Showing 51001 words to 54000 words out of 247770 words
haba U-Boy, ashe da mun ci ubanmu, yanda na san gayen cen baya da wasa ko alama, yana iya Sanyawa a kulle mu fa wallahi, baya son rashin kunya" "Muje Baba, Allah ya so mu ba gaban sauran guys ɗin aka yi ba, ai da mun sha kunya" Adnan ɗin ya faɗa yana mai jan hannun su suka cigaba da tafiya domin barin makarantar
***************
Muna isa gidan ya sauke ni baƙin gate, bai ceman ƙala ba, haka nima ban tanka mashi ba, na Miƙa mashi hanky ɗinshi, ɗaga man hannu kawai yayi alamar in bar shi, fita nayi na kulle motar, gami da ɗan ja baya, ina jiran ya miƙo mani wayar, motar shi ya ja ya wuce ba tare da ya ko kalle ni ba, jiki a saɓuke na shige gidan zuciya ta a cunkushe, har saida umma ta fahimta
Aiko ta shiga tambaya ta lafiya? Ko Jarabawar ce tayi wahala? Girgiza mata kai nayi, ina mai ƙaƙalo murmushi dole nace "a'a umma, Jarabawa Alhamdulillah, kawai gajiya nayi, gashi kaina yana ɗan ciwo, kinsan na kwana karatu jiya ban samu isasshen barci ba" cikin tausaya wa ta shiga ɗan ɗaga man kai alamar eh, sannan ta shiga cewa "to maza kiyi wanka da sallah, kici abinci ki kwanta ki huta, ai an daɗe ba'a gamu da karatun ba, dama sai a hankali" da to na bita ina mai kwaɓe kayan na shiga ban ɗaki domin yin wanka.
Sai da na kammala komai, sannan na shiga cin kafiyayyen abincin da umma ta girka mana, duk da zuciya ta babu daɗi akwai tinanin da nake son yi nafi so sai na natsu, gashi waya ta dake hannun Ya Ameen ɗin, naso in kira Afnan domin jin me take nifi da kalama ta na ɗazu? Saidai wata zuciyar tana mai ƙwaɓa ta, gami da tunatas da dani shirme da shiriritar afnan ɗin lokutta da dama.
Da haka bacci ya kwashe ni, bayan gama yabiɗar abincin, dama da tarin gajiya fal acikin a jikina.
~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:37 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
*Page ~19~*
*Gaisuwa da ɗaukacin marubutan Golden Pen Writer s Association, Ina matuƙar yinku a ko ina kuke, kuci gaba da rubuta mana litattafai masu ma'ana, mu kuma muna suburbuɗa karatu Insha Allah, Allah ya ƙara maku ɗaukaka da zaƙin hannu. _Love u All_*
*kyautar Page gareki _Khadeeja s. Dogarai (Lipton Girl)_ shafinki ne wannan kiyi kaca-kaca da ɗan Albarka, abu naka maganin a kwaɓe ka* 🤷🏻♀
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Bacci yayi daɗi, nice ban tashi ba sai da kiran sallar la'asar ya tada ni. A gurguje na sake watsa ruwa domin in ƙara jin daɗin jiki na, na maida komai na adana daya danganci karatu na.
Mamaki nake yanda umma tayi mana girki a cikin ɗaki nake, kasancewar umma ta mace mai tsafta da kula, ya sanya bama a gane anyi girki a wajen har ta kauda ɗan ƙaramin gas cylinder ɗin da na siyo mana, aka ciko ta da gas, saboda stove akwai ɓata wuri, ga warin kerosine.
Wuraren ƙarfe biyar na yamma ne, abun duniya ya isheni, ina son waya ta a kusa dani, gashi abinda yaran nan suka mani ɗazu a makaranta ya tsaya mani a rai, ai duk shi ya ja mani da ya bar mani hijab ɗita a mutumce ba ɗan iskan yaron da yaso ma tunkara ta.
Naji mutum da ƙarfin hali, wai har cewa yake ina cen ina shiririta na kusa makara, ko sau nawa ma na kira shi bai ɗaga ba? 😡😏
Shashantar da zancen nayi, gami da miƙewa na janyo kayan guga ta da ban ƙarasa ba jiya na hau idasa wa.
