Showing 75001 words to 78000 words out of 247770 words

Chapter 26 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10457

da yin wanka, a haka suka janki dole ba don naso ba na bisu sashe nasu na amare, itama dai ummata taji daɗin hakan, domin bata son kwanciyar da nake yawan yi, gashi ta kula jikina a sanyaye, in nazauna nan kuma ba abokin fira saidai inta tinani.

Itama wanka tayi ta fice zuwa sashe nasu Hafsat domin ta gani ko da Abunda zata kama.

Wata ƴar matashiya yarinya ce tayi sallama ɗakin namu, amsawa mukayi mu duka da muke zazzaune ana ta fama fira da bada labarin event ɗin da aka yi jiya, "Wacece Suhana a cikin ku?" ta faɗa cike da yatsina, nuna ni Hafsat tayi gami da cewa "gata nan lafiya dai ko?" "eh lafiyar kenan, Saudat ce ke kiran ta" tana gama faɗar haka ta juya gami da ficewa.

Afnan ce ta miƙe gudun kada a wulaƙanta ni bayan naje, "muje in raka ki" jerawa mukayi har ɗakin nasu gami da sallama, mun taddasu zazzaune bisa gado wasu a sama carpet, sun yi break oast ko ina gaja gaja, wasu ma duk babu kaya jikin su illa na barci ƴan yalolo.

"Ɗakin nan zaki gyara mana ki wanke mana toilet yayi datti gashi muna son yin wanka" Saudat ɗin ta faɗa cikin gadara da nuna isa, binsu nashigayi da kallo, su su ɓata don son neman magana Amman nice za'a kira in gyara bayan an dakatar damu daga aikin da mukeyi a cikin gidan? Afnan ce tayi saurin cewa "Amman fa Aunty Saudat an hana suhan aiki a cikin gidan nan, ko dai maree za'a kira maki?"


"Ke" ta daka mata muguwar tsawa da har saida na razana, su kau sauran ƙawayen nasu ƙyalƙyalewa sukayi da dariya, wasu na latsa waya wasu ma system ce a gaban su ba Abunda ya sha masu kai.

"Je na kira da zaki biyo wa? Ko kin biyo ta ne ki gani in aiki zan sanya ta ki hana ta? Zaman me suke yi mana a cikin gida? In banda son su mallake mana yaya su mallake Abunda ya mallaka? To dole ne ayi mana aiki wallahi ko a tattara a ƙara gaba" ta faɗa cikin matuƙar ɗagawa da karara zance yanda zai shiga har cikin ƙwalwa ta, ya kuwa shiga a sanyaye na kalli afnan ina mai cewa "Afnan bashi kawai zanyi, ki koma ɗaki don Allah"

Afnan ɗince ta ƙuta gami da ficewa a hasale ta koma ɗakin nasu, ni kuwa tattare hijab nayi na shiga aiki, wata daga cikin ƙawayen nasu, wadda na kula tana yawan zubda mannhabaicinlomuta da dama in suna falo zaune ce tayi ƴar dariya cikin salo na son cin mutumci ta shiga faɗin "Haba Saudat bari wannan maganar mana, ai yayan namu ya wuce ajin wannan yo in banda ma ke da abunki me zai ci da ƴar aiki irin wannan? Dubeta fa ai in ba don Allah ya sanya tana da ɗaske ba da ba ƙaramar mummuna aka yi nan ba, duk tarin matan da suke sonshi a faɗin garin na Abuja da kewaye ya rasa wadda zai kula sai wannan? " ta ƙarshe tana mai nuna ni da hannu.

Shewa suka sany gami da tafawa, ni kuwa zuciya ta zo man iya wuya, saidai bana son tashin hankali ummata ba lafiya ce gareta ba, inko har na tanka abun kanta zai koma, gara a lallaɓa a rabu lafiya duka saura kwana nawa ne a rabun?

Girgiza kaina nayi gami da cigaba da aiki, raina na matuƙar ƙuna, Allah sarki Ya Ameen a kammu fa zai gamu da ƙalubale da dama tinda yace yana so ya taimake mu.

