Showing 150001 words to 153000 words out of 247770 words

Chapter 51 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10465

gadon nawa da ya wadata da katifa mai matuƙar taushi.

Ɗakin umman na ƙanƙwasa, daga ciki ta bani umurnin in shiga.

Tura ƙofar nayi a hankali ina mai shiga ɗakin, gefen gado na samu na zauna ina mai faɗa ma umma na kasa bacci ni ɗaya.

Cewa tayi in kwanta nan bisa gadon nata, zuciyar tata fal da tausayi na, ta kula yarinyar tata gabaki ɗaya kaman bata yi murna da wannan auren nata ba,tsoro ne fal acikin zuciyar yarinyar tata, saidai ba zata taɓa fuskanta ba, dalilin zaman nata a wannan gidan, da dalilin auren Alhajin da tayi duk yana da nasaba da ita Suhan ɗinne.

Ban yi baccin kirki ba, kaman yanda itama umman bata yi ba, tana kula da dukkanin juye juye na.

Saidai bata tanka mani ba, sai ma miƙewa da tayi ta dosa sallolinta.

To shima dai ɗin gogan zamu iya cewa bai runtsa ba ko sau ɗaya.

Abubuwa ne fal yake damun shi cikin zuciya. Ɓangare ɗaya Mom ɗin tashi ce ke kai komo.

Wani Al'amari irin na uwa da ɗa ke taso mashi, sai kuma cen ƙasan zuciyar shi Suhan ɗin ce tayi tsaye ƙiƙam, duk son da yayi na ya matsar da ita ya kasa.

Sai kuma tinani da taraddadin dalilin Dad ɗin nashi na son auren Umman Suhan ɗin, wanna amsar dai a yanzu kam baya da ita. Zai jira har lokacin da Alhajin nashi zai warware mashi zare da abawa.

Tin da farar safiya yayi shiri ya fice daga gidan, Bilal ya tsaya ya ɗauka sannan suka wuce.

Mu kau tin bayan munyi wanka, sai kuma muka koma zaman jigum jigum.

Nikam miƙewa nayi na koma falo, domin yana yin da nake ciki ba zan iya fasalta komai ba, cikin raina tausayin yanda rayuwa ke walagigi dani nakeyi, a hankali a hankali nakan sanya yatsa in share kwallar da take bi mani fuska, sai nayi kaman in kira Sir Salim ko zai sanya ni dariya ko da kuwa sau ɗaya ne sai na kasa.

Ina jin Kunyar ince mashi mahaifiya ta ce tayi aure, Amman kuma ya zama dole ya san inda nake ko don saboda sanin halin da makaranta take ciki.


Dirin mitoci ne ya karaɗe ilahirin gidan, sai kuma muka ji hayaniya ta ɓarke a gidan.

Miƙewa nayi a hankali na isa ga wangamememiyar tagar da take falon, leƙawa nayi, saida gabana ya ruguje ya faɗi.

Ƴan kankiya ne su da yawa, ƙwansu da kwarkwata, duk wani wanda zai iya zuwa saida yazo.

Hajiya Zainab ce gaba gaba, sai kuma Hafsat a gefen ta daƙyar take cira ƙafa saboda girman da cikin ta yayi.

Gaza matsawa nayi, ita kuwa Ummata tinda taji hayaniya ta tashi ta shige ɗaki ta barni nan tsaye ina mai binta da kallo.

Hafsat ta riga kowa shigowa, da sauri ta shigo tana mai dube dube kaman tana neman wani abu, sai kuma naga ta saki murmushi ta nufo ni, tana mai rungume ni tsam a jikin ta.

Shigowa suka fara yi, lallai suna da yawa, hannuna Hafsat ɗin taja alamun inzo mu shiga ɗaki, ganin bata san ɗakin bane ya sanya na shiga wucewa gaba, tana biye dani.

Ɗaki da yake mallakina wai muka shiga, bakin gado muka zauna, tana mai bina da idanu kaman zasu faɗo ƙasa.

Sai kuma na saki kuka mai cin rai, Hafsat ɗin ƙawa ce, aminiya ce gareni.

Bata ce komai ba sai ma sake bina da tayi da idanu.