*******************
Ya daɗe office zaune yana jujjuya wayar a hannu, ƙare mata kallo yake tsaf, shi dariya ma abun yake bashi, lallai mace sai dai a barta, bai ga abun kuka ba anan, ita bata san ma kukan da take masu zai ƙara masu ƙaimi wajen Abunda suke shirin aikata mata ba? Tin farkon biyo ta da sukayi yake kallon su ta cikin mota, har kawo inda ɗaya ya janyo mata ƴar hijab ɗin dake saman kanta, baiyi niyyar fita ba, Amman kasancewar hangowa da yayi abun nasu na neman wuce makaɗi har ta kai ga sun janyo mata jikka ta katse, shi ya tunzura shi ya fito a sukwane zuwa gare su, yayi niyyar hukunta su, sai kuma ya fasa ganin cewa zai iya ja mata, wata rana ko a hanya suka haɗu da ita su so su rama abinda ta sanya aka yi masu, hakan ce ta sanya bai ko tanka masu ba lokacin da ya isa wurin.
Hannun shi ya ɗaga gami da kallo, cen ƙasa zuciyar shi na raya mashi, me yasa ya kama mata hannu? Har da goge mata kwallar dake zirara saman fuskar ta? Me hakan ke nufi? Shi dai ya san in afnan ce ba zai iya bari yana kallo a so aci mata mutumci ba, ba zai iya jura ba, ita kuwa suhan ɗin yana mata kallon kamar afnan ne, ko don saboda tsananin ƙaunar afnan ɗin ga suhan ɗin.
"Sai dai kada ka manta, ita ɗin ba afnan bace, ba muharrama ka bace"
Abunda wani sashe na zuciyar shi yake tinano mashi kenan, ɗan murmushi ya saki yana mai girgiza kanshi irin na gamsuwa.
Murmushi ya sake saki har saida kuma tun shi gabaɗaya suka loɓa, tinowa da yayi da hajiyar shi ƴar drammer, da yanda ya rufe mata baki d damun shi da zancen aure da take yi, nisa wa yayi gami da jawo wayar shi, ya kamata ma ace sun dawo hakanan, gidan baya mashi daɗi ya kasance babu kowa daga shi, sai masu aiki, Alhaji nasu ma baya ƙasar duk da shima gaf yake da dawowa ko don hidimar bikin su Nihal ɗin.
Kira biyu yayi Alhajin ya ɗauka yana dariya "Yaya dai Son? Kwana biyu kajini shiru ko?"
Murmushi ya saki yana mai cewa "Nothing Dad, good afternoon, Ya aiki?"
"Aiki Alhamdulillahi Ameenullah, ya fama da jama'a? Fatan dai komai yana tafiya normal?" Amsa mashi yayi suka ɗan taɓa fira haka mafi yawanci da ya danganci aiki ne, yana kuma sanar dashi shirye shiryen kammala ginin gidajen nashi, da yanda za'a shirya ƙaddamar dashi, Alhajin ne yace su bari tukunna su gama da hidimar bikin su Saudat ɗin, saboda kada ayyuka su rincaɓe masu, ba haka yaso ba, yaso ya cigaba da shirye shiryen shi, hidimar biki ai ba tashi bace shi da yake namiji, kuma ba bikin shi ba ko na abokin shi Bilal, da to ya amsa ma Dad ɗin nashi, sannan ya sa yo buƙatar shi ta son Alhajin yayi ma Hajiyar tashi magana su dawo gida hakanan, duk abinda basu gama siya ba, akwai a gida nigeria, shi bai ga dalilin da za'a ce siyayyar kayan gida ba, sai an kwasa zuwa wata uwa duniya, murmushi Alhaji Mustaphan yayi, ko ba komai ya san yaron nashi wajen kishin ƙasar tashi ta nigeria, amsa mashi yayi da zai kira su ya sanar dasu, sallama sukayi suna mai marmari da begen juna, ƙauna ce mura ran mai tsafta Alhajin yake ma yaron nashi, ko dan kafin hankali da zurfi tinani irin na ɗanɗan nashi, duk ayyukan dake gaban shi, baya taɓa gajiyawa, ko ya nuna ya sare, balle ya gaza, addu'a yaci gaba da bin yaron nashi, Allah ya cigaba da taimaka mashi da haskaka mashi a dukkan al'amurran da ya sanya a gaba.