A haka na kammala masu gami da ficewa daga ɗakin a matuƙar sanyaye, maganganu marasa daɗi dai yau na sha su, a hakan ma wani abun baya faɗuwa, har kwalla saida nayi ta baƙin ciki, Amman Allah ya san damu bai manta damu ba.

Ina komawa sashe namu Hafsat ta balbaleni da faɗa wai akan me nayi aikin ban ce mata banayi, ni kau ce mata nayi nayi aikin ne saboda ummata kada abun ya shafe ta, tana jin haka taja baki tayi shiru Amman fa ranta ya gama ɓaci, ita kuwa afnan haƙuri ta bani tana cewa sai ta gaya ma ya Ameen ɗin, nice na hana ta ina mai cewa haba ai ko ba komai su ɗin yayye na ne ba Abunda ba zan iya masu ba, saidai in har basu buƙata ba.

Muna cikin haka ne wayata ta ɗauki tsuwwa alamar an mani saƙo, dubawa nayi mamaki fal a fuska ta, Ya Ameen ne ya turo mani saƙo kaman haka



_Ya ƙarfin jiki, kin dai sha magani ko?_

Ɗan murmushi na sauke, raina yyai fari ko ba komai dai idan wani ya ƙi ka wani zai soka, duk da su ɗin sun nuna man halin ƙiyayya ga ƴaƴan su nan yana nuna man halin kula.

Ban maida mashi da reply ba na share, muka cigaba da fira, wani saƙon ne ya shigo

_"kina dai lafiya ko?"_


Wannan karon nima maida mashi nayi da cewa

_" Eh yaya ina lafiya, nagode da kulawa"_

Shigowar saƙon nata ne ya sanya shi tashi zaune, dama dai yana son yaji halin da take ciki ne, kada ace mahaifiyar tashi ta koma ta sake yin wani abun kuma.

Bilal ɗin dai na kallon shi kanzil bai ce mashi ba, sai faman ɓoye murmushi da yake yi, ajiye wayar tashi yayi gami da shige wa toilet domin yin wanka saboda yanzun kusan ƙarfe sha biyu da rabi lokacin sallar juma'a ya ƙara to.

Saida Bilal ɗin yaji alamar ya fara watsa ruwa sannan ne ya ɗauki wayar tashi ya shiga duba saƙonni.

Tiryan Tiryan ya shiga bin saƙonnin da suka aike wa juna, saidai shi baicin karo da wani saƙo dake nuna soyayya ba, illa iyaka kulawa da kuma saƙon godiya da ta taɓa aike mashi da daɗewa bayan ya bata waya.

Jin alamar fitowa ya sanya shi saurin kashewa ya ajiye, shi dama ya riga ya shirya Al'ameen ɗin yake jira, miskilancin na na na a kai, ya sanya bai tanka ma Bilal ɗin ba har ya gama shiryawa, saidai yana kula da Bilal ɗin da irin kallon da yake bin shi, basarwa yayi yana faɗin zaka ci ubanka ne ai.

Daidai parking lot muka haɗu dasu, tin daga nesa na hango su, hakan ce ta sanya ni ƙara ɗaga ƙafa, afnan ce taja ta tsaya tana cewa Laa ga yaya bari yazo mu gaisa tin jiya rabona dashi, Ganin Hafsat ɗinma ta tsaya dole nima naja na tsaya.