To ita ai bata ma ga abun kuka ba anan, murna ma ya kamata inyi, Allah ya kawo ranar da muka samu ƴancin mu a cikin gidan.

Sake rungume ni tayi tana mai ɗan bubbuga bayana a hankali alamun lallashi.


"Suhan menene na kuka kuma? ko Auren Umman ne baƙya so."

A hankali na ɗago ina mai kallon ta, sai kuma na shiga ɗaga mata kai, alamun bata tabbacin Abunda ta faɗa.

"Kin jiki? To menene a ciki? Umma fa ba wuce aure tayi ba, kuma bayan haka, Babana Mutum ne da kowacce mace take fata da burin ta samu a matsayin miji, saboda yana da kirki da mutumci matuƙa. To ke menene dalilin da yasa zaki ce bakya son hakan?"

"Hafsat, Hajiya Kubra, Hajiya Kubra ba zata ɗaga mana ƙafa ba, ba zata ƙyale mu ba, ga su Aunty Nihal, da Aunty Saudat. Da cen ma da muke ƴan aiki bata ɗaga mana ƙafa ba sai yanzu da Umma ta aurar mata miji?"

Na faɗa ina mai sake matso wani kwallar daga idanuna.

Ɗan murmushi ta saki tana mai faɗin" Ke da zaki auri yaron nata ma tin yanzu kin fara karaya balle?"

Ɗan zabura nayi ina mai ce mata" Inji wa? Waya faɗa maki?"

" Mama Mana, a bakin ta naji, tin lokacin da su Baba suka je neman auren naki"

Ta faɗa tana mai ƙumshe dariya

Ohh ni Allah, ashe wancen zuwan da su Alhaji Auwalun sukayi a ranar da abun nan ya faru dani wai aure na suka je nema ma ya Ameen?

Ashe Shiyasa yace mani zan aure shi?

Kenan don kada a kirani jin ta bakina ince bana so ne ya sanya shi tara ta da wannan maganar

Gaske fa, ni dama nayi mamaki, ashe ba har cikin zuciyar tashi son nawa yake ba.

Dama wace ni da Ya Ameen??? Ai ni kaina nasan yafi ƙarfina har gaba da abada ma.

Kawai da zancen zucin da nakeyi nayi, ina mai share kwalla ta.

Ɗan duka na kai mata ina mai cewa "Banason haka hafsat, ba don babyn mu ba da sai kinji jiki"


Dariya ta saki iya ƙarfinta, sai kuma tace "Ya naga wai baki fara shiri ba? Haka zaki ci walimar?"

Da mamaki nake kallon ta ina mai cewa "Wace walima kuma?"

"Bakiga baƙi ba? Ƴan uwa ne duk suka zo za'ayi walima yau, ƴan uwan ango Dad"

Ta faɗa cikin zaulaya tana mai kanne mani ido ɗaya.

Hayewa nayi bisa gadon ina mai ce mata "A gama lafiya ƴaƴan ango"

"To ɗiyar amarya" ta faɗa tana mai wucewa gaban akwatina na da suke gefe ajiye.

Jawosu tayi ta shiga buɗewa.

Dudduba komai ta shiga yi, sai cen ta fiddo wani material mai kyau matuƙa ta ajiye ta haɗo harda gyalen da zai iya shiga dashi.

"Kinga kayan da zaki sanya nan please ƙawata, don Allah ki saki ranki, na rana ɗaya ne zamu yi tafiyar mu mu barku"

Kallon ta nake in mai taɓe baki, Ƙala bance mata ba, sai ma juyawa da nayi ina mai kulle idanu na.

Da dai taga alamun rigima nake ji da ita, kuma har cikin raina tsoron auren nan ya kama ni, sai ta miƙe haɗi da ficewa daga ɗakin.

Hajiya Zainab ma kai tsaye ɗakin ummata ta shiga, sai a na biyun ne ta hango ta zaune bakin gado.

Isa tayi suka shiga gaisawa cikin mutunta juna da ƴar firar yaushe gamo,sannan tayi mata Allah yasa Alkhairi ya bada zaman lafiya.

Bata ce ma Umman komai ba akan walimar da za'ayi, domin komai na a hannun ta ne.

Wai Ashe har mai make-up aka kira zata yi ma umman tawa, abun ban dariya.

