Showing 18001 words to 21000 words out of 247770 words

Chapter 7 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10399

ku" "Toh Talatu" Ummana ta amsa mata.

Kai tsaye falon muka shiga tare da sallama, waeh Aljannar duniya kenan, tsayawa fasalta kyaun falon da dukiyar da aka narkar ma ɓata lokaci ne, kawai ka fasalta shi da duk falo mafi kyawo da ka taɓa gani a Rayuwar ka. Zaune take, hakimce cikin isa, izza da taƙama (Hajiya Kubra ba dai ji da kai ba) ko amsa mana sallamar da muka yi bata yi ba, sai ma cen gefe ɗan nesa da tayi mana nuni saman carpet din da ya lashe fin rabin falon tayi, bamuyi ƙasa a guiwa ba muka zauna, muna mai gaisheta cikin ƙan-ƙan da kai, shima bata amsa ba, sai ma shiru da ya biyo bayan hakan na tsawon wucin gadi, sannan ta nisa cike da gadara ta fara faɗin "ina so ku nisanci ɗiyata Afnan, domin duk abubuwan da suke faruwa cikin gidan nan tin zuwanta a kunne na suke, na hana ta taƙi bari, ina so ku sa ta tayi nesa daku, domin ko alama bana son zuwa sashen masu aikin nan da take yi, kuma na san ɗiyarki ke janta" ta faɗa tana maida duban ta kan umma ta da kanta ke sunkuye, sannan ta cigaba "kunsan ko alama ba da son raina kuke zaune a gidan nan ba, saboda har yanzu kin ƙi ki faɗa mana asalin daga inda kuke, daga ke har ɗiyar taki bamu san asalin ku ba, sannan ki shirya bayyana mana komai da ya shafe ku idan ba haka ba, ba jin zaman ku a gidan nan zai cigaba da ɗorewa, bazan lamunci a mallake man ƴaƴa ba idan kunne yaji...... " ta ƙarashe tana mai ajiye maganar cike da gadara, ko ɗar bata ji ba, duk cin mutumcin da tayi mana bata gani ba, wannan ai tozarci ne, ko ba'a faɗa ba, na san mama Talatu da uwani ne suka kawo wannan gulmar, watau ita dai duniya haka take kana barci ana maka mun shari, idan da sabo ma mun saba jin ire-iren wannan tozarci daga gurin Hajiya kubran, muryar Hajiyan ce ta katse man tinanin da na Lula "Kuna iya tafiya Maryama, Amman kada ki manta da buƙata ta a gare ki"

Cikin mutuwar jiki muka taso muka fito, tabbas idan raina yayi dubu ya ɓaci, a bakin ƙofa muka haɗu da afnan ɗin, tana yi man magana amman ni Sam hankali na ma baya kanta, murmushi kawai nayi mata na raɓa ta na wuce, juyowa tayi da niyyar binmu, na sanya hannu na dakatar da ita gami da girgiza mata kai, sannan na sanya ƙafa cikin sauri na bi umma ta da har ta kusa ficewa a babban falon.

Wucewa Afnan ɗin tayi zuwa cikin falon Hajiyan, tare da zama cikin tashin hankali don ta san halin mom ɗin tata sarai "Mom me kika yi masu? For God sake me kika faɗa masu?" ta faɗa kaman zata yi kuka, "ke dallah saka rai shashasha, me kika gani jikin waɗancen faƙiran da har kika liƙe masu, har kina ɗaukarta kuje siyayya tare? Su fa ƴan aikin mu ne, ko kusa ba tsararki bace, bata da wani amfani wajenn mu in ba tayi mana aiki ba mu biya ta, ko kaya sai mun sanya mun cire sana muke basu su sanya, Amman wai kece yau kike haɗa kanki dasu, har kike zuwa ɗakinsu ki zauna, to ahir ɗinki wlh in ba haka ba zan saɓa maki fiye da tinaninki wallahi" ta ƙarashe tana mai nuna zallan ɓacin ranta ga autar tata "mom, ni fa banfisu da komai ba, in fact ma, babu Wanda yafi wani wurin Allah sai wanda yafi tsoron shi, so ni gaskiya momy baki kyauta mani ba, ai su ɗin ma ƴan adam ne, wanda ya halicce mu ya bamu, suma shi ya halicce su, kuma bai manta dasu ba" ta ƙarashe cikin matsanancin ɓacin rai, domin ga alama mom ɗin tata magana marar daɗi ta faɗa masu, kuma akan ta ne, mom ɗin ce ta amshe da cewa "au haka kika ce? Ashe ba zaki dena ba kenan? Maza ki shirya kayan ki, in kin fita ki kirawo man Nafeesa kuzo ku koma inda kuka fito domin bazan lamunci wannan iskancin naki ba wallahi, kada in saɓa maki"