Cikin tafiyar shi ta ingarma namiji suka ƙaraso gare mu, afnan bata yi wata wata ba ta rungume shi tana faɗin oyoyo yaya, shima rungume ta yayi kaɗan yana mai janye ta daga jikin shi ya shafi gefen fuskar ta "Ya kike sweet Heart? Ya faɗa cikin kulawa hannuwan shi cikin nata," Lafiya Lau Bro love"

Mu kau ganin hankalin shi na ga Afnan ɗin sai muka shiga gaida Bilal, Bilal ɗin da ya kafe ni da ido ne ya amsa mana, duk hankalin shi na a kaina, har saida na tsargu na duƙar da kaina, Hafsat ce na ji tana gaida Ya Ameen ɗin shi kuma ya amsa mata cikin kulawa, ɗago kaina nayi da niyyar gaida shi idanun mu suka sarƙe cikin na juna, wani irin shirk ne Naji ya jani kaman an jona man wutar lantarki, yayi kyau cikin dakakkiyar shadda shi ruwan sarari samaniya, hula da takalmin dake kanshi duk kalar shadda ne, saidai hannun shi dake ɗaure da haɗaddiyar agogo ƙirar kamfani gucci riƙe yake da makullan mota, fuskar nan tayi fayau da ita, sai ƙasumbar da take kwance a haɓarshi ce ta ba fuskar damar ƙara haske idanun shi manne ikin fari tar ɗin glass da ya ƙara fiddo da kyaun fuskar tashi.

Saurin sadda kaina nayin ƙasa ina mai matse ƴan yatsu na, domin wani abu Naji ya tsira mani tin daga kai har tafin ƙafa ta, "Ba gaisuwa?" Naji ya faɗa, saurin ɗaga kaina nayi gami da kallon shi ina addu'ar dai ace ba dani yake ba.

Idanuwan shi kuwa fes a kaina, "Ina yini" na faɗa ina mai son kauda kaina ga barin kallon shi, ji nake yi duk ya cika gidan, irin Abunda nake fuskanta kenan a duk lokacin da zan ɗora idona a kanshi.

"Ba zan amsa ba, tinda saida na roƙa" ya faɗa yana mai zagaye mu ya wuce zuwa ga motar shi, da tini Bilal ya isa yana jiran shi, da kallo na bishi har ya wuce, lallai ya Ameen ya haɗu ta ko ina, cikakken namiji ne mai tarin kwarjini....

Ɗan ɓangazata Afnan tayi da kafaɗa ganin yanda nabi yayan nata da kallo tana murmushi cikin zaulaya take cewa "Lallai Aunty Suhan yayan nawa yana yin ki, ga dukkan alamu kema kina yin shi na gani"

Ɗan firgigit na dawo hayyaci na daga da tinanin da na tafi na wucin gadi, buɗe baki nayi da da niyyar cewa wani abu muka ji cikin kakkausar murya daga bayan mu ance

*Al'ameen*

Dukanmu juyawa mukayi gami da maida hankalin mu wurin

Hajiya Kubra da take tsaye tin ɗazu tana nazarin mu ta fara tako wa a hankali cikin isa da taƙama fuskar ta tam babu fara'a ko alama a fuskar

Sanye take cikin wata haɗaɗɗiyar atamfa anyi mata ɗinkin nan mai A shape marar breast cup, sai ɗan kunne da sarƙar gold gami da abun hannun su danƙara danƙara sai walwali takeyi.

Tini jikina ya fara ɓari naja baya a sukwane, ni da Al' ameen kawai na lura take kallo, Al'ameen wanda har ya sanya key zai buɗe mota ya fasa gami da dawowa inda taja burki ta tsaya gami da cewa

"Gani mom Lafiya dai ko?"

Ya faɗa yana mai kafe ta da idanu, cikin fushi ta buɗe baki gami da cewa........

😛😝😜🤪😜🤪😛😝🤪😜😛😝

~ku tara a Page na gaba~


~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._

*Page ~27~*

*Page ɗinki ne Aishatu Babayo, muna matuƙar yinki, kuma muna jin daɗin comment ɗinki matuƙa, ɗaukacin ƴan golden pen suna gaisheki*

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

"Kasha maganin ka ne da kake ƙoƙarin fita?"

Mom ɗin tashi ta faɗa, har yanzu fuskar ta a matuƙar ɗaure take.

Gyaɗa mata kai kawai yayi, ba tare da ya tanka mata ba, kallon ta ta maida kan Bilal da yake tsaye ta bayan Al'ameen kaɗan haka, yana gaida ta.

Amsawa tayi gami da cewa" Bilal ka kula fa da abokin ka sosai, kada ka bari ya wahala Kaga dai Abunda Dr. Yace". Ɗaga mata kai Bilal ɗin ya shiga yi yana cewa "consider it done Mom"

Hafsat na tsinkayi muryar ta tana gaida ta, hakan ce tasa nima na gaishe ta, gaisuwar Hafsat ɗin kawai ta amsa, itama a daƙile, hakan ce ta sanya na ƙara shan jinin jikina gami da ƙara ɗan matsawa baya.

Afnan ce ta ruga kusa da yayan nata, daidai lokacin da Mom ɗin ta juya da niyyar barin wurin, maganar Afnan ɗince ta dakatar da ita da barin wurin da take niyyar yi.

"Yaya me ya same ka? Baka lafiya ne? Yaushe kaje hospital bamu sani ba? Duk ta jero mashi tambayoyi tana mai kamo hannuwan shi gami da dudduba jikin shi da idanu.

Ɗan zare hannun shi yayi yana mai shafo gefen fuskar ta kaɗan," Am OK Dear Love, ba Abunda ke damuna" ya faɗa yana mai juyawa ya nufi jikin motar tashi, domin ya kula sosai da rashin amsa gaisuwar da mahaifiyarshi tayi ma Suhan ɗin.

Bai jira komai ba ya buɗe motar gami da shiga, shima Bilal ɗin shiga yayi, ganin haka ne Hafsat ɗin ta shiga jan hannuna tana cewa "zo muje Suhan, Afnan ɗin zata tadda mu"

Binta na shiga yi, muka shiga tafiya, daidai lokacin da Mom ɗin ta bimu da kallon tsana da jin haushi ƙarara a fuskar ta.

Afnan ce ta bita da kallo daidai lokacin da ta juya da niyyar wucewa sashe kaka zuwaira, girgiza kanta ta shiga yi tana mai ɗaga ma yayan nata hannu har ya fice daga gidan.

Bayan an sauko masallacin ne kiran Alhaji Mustapha ya shiga wayar tashi, umurtar shi yayi da yazo gidan gonarshi yana son ganinshi yanzu shi da Bilal ɗin.

Sai da ya ɗauki hanyar gidan gonar ne, yake sheda ma Bilal ɗin kiran da dad ɗin nashi keyi masu. Har suka isa babu mai tanka ma wani.

Sun tadda falon cike da manyan mutane, sai firar su suke cikin nishaɗi, ga sanyin Ac na ratsa su, wucewa sukayi cen gefe gami da zama ƙasa domin girmamawa ga iyayen nasu.

Miƙa mashi wata kyakkyawar emvelop mai ado da ruwan gold dad ɗin yayi yana mai cewa duba nan ka gani.

Amsa yayi cikin girmamawa ya shiga dubawa, bayan ya gama karantawa ne ya miƙa ma Bilal ɗin, ya maida duban shi kan mahaifin nashi yana mai neman ƙarin bayani.

Dad ya gyara zama gami da duban yaron nashi cikin soyayya, farin ciki fal a kan fuskar shi, sannan ya cigaba da cewa"Daga sarkin Katsina ne, haɗin guiwa da sauran sarakunan yankin namu na arewa, saboda yanda kake taimakon matasa ƴan uwanka da basu ayyukan yi, da taimaka masu da jari, da koya masu sana'oi, suka ga ya dace su girmama ka domin suma sauran matasan masu hannu da shuni suyi koyi da kai, sun yanke shawarar naɗa ka sarautar *yariman matasan arewa* kuma suna buƙatar daga yau zuwa gobe ka shirya komai domin a goben ne zasuyi maka naɗin bayan kammala ɗaurin aure, sannan kuma akwai hawan daba bayan kammala lunching ƙarfe biyar na yamma, da fatan zaku je ku shisshirya komai da ake da buƙata, sannan inaso ka aika manyan motoci guda biyu Katsina da zasu kwaso iyayen matar Aleeyu tin da safe su juyo dasu



~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._

*Page ~27~*

*Page ɗinki ne Aishatu Babayo, muna matuƙar yinki, kuma muna jin daɗin comment ɗinki matuƙa, ɗaukacin ƴan golden pen suna gaisheki*

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

"Kasha maganin ka ne da kake ƙoƙarin fita?"