Hajiya Zainab ce gaba gaba wajen haɗa komai, ƴan aikin dake gidan kaf saida aka kikkira su, kowanne da aikin da yake yi, duk da suma mamaki ya cika ransu fal, gashi sun san Hajiya Kubran bata ƙasar, saidai sun san duk inda take tana bisa hanya.

Canopee ne aka kakkafa manya masu kyau, anyi masu ado sosai, sai kujeru da aka jejjera.

Daga wani eatery aka dinga shigowa da abinciccika suma duk jejjera su aka shiga yi, ƴan kankiya ma har sun zazzauna.

Kowa ya sha kwalliya daidai gwargwado, nima daƙyar Hafsat ta lallaɓa ni na sanya kayan, Amman fuskanta babu wata kwalliya, ko kwalli babu daga mai sai farar powder.

Bamu kai ga fita ba, saidai ance da anyi sallar azahar za'a fara gabatar da walimar cin abincin, kafin a gabatar da Umman wurin ƴan uwa.

Ma'aikatan gidan sai ƴan maganganu suke yi, saidai ba damar a faɗa fili, duk da har yanzu cikin su ba wanda ya san abunda ke faruwa sai mudi ne kawai ya sani, shima da yake ba surutu gareshi ba yaja bakin shi ya tsuke kada aji maganar sarki a bakin shi.

************


Yana tsaka da aiki wayar tashi ta soma ruri, saida ya kai kallo sashen da Bilal yake zaune shima yana latsa laptop.

Sai kuma ya ɗaga yana mai sallama ganin Sunan Mom ɗin nashi yana yawo a bisa screan ɗin, saida gaban shi ya faɗi.

Sallama yayi cikin dakiya da son kauda komai a cikin ranshi kada ta fahimci ko yana da damuwa.

"Son na dawo kazo ka ɗauke mu a airport yanzun nan"

Ta faɗa cikin bashi umurni kai tsaye.

Miƙewa tsaye yayi yana mai tattara wayoyin shi bayan ya kashe wayar.

"Friend akwai matsala"

Ya faɗa cikin wani irin yanayi mai nuna alamun ya kusa sarewa.

Cikin ƙarfafa guiwa Bilal ɗin yake tambayar abokin nashi.

"Mom ce ta dawo yanzun nan, kuma wai ni zanje in ɗauko su in kaisu gida, may be ita da ƙawayen ta ne"

"Toh fa! Menene abun matsalar a ciki? Friend mahaifiyar ka ce fa"

Ya faɗa yana mai ɗan tallafe kanshi da hannuwan shi.

"Anyway, bari inje in gani ko zan samu in dawo da wuri in idasa aikin nan"

Ya faɗa yana mai wucewa cikin salon takun tafiyar shi mai ɗaukar hankali.


Koda ya isa lallai hasashen shi ya zama gaskiya.

4Hajiyas ne cikin shiga ta alfarma sai zuba ƙamshi suke yi, tin daga nesa zaka iya hango isar su da hamshaƙar su.

Cikin murmushi irin na ɗa da uwa ta shiga taka wa tana nufar inda yake doso su kai tsaye.

Ɗan rungume shi ta shiga yi, tana faɗin "I missed you My Lovely Son"

Ɗan murmushi yaƙe ya saki yana faɗin "Mee Too Dear"

Motar suka ɗunguma gabaki ɗayan su bayan ya gaida ƙawayen Mom ɗin nashi.

Cikin Murmushi da ban sha'awa suka shiga amsawa, ko ba komai suna matuƙar alfari da yaron Ƙawar tasu kuma hamshaƙiyar tasu.

Tin da suka doshi gidan gaban shi ke faɗuwa, cikin mamaki take kallon shi, hango motoci da tayi ƙofar gate ɗin gidan nasu, gashi kuma ita batasan abunda akeyi ba, kuma ko da safe sunyi waya da Alhaji Mustaphan Amman bai ce mata ana yin wani abu ba.

Ɗan kallon shi ta shiga yi, alamar son ƙarin bayani.

Janye idanun shi yayi yana mai runtse su, Abunda zai je ya dawo a daidai wannan lokacin yake gudu, ina ma ace yabi shawarar abokin nashi wajen barin garin ma gabaki ɗaya.