***********************
Ko da Alhajin ya kira su akan su koma gidan, a cen ƙasa ran Hajiya Kubran ba haka taso ba, saidai isa da izza ba zasu bari ta bari ta nuna ba har ma waɗanda suke tare su gane, watau su Hajiya Laila, da kuma wata ƙawar ta makusanciya watau Hajiya sa'a, dama su shidda ne sukayi tafiyar sai sabuwa ƴar aikin da suka samu itama yarinya ce duk da zata ɗara ma Saudat kanta a shekaru, idanun ta a buɗe yake, dama bata aiki sai gidan masu hali, ga iya tuggu da munafunci, wannan ce ta sanya ta ƙara shisshigi ma hajiyar, duk da tana jin haushin mulki irin na hajiyar, su bakwai kenan, Hajiya Kubra, Hajiya Laila, Hajiya sa'a sai Nihal da Saudat sai hafsat ɗiyar Alhaji Awwalu da za'a haɗa bikin nata da su Nihal ɗin sai kuma sabuwar ƴar aikin tasu mai suna Maria, ana ce mata Maree.
Ko da Hajiyar ta faɗa masu batun komawa tasu, basu ji daɗi ba matuƙa, kumburi suka shiga yi, harda cewa zasu kira Dad ɗin nasu su roƙeshi ya ƙara masu sati, Hajiya Kubran ce ta hana su, saboda mulki da taƙama na kai kawo acikin jinin jikin ta, kuma bata isa saɓa ma Alhajin ba, saboda shi ɗin namiji ne tsayayye a gidan shi, baya ɗaukar wargi ko saɓa dokar da ya gindaya akan kowa dake zaune a gidan.
Ta ɓangaren Hafsat kuwa abun yafi kowa faranta mata rai, cikin zuciyar ta dama ta ƙagara su koma ƙasar tata ta haihuwa, ta samu ta koma gidan su cen Katsina, dama abban ta ne ya tilasta mata zuwa, ko mahaifiya ta ba don taso ba, saboda ta san yanda family ɗin na ƙanen mijin nata suke da bala'i jin kai da sangarta, uwa uba kuma mahaifiya su da dama ba wani shirin arziƙi suke ba, domin ita ba zata iya binta ba, a matsayi ta na wadda take gaba da ita, ko ba komai daga ita har mijin nata basa jiran komai daga garesu, don dai ma kawai ƴan uwantaka, da kuma shi Alhaji Mustaphan da ba halin shi ɗaya ba Sam da matar tashi.
Ware ta suke yi, komai za'a siya ko za'a zaɓa ra'ayin su ake ɗauka, ba kuma komai bane in an siya masu ake siya mata ba, to don dai itama mahaifiya tata tayi ƙoƙari wajen ganin ta haɗo ta da ƴan kuɗaɗe daidai ƙarfin ta, gudun faruwa hakan, Hafsat yarinya ce mai natsuwa da kawaici, hakan ce ta sanya ko sunyi waya da mahaifiyar tata bata faɗa mata komai da halin da take ciki, ta riga da ta san Allah ya bata miji da gari, mai natsuwa na nuna ma sa'a, ita ba wannan abun duniyar ne yake gabanta ba, fatan ta dai kawai ɗaya ta koma ƙasar tata ta haihuwa, ko zata ga mahaifiyar ta mai share mata ku kanta, tana kewarta sosai, dan wanda zata aura bata jin shi, saboda kullum suna tare a waya ko kuma we-chat.
Saboda haka yanda suke ware ta ko kuma suke nuna mata halin ko in kula bai dameta ba, duk da abun na mata ciwo, wai ace waɗannan ƴan uwanka ne, Amman babu wata alaƙar arziƙi da zata haɗa ka dasu, kai su dai waɗannan ba suyi da cen hali ba, nazajen su sun kwasar ma kansu, yara babu abinda suka sani daga sangarta sai jin kai? Ta lura ita kanta ƴar aikin tasu Maree munafuka ce, bata cen bata cen, wannan ce tasa ta ja jikin ta bata sake masu sosai su kansu, balle su wulaƙanta ta, duk da ta san maƙudan kuɗi Alhajin ya haɗo su dasu, kuma Yayansu Al'ameen na sake turo masu wasu akai akai, hakan bai sanya mata kwaɗayin abun su ba Sam, kuma shi Alhajin da sunan siyayyar yara uku yake bada komai, har shi Al'ameen ɗin yana sake haddada masu duk da Abunda suka siya su siyawa Hafsat itama, Amman basa ji daga su har mahaifiyar tasu, da ta kwaso ƴan barandanta saboda kankan a suka wani taho siyayyar aure.
************
Cikin kwana na biyun da basu umarni sai gasu sun tarkato sun dawo dukan su da tarin siyayya raga raga, tare suka taho da kayansu, hayaniya ƴan taron su ne ya alamta mana da dawowar tasu, ba zance bamuji daɗi ba, saidai lallai gabanmu ya faɗi, daga ni har umman tawa.