Mom ɗin tashi ta faɗa, har yanzu fuskar ta a matuƙar ɗaure take.

Gyaɗa mata kai kawai yayi, ba tare da ya tanka mata ba, kallon ta ta maida kan Bilal da yake tsaye ta bayan Al'ameen kaɗan haka, yana gaida ta.

Amsawa tayi gami da cewa" Bilal ka kula fa da abokin ka sosai, kada ka bari ya wahala Kaga dai Abunda Dr. Yace". Ɗaga mata kai Bilal ɗin ya shiga yi yana cewa "consider it done Mom"

Hafsat na tsinkayi muryar ta tana gaida ta, hakan ce tasa nima na gaishe ta, gaisuwar Hafsat ɗin kawai ta amsa, itama a daƙile, hakan ce ta sanya na ƙara shan jinin jikina gami da ƙara ɗan matsawa baya.

Afnan ce ta ruga kusa da yayan nata, daidai lokacin da Mom ɗin ta juya da niyyar barin wurin, maganar Afnan ɗince ta dakatar da ita da barin wurin da take niyyar yi.

"Yaya me ya same ka? Baka lafiya ne? Yaushe kaje hospital bamu sani ba? Duk ta jero mashi tambayoyi tana mai kamo hannuwan shi gami da dudduba jikin shi da idanu.

Ɗan zare hannun shi yayi yana mai shafo gefen fuskar ta kaɗan," Am OK Dear Love, ba Abunda ke damuna" ya faɗa yana mai juyawa ya nufi jikin motar tashi, domin ya kula sosai da rashin amsa gaisuwar da mahaifiyarshi tayi ma Suhan ɗin.

Bai jira komai ba ya buɗe motar gami da shiga, shima Bilal ɗin shiga yayi, ganin haka ne Hafsat ɗin ta shiga jan hannuna tana cewa "zo muje Suhan, Afnan ɗin zata tadda mu"

Binta na shiga yi, muka shiga tafiya, daidai lokacin da Mom ɗin ta bimu da kallon tsana da jin haushi ƙarara a fuskar ta.

Afnan ce ta bita da kallo daidai lokacin da ta juya da niyyar wucewa sashe kaka zuwaira, girgiza kanta ta shiga yi tana mai ɗaga ma yayan nata hannu har ya fice daga gidan.

Bayan an sauko masallacin ne kiran Alhaji Mustapha ya shiga wayar tashi, umurtar shi yayi da yazo gidan gonarshi yana son ganinshi yanzu shi da Bilal ɗin.

Sai da ya ɗauki hanyar gidan gonar ne, yake sheda ma Bilal ɗin kiran da dad ɗin nashi keyi masu. Har suka isa babu mai tanka ma wani.

Sun tadda falon cike da manyan mutane, sai firar su suke cikin nishaɗi, ga sanyin Ac na ratsa su, wucewa sukayi cen gefe gami da zama ƙasa domin girmamawa ga iyayen nasu.

Miƙa mashi wata kyakkyawar emvelop mai ado da ruwan gold dad ɗin yayi yana mai cewa duba nan ka gani.

Amsa yayi cikin girmamawa ya shiga dubawa, bayan ya gama karantawa ne ya miƙa ma Bilal ɗin, ya maida duban shi kan mahaifin nashi yana mai neman ƙarin bayani.

Dad ya gyara zama gami da duban yaron nashi cikin soyayya, farin ciki fal a kan fuskar shi, "Daga sarkin Katsina ne, haɗin guiwa da sauran sarakunan yankin namu na arewa



~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login