A hankali ya shiga gangarawa cikin gidan, bayan mai gadi ya wangale masu gate.

Tsabar mamaki tsantsa ne a kan Fuskokin 4Hajiyas ɗin, tin kafin ya idasa parking Hajiya Kubran ta ɓalle murfin motar ta fito, gyalen ta saman kafaɗa guda ɗaya, sai ƴar mitsitsiyar jikkar dake hannun ta kaman ta wasan yara, da tafka tafkan wayoyin dake hannuwan nata riƙe

Abokan nata ne suka shiga mara mata baya. Kusa da Canopee ɗin taja ta tsaya, tana iya hango ƴan kankiyar a cikin runfar, walima akeyi, abinci ake ci mai rai da lafiya, kowa sai hidimar shi yake yi, duk da sun kula da ƙarasowar ta wurin.

Waiwayawa tayi tana mai kallon Al'ameen ɗin da yake tsaye bakin motar tashi, ya gaza ɗaga ƙafa balle yabar wurin.

Sai kuma ta maida kallon ta kan mutanen da suke cikin rumfar.

Wata kujera mai matuƙar kyau, ruwan gold ce ajiye gefe guda ba kowa a kanta, sai kuma kanta ya ƙara ƙullewa.

Ta rasa wanda zata tambaya, gashi tana son tambayar Amman isa da mulki sun hana ta tambayar.


Hajiya zainab ce kan gaba, sai Goggo Aisha da Goggo Fatima a bayan ta, sun sanya wata mata tsakiya. Tasha ɗanyen leshi mai matuƙar tsadar da tasan kuɗin shi sun haura ma naira dubu ɗari biyar, wara idanu ta kuma yi sosai, daga sashen da Alhajin yace mata nashi ne aka fito da ita, kanta lulluɓe da mayafi mai kyau da walwali.

A bayan ta yara ne guda biyu, ta shaida Hafsat da take cira ƙafa daƙyar, sai kuma gudar da ta kalle ta a fige ba tare da ta shedata ba, saboda hankalin ta ba'a kanta yake ba.

Kai tsaye kujerar da take ajiye suka zaunar da ita.

So take taga fuskar matar, hankalin ta in yayi dubu ya tashi, ƙawayen nata ta maida kallon ta wurin da suke tsaye suma cike da tsabar mamaki.

A hankali ta shiga takawa har gaban matar da aka zaunar bisa kujera, hannun ta duka ta sanya ta ɗage gyalen da yake lulluɓe saman fuskar Umma tawa.

A matuƙar zabure taja baya, har tana shirin faɗuwa.

Wa take gani haka?

Maryama ce zaune bisa kujerar tasha kwalliya har ta gaji, wuyan nan nata cike da ɗanyen gwal ɗinda kuɗin shi saidai a kira miliyoyi, hannayen ta kaf cike suke da awarwaro na gwalagwalai


"Ayuririririririri"

Taji wata mayyar guɗa ta saki guɗa cike da ƙwarewa matuƙa, sai kuma taji an shiga faɗin


"Uwargida ke nan a wurin Alhaji Mustapha Dambulan ɗin, ita ce da kanta ta siyi wankan da Amaryar tata tayi ayau domin faranta ran dangin mijin nata. Ayau Allah ya kawo mu shagalin bikin Amaryar ta Alhaji Mustaphan Farar mace alkyabbar mata, Uwargidan ki na tsaye a gaban ki tazo kawo gaisuwar ban girma da yi maki maraba da shigowar taki gidan nasu da yake cike da ɗumbin wadata da arziƙi haɗi da soyayya da zaman lafiya."

Gabaki ɗaya muka waiwaya domin ganin wacece wannan zabiyar haka?

Wata mata ce tafe jikin nata sanye da atamfa mai matsakaicin kuɗi, da gani dai zabiyar ce da gaske, to ko wa ma ya gayyato ta kuma? Oho!

Hajiya Sa'a ce ta matsa haɗi da kamo hannun Hajiya Kubran da ta tabbatas tayi mutuwar tsaye ne, idanun ta sun firfito kaman zasu faɗo ƙasa, ita kuwa umman tawa murmusawa kawai takeyi cikin ƴar kwalliyr da akayi mata Light mai ban sha'awa, ashe haka Umman tawa take da kyau masha Allah.

Bata da zaɓi illa ɗaga ƙafa ta shiga bin abokiyar tata, ƙafafun ta har suna harɗewa, to sanin da kowa yayi akan halin hajiya Kubran ne ya sanya basu kawo komai ba, sun ɗauka isar tata ce ta motsa, kuma gashi babu wanda tayi ma magana.


Ya Ameen da yake gefe, nannauyar ajiyar zuciya ya saki, yana mai kai idanun shi bisa fuska ta da take tar babu ko ɗigon kwalliya bisa, hakan ne yasanya haskena ƙara fitowa, da idanuna suka yi ɗan ja saboda kukan da nayi gashi kuma babu kwalli a jikin su ko ɗis.

Kallona yayi na tsawon Second goma, sai kuma ya ɗaga ƙafa cikin sauri ya nufi sashen nashi, yana mai ɗan sauke ajiyar zuciya ganin Mom ɗin tashi bata saida hali ba.

*************


Suna shiga sashen nata, ta fizge hannun ta daga na Hajiya Sa'ar, sai kuma ta shiga kai komo.

Cikin wani irin yanayi na tsantsar ɓacin rai, zuciyar ta kaman zata tsago ƙirjin ta ta fito, ga wani irin ja da farar fuskar tata tayi.

Kai komo ta shiga yi cikin falon da ya wadatu da kayan alatu.

"Ni?? Ni?? Ni???"

"Ni Alhaji zaiyi ma haka? Ni Alhaji zai cima amana? Ya rasa wadda zai aura sai ƴar aikin gida na tsawon lokaci? Ƴar aikin ma wadda nafi tsana a rayuwa ta? Ƴar aikin ma marar galihu da asali irin Maryama?"

"Niiiiiiiiii???"


Ta faɗa tana mai zama bisa kujera ta shiga dafe kanta, sai kuma ta miƙe ta wawuro wayar ta ta shiga danna kira.


"Hello Saudat, kinji Abunda mahaifin ku yayi? Aure yayi, kuma ma wannan shegiyar ƴar aikin marasa asali, Eh ki kira Nihal yanzun nan kuzo ku same ni a gida"

Sai kuma ta kashe wayar tana mai danna ma Ya Ameen kira.

Gabaki ɗaya ta fita kamannin ta da hayyacinnta, lallai ma Alhaji ya zubar mata da ajin da mata dayawa suke ganin ta dashi.

Yana ganin kiran nata ya kasa ɗauka, ya san abunda zai faru, zama yayi yana mai dafe kanshi da dukkanin hannuwan shi da yake jin kaman zai tsage mashi.

Hajiya Laila ce ta amshe wayar a hannun ta

"Hajiya Kubra ki tsaya muyi magana, ki zauna mu nemi mafita"


A zafafe Hajiya Kubran ke kallon ta, sai kuma ta shiga cewa

"Duk laifin kune Laila, ku kuka ja mani, wane irin kuɗi ne ban ba ku ba akan a ɓatar dasu a cikin ƙasar nan? Kuma kun mani albishir ɗin sun tafi kenan? Ta yaya zasu dawo mani cikin gida, kuma ma wai a matsayin matar gida? Kunci amana ta Laila da Sa'a kunci amana ta bazan taɓa iya ɗaga maku ƙafa ba har abada"

Ta faɗa cike da hargagi tana mai watsar da tukwanen plowers ɗin dake ajiye bisa wata pula gefen falon.

Kaman zata yi hauka haka take ji, ta watsar da gyalen da jikka harda wayo yin nata, abun kunya ne a wurin ta ace kaman ta mijin ta ya auri ƴar aikin ta.

Hajiya Sa'ar ce zata fara magana ta shiga dakatar da ita.... "Kiyi mani shiru Sa'a, har maci amana ma irin ku zaku iya bani uzirin ku? Amman nasan mai laifi, ba kowa keda Laifi ba asai Al'ameen, shine ya fara bijiro da maganar Aure a gidan nan, zai zo ya iske ni, sai na ci mashi mutumci wallahi zai tadda ni.



Mai gadi ne ya shiga buɗe gate ɗin gidan, a guje motar ta shigo haɗi dayin

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login