Fashewa tayi da kuka gami da barin part ɗin ma gaba ɗaya, cikin gudu ta sashen yayan nata, ta tarad dashi dawowar shi kenan daga office, don ko takalma ma bai cire ba, faɗa mashi tayi cikin kuka mai fidda zallan ɓacin rai, cikin tashin hankali ya janyo ta gami da rungume ta ya shiga shafa mata baya, cikin sanyin shi mai haɗe da miskilanci yake faɗin " Is OK Lil, is OK, tell me what is happening ne, me ya same ki? Ina ke maki ciwo?" cikin wani sabon kukan ta zayyana mashi komai dake faruwa da Abunda mom ɗin tasu tayi, zaunar da ita yayi yana mai faɗin "is OK Afnan, kinsan halin mom sarai, no, bai ma kamata ki ɓata ma kanki rai ba hakanan, ko ni da kika ga ina gaya mata gaskiya ba saurarena take yi ba a times, sai muyi mata addu'a insha Allah zata gyara halin ta, kiyi shiru babu inda zaku koma sai hutun ku ya ƙare, Amman ina so kema ki ɗan ja baya da su, saboda kada ki dinga ja masu ɓacin rai wajen mom ɗin, kin gane ko? Gyaɗa mashi kai tayi tana mai faɗin "na gane Yaya, amman wlh maman Suhana ba lafiya gareta ba, ina gudun ɓacin rai ya sanya wani abu ya same ta, gashi na baro Phone ɗita ɗaki balle in kira su na basu haƙuri" ta ƙarashe faɗi tana goge kwalla da ke saman fuskanta kwance shaɓe shaɓe.

Is OK, kwanta nan ki huta,bari in shiga in watsa ruwa, sai in fito mu san abun yi,; ya faɗa mata haka ne don ya san rikicin Afnan, tana iya cewa zata kuma zuwa sashen nasu, kuma shi ba zai so hakan ba, gara ace ta ɗan ja bayan dasu, ta bar mashi komai a hannun shi insha Allah shi zai daidaita komai.


Ni kau muna fita na kama umma ta muka nufi sashen namu, ina kallon mama Talatu murna fal cikin ranta, ga duk kan alamu ma laɓe tayi mana, domin taji Abunda Hajiyan zata faɗa, dama ita ta kai mata gulmar, kuma tayi ta zuzuta Hajiyar tana ƙara ma labarin gishiri, har cewa tayi Afnan ɗin sai ta kai ƙarfe sha biyu a ɗakinmu, kuma wai kuɗi take kashe mana sosai muke yi mata wayau, kuma yanzu na fara jin kaina daidai da su Nihal, saboda irin sutura da afnan ɗin wai ta siyo mun daga cen ƙasar wajen.

Lafiya muka isa ɗaki, duk da umman tawa na ƙoƙarin dannewa, tinda ta lura da kwallar da nake share wa akai, akai, Amman hakan bai hana ta kwantawa ba, ba tare da ta furta ko uffan ba, nima bazan tada maganar ba, saboda maganganu ne marasa daɗin ji, to kenan ma tana nufin ƙilan bama da asalin kenan?, me umma ta ke nufi da ɓoye mana salainmu da take yi? Me hakan ke nufi,?