Jiki ba kwari muka fito taron su muma, gefe mukaja muka tsaya gami da gaishe su, cikin su ba wadda ta amsa mana, sai a tsaki da Saudat tayi ta shige war ta cikin gida, Hajiya Laila ce naga tana mani wani irin kallo da na Gaza gane ma'anar shi, ita kau Hajiya Kubran ko kallo bamu isheta ba, Hafsat ce kawai ta matso inda muke tsaye cikin girmamawa ta gaida umma ta, cikin fara'a ta amsa tana mai tambayar ta Mamanta, Lafiyarsu lau ta tabbatar mata, sannan ta janyo hannuna da nake tsaye gefe guda cikin zaulaya tace "Ƴan mata ya ake ciki?" murmushi nayi ina jan hannun ta zuwa gefe, na shiga cewa "ke Hafsat zakiyi laifi fa, ki bari zamuyi magana anjima" da to ta bini, tana mai matsawa gefe, hakan ce ta sanya ta ƙara basu haushi, bata ko kula su ba ta shige cikin gidan.
Bamu bar wajen ba muna tsaye har saida suka shige cikin gidan, sauran ma'aikatan duk suka watse suka barnu nan tsaye, umma ta ce ta matso inda nake tsaye ta shiga kallo na cikin gargaɗi, "Ki kula suhan, kar ki ja mana wani abu daban, kinga dai yadda suka dawo, tin anan ya alamta maki yanda abun yake, ki kiyaye" gyaɗa mata kai na shiga yi cikin gamsuwa da maganar ta, wucewa tayi gaba Ina binta laƙwai-laƙwai har zuwa sashe namu.
***************
Al'ameen da yake tsaye ta jikin window ɗinshi, yana kallon duk abubuwan dake faruwa, tin daga shigowar shi gidan har watsewar su, ya sauke ajiyar zuciya, lallai Abunda yake gudun afkuwar shi ne yake faruwa, tsanar mutanen guda biyu ce yake hange cikin kayar idanun mahaifiyar da ƴan uwa nashi.
Tabbas ya san shine ya jaza masu, ba tare da sanin su ba, ta yaya zai bi ya warware wannan tsanar da suke fuskanta? Laifin shi ne, ina ma ace da wata yayi wannan trap ɗin ba suhana ɗin ba, "Huh" ya sauke ajiyar zuciya cikin sanyin jiki ya ja ƙafafu shi daƙyal ya isa ga bakin gadon ya zauna yana mai dafe kanshi cikin matsananci yar damuwa, menene ya sanya yanzu yake yawan kula da al'amarin yarinya ne? Menene ya sanya yanzu tinanin ta baya fita a ranshi? Hannu ya sanya gami da jawo wata farar leda, fiddo Abunda yake ciki yayi ya shiga juyawa a hannun shi, waya ce mai masifar kyau, sabuwa dal a kwalin ta, ƙirar Samsung galaxy.
Tunani yake ta yanda wayar zata isar mata ba tare da kowa ya fahimta ba yanzu, tinda ƴan gidan sun dawo, su kansu munafuka masu aikin yanzu zasu dinga kai komo acikin gidan, wani tinani ne ya faɗo mashi arai, maida wayar yayi cikin ledar ya miƙe gami da aza ta bisa mirror ɗin da yake ɗakin ya fice domin zuwa yi ma Mom ɗin tashi barka da zuw.
A babban falo dukan su ya tada su, sun baje gajiya tayi masu ligif, Hajiya Kubra ce kawai bata wajen ita da aminan nata, suna cen sun ƙule a sashe na Hajiyar suna tattauna wa, gaida shi suka shiga yi, ya amsa masu babu yabo babu fallasa, sannan ya maida hankalin shi akan Hafsat ɗin da take jingine da kujera saman carpet, cikin ɗan dakin fuska yace "Hafsat ya gajiyar tafiya, fatan kun dawo lafiya?" ɗan murmushi tayi tana mai cewa "lafiya ƙalau yaya, ya muka same ku?" Lafiya lau ya bata amsa, yana mai nufar upstair domin zuwa ga Mom ɗin tashi.
Ƙwanƙwasa ƙofar ya shiga yi, daga cen ciki aka bashi umarni ya shiga, cikin takun shi na ingarma namiji ya taka ya shiga bakin shi ɗauke da siririya sallama, da kallon ƙauna mahaifiyar tashi ta bishi, ɗan nesa dasu ne ya samu kujera gