ɗan murmusawa a hankali.

Ban san me ta rubuta ba, na dai ga kawai ta jawo wayar ta ta ɗauki number ɗinshi ta tura, sannan ta miƙa man wayar tana faɗin "Done, saƙo ya isa"

Firar mu muka cigaba da yi, tana faɗ man yanda tsare tsaren bikin nata zai gudana, duk da ba wani pherty zata yi ba illa iyaka traditional day da za'a gudanar lambun gidan, wanda su kau su saudat sun haɗa pherty ya kai kala biyar wata rana ma sau biyu za'ayi.

Ita dai tace ba zata shiga ba, cikin hidimar su, bata da ra'ayi, duk da mijin nata yaso ayi ko kala biyu ne saboda abokan shi, Amman ta kafe kawai tace kowa ya sanyo kayan gargajiya, yazo yaci goruba ya sha rake🤣🤣

Nan ne na ƙara fahimtar sauƙi hali irin na hafsat ɗin, lallai duniya da Abunda ke ciki ta basa gabanta, tana tausaya ma mijin nata, tace wannan kuɗin da zai kashe sun isa yayi hidima da baƙin shi har su tafi.


********************

Shigar shi kenan part ɗin nashi, a matuƙar gajiye yake, waya kawai yayi ma Nihal ta kawo mashi snacs yunwa yake ji, kai tsaye ɗakin shi ya faɗa ya shiga kwaɓe kayanshi, wanka yake son yi ko zaiji sauƙi gajiyar dake nuƙurƙusar shi, gashi part ɗin nashi yayi matuƙar dauɗa, rabon da ya samu kyakkyawa n gyara tin wanda Suhan ɗin tayi mashi.

Bayan ya gama wankan ne, ya shirya cikin pajmas na maza, saboda sauƙin nauyin su, gashi yana so ya kwanta ya ɗan huta, sallama yaji ta baƙuwa murya daga cen falin nashi, a hankali ya miƙe gami da fita domin ganin wake sallama, kaman muryar mace yake iya jiyowa.

Maree ce tsaye, hannun ta ɗauke da farar roba mai garai garai, kana iya hango Abunda ke ciki, a tsakiyar falin ya iske ta tsaye tana ƙare ma sashe nashi kallo, ita asali ma bata taɓa shigowa cikin shi ba, saidai kawai ta hango shi daga nesa, duk da a zahiri kasan zubin nashi dama zai yi kyau, saidai ya zarta yanda take tunani.

Ƙamshin turare ne, ya alamta mata lallai akwai wani tsaye kusa da ita, ɗan zabura tayi kaɗan tana cewa "Yallaɓai barka da hutawa, gashi inji Aunty Nihal tace in kawo maka" ta faɗa tana miƙa mashi robar cikin ƴar rissinawa tana wani far-far da idanu, ko kallon ta baiyi ba, ya nuna mata stool dake gefen kujera ajiye, alamar ta ajiye

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login