Ganin ta samu barci ne, ya sanya nima komawa gefen ta na kwanta ƙasa, nayi matashi da katifar tamu, ina fata in ta farka komai ya wuce guri ta, ina fata kada ta tashi da :a in rai, domin kafin ta kwanta saida na ɓalli maganin ta na bata, na ƙudurce a raina zan nisanci Afnan ɗin, ba tare da na bari ta zargi wani abu ba, sai dai don mu tsira da mutumcin mu.


Afnan ɗin ce ta roƙi Yaya Al'ameen ɗin da ya ara mata wayarshi ta kirani, sai kuma ta manta bata riƙe number ɗin wayata ba, dole ta sanya ta haƙura da niyyar in mun haɗu cikin gida zata sake bamu haƙuri dangane da Abunda mom ɗin tata tayi mana.

Ta ɓangaren Hajiya kuwa, ko da ta tuntuɓi Aunty feena da maganar komawa, cewa tayi gaskiya ita ba yanzu ba, duka ma yaushe tazo? Kuma wannan dalilin ma bai kai Abunda za'a ce an koma saboda shi ba, ai tinda an ja kunnen Afnan ɗin shikenan bazata kuma maimaitawa ba,; su kuwa su Aunty saudat da sauran ma'aikatan gidan daɗi suka ji, wai ko ba komai an nesa ta ni da afnan, dama ƙaryar tawa ta Afnan ɗin ce (oh🤔 wai ko ma yaushe Afnan ɗin ta dawo, duka duka?)


Haka Ya Ameen ya ta lallaɓa Lovely sister ɗin tashi har ya samu sukayi kwana uku da faruwa Al'amari, dama Alhaji mustapha yayi tafiya, duk wainar da ake toyawa bai sani ba acikin gidan, wannan ce ta sanya bayan ya dawo Al'ameen ɗin ya kuduri niyyar tunkararshi da maganar karatun suhan ɗin, a ganin shi wannan ce kawai damar da zai yi amfani da ita wajen ceto suhan ɗin da mahaifiyarka a halin taskun da suke ciki.


**********************


Ƙarfe takwas daidai 08:00pm yayi sallama falon abban nashi, tafiya yake cikin salo shi na cikakke ɗa namiji, duk da yana da sanyi, wannan ce ta ƙara ƙawata tafiyar tashi, murmushi Alhaji mustaphan ke bi shi dashi, har ya ƙara so ya zauna kujerar dake kallon ta Alhaji mustaphan.

Ɗan sunkuyar da kai yayi alamar girmamawa tare da faɗin "ABBA barka da dare" miƙa mashi hannu Alhajin yayi suka yi musabaha, "barka ka dai Son, ya aiki ya jama'a?" Abban ya faɗa fuskar shi cike da annashuwa, "Lafiya ƙalau Abba , an dawo lafiya.?? " ya faɗa cikin girmamawa, "Lafiya ƙalau Son, ina fata dai lafiya? Al'ameen ɗin ne ya amsa da" Lafiya lau Abba, wata magana ce nazo muyi idan ka da lokaci". "To to to, bismilla ina jinka Al'ameen ince dai ko lafiya ko?" Alhajin ya faɗa cikin dattako, lokaci daya yana mai ajiye kofin coffe da yake sha a hankali, ya tattara duk kan natsuwarshi ya ɗora ta kan mafi soyuwa daga cikin ƴaƴan shi.


Natsuwa Ya Ameen ɗin yayi tare da warware mashi komai da ake ciki, dangane da karatun suhan ɗin, sai dai bai faɗi Abunda mahaifiyarshi tayi ba, sannan ya ɗora da faɗin "Abba kuma ina so asamu wasu masu aikin da zasu mayi gurbin su, Kaga dai ita maman yarinyar ba cikakkar lafiya gareta ba, kowa kuma ya sani, sannan idan Allah yayi ita kuma Suhana makaranta zata tafi, Kaga akwai nbuƙatar wasu madadin su, sannan bana so mom ta san da hannuna ko na Afnan a ciki, ka shige mana gaba wajen ganin ka daidaita komai wajen hajiya"


Murmushi Alhaji mustaphan yayi irin nasu na manya, sannan ya ɗora da faɗa ya aka yi ba'a faɗa mashi hakan ba tun farko? Ai da yanzu ma yarinyar tayi nisa a karatu, ko ma ya tura ta cen wajen Aunty feena tayi karatun ita da Afnan ɗin, Amman ko yanzu babu matsala, babu Abunda zai gagara da izinin Allah, wasu ma an temakesu balle waɗan da suke ƙarƙashin su?, shi ɗa ai na kowa ne, kuma baka san mai amfanar ka ba nan gaba.

"Babu komai Al'ameen, ka bar maganar a hannuna insha Allah da kaina zan samu ita mahaifiyarka tata, zan kuma roƙe ta wannan alfarmar in har na isa tayi man" Alhajin ya faɗa cikin son ƙarfafa ma Al'ameen ɗin guiwa ga temakon da yake son yayi, ko bayan ba ranshi, shi ya san ya bar wanda Al'umma zasu amfana dashi, ya san ya bar ma dadi, ko ma yace mafi yi, domin Al'ameen ɗin yaro ne irin wanda kowanne uba yake da burin ace ya mallake shi, a matsayin magaji.

Cikin jin daɗi da godiya yayi ma Abban nashi sallama gami da cewa "bari in barka haka nan Abba, ka huta na san ka gaji, a tashi lafiya, sai da safe" ya faɗa yana Miƙewa da niyyar barin ɗakin, da kallo Alhaji mustaphan ya bishi yana ƙissima wani al'amari da zai faru nan gaba ƙaɗan akan ɗanɗan nashi mai girma, tabbas yana da buri da fatan hasashen nashi ya zamo gaskiya. Murmushi yayi yana mai janyo kofin coffe ɗinshi ya cigaba da kurɓa cikin dattako gami da faɗin
"Allah shi kaimu Son"


_Toh fa Fans, magana ta girmama, lamarin ya kai kotun ƙoli, ko ta yaya Alhajin zai yi domin shawo kan maman Suhana?, Kudai kuci gaba da bin Alƙalamin Oum Deedat domin ta warware maku zare har abawa_



_~Oum-Deedat ce~_
[8/5, 8:23 PM] Aminatu Hassan: 🌹 *_BAN FI ƙARFINTA BA_*🌹

🌺🌺🌺🌺🌺

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u nopain✍🏽~*

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._

*Fans ina jin daɗin comment ɗinku, hakan na ƙara man ƙwarin guiwa, nagode akafta*


_*Page ~10~*_

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°


Takowa ya cigaba da yi a hankali cikin salon tafiyar shi ta ingarman namiji, daf dani ya sunkuyo ta yadda zan iya jiyo shi, sannan ya shiga faɗin "pray for your mom, yanzu ba kukan ki take buƙata ba, sannan ki tashi daga wajen ki koma bisa chair kin tare hanya, wani zai iya bugeki" Abunda ya faɗa kenan a gaggauce ya koma inda yake zaune ya sake zama.

A hankali na tashi ina mai haɗa hanya cikin jin juwa da ke neman yin haji-jiya dani, kujerar dake kallon tashi na zauna tare da juyar da kaina daga saitin shi, ta yadda ba ma zamu iya haɗa idanu ba.

Akai Akai yake ɗaga idanu yana kallon kyakkyawa agogon dake hannun shi samfurin Apple, sai kuma kiran da akeyi mashi Akai Akai yana latse wa. Ƙarar buɗe ƙofa ce ta dawo da hankalin mu duka wajen, zabura muka yi mu duka biyun wanda a tare muka isa ga likitan da ya fito daga cikin ward ɗin "likita umma ta ta farfaɗo? Kaddai kace man ta mutu dan Allah" na faɗa ina mai matso wani sabon kwallar, "ummanki lafiya lau ta farfaɗo amman mun yi mata allurar barci saboda ta sake samun hutu, zaki iya shiga ki ganta nan da anjima idan ta farka" ya faɗa man yana mai maida hankalin shi kan yaya ameen ɗin da yake tsaye ta gefen mu, "a'ah yallaɓai ashe baka shiga office ɗin ba? Sai ka zauna waje?" dan guntun murmushi yayi sannan yace ma Ya Ameen ɗin "to muje sai in maka ƙarfin bayani ko" ya wuce gaba Ya Ameen ɗin ya bishi a baya, da idanu na raka su har suka shige office ɗin sannan na sauke ajiyar zuciya lokaci guda ina mai hamdala gami da sanya hijab ɗina na share dukkan ƙwallar dake kan fuskata, muskutawa nayi sannan na maida duba na kan mama Talatu dake tsaye tana binmu da kallo da kuma naɗe dukkanin motsin mu cikin fai-fain ta na gulma, ɗan taɓe baki nayi kaɗan ina mai rayawa a cikin raina "dukkan ku zaku gama ne, zaku gaji ku bari, ai Hajiya Kubra ba'a mata gwaninta.


***************

Likita ne ya zauna a kujerar sa gami da nuna ma Al'ameen ɗin kujerar zaman patient," Bismillah yallaɓai ga wuri zauna" bayan ya Ameen ɗin ya zauna ne sannan ya muƙa mashi hannu suka sake yin musabaha gami da ƴan gaishe gaishe, dama sun san juna don shine family doctor ɗinsu, kuma a asibitin ne suke da file, Dr. Ashafa kenan kwararren likita ta kowanne fanni.

"Yallaɓai garin yaya haka kuka bar matar nan cikin irin wannan hali? Abun yayi tsanani, zuciyar ta ta kusa ta buga, ta daɗe da ciwon zuciya duk da bincike ya nuna tana kan drugs, sai dai ba wasu masu ƙarfi bane, ba zasu yi tasirin hana zuciyar kumbura ba, gaskiya ba dan kunyi gaggawar kawo ta nan ba da abun ya munana, a dinga kulawa pls" ya sauke maganar tare da ɗora dukkanin idanun shi da natsuwarshi akan Al'ameen ɗin don jin amsar da zai bashi.

"Dr wallahi ban san abun yayi worse haka ba, ban ma san wane asibiti suke zuwa ba, na dai san bata da lafiya Amman ban san me ke faruwa da ita ba, yanzu ya jikin nata? Ba zamu iya ganin ta yanzu ba, ina da uzuri ne tin ɗazu ma ake kira na" ya sauke maganar da gani dai cikin hanzari yake don ya ƙagara ya tafi "No babu wani damuwa yanzu mun shawo kan matsalar, sai dai gaskiya a kula, a dena yawan ɓata mata rai, in da hali ma adena bari tana aiki mai yawa da zai iya gajiyar da ita, yanzu ma zaku iya shiga ku ganta, sai dai zaku barta anan ne, ka san tsari asibitin ba'a zaman jinya" ya faɗa yana mai sake miƙa ma Al'ameen ɗin hannu dan musabaha, shima Al'ameen miƙa mashi yayi yana faɗin "Nagode Dr. Ashafa, sai dai alfarma zakuyi mana wannan karon, ita wannan yarinyar ɗiyarta ce, so ko mun koma da ita zata tashi hankalin ta ne, zata damemu da kuka, ku barta ta zauna wajen ta har muga yanda jikin zai yi, ni zan je, idan na taso daga office zan dawo inga yana yin jikin ko da Abunda ake buƙata" "OK shikenan yallaɓai" likitan ya faɗa, sannan suka juyo a tare suka fito domin shiga ɗakin da umman tawa take; ya ameen ɗin ne ya tsaya yana faɗa mana mu shiga muga jikin ta har da mama talatun domin ita zata koma ne gida.

A tare muka shiga ɗakin da shi da mama talatun, likitan ne yake shaida mana banda hayaniya, kada kuma a tada ta har sai dai ita ce ta tashi dan kanta, kuma kada a bata komai taci, akwai sinadari abinci da ake bata ta iskar oxygen ɗin da yake maƙale a hancin ta.

Duk iya rashin imanin mutum sai ya tausaya wa umma ta, kwance take tayi fayau da ita, numfashi take sauke wa a hankali, babu Abunda ke motsi jikin ta, jawo kujera nayi ta roba mai kyau na zauna yayin da na ƙure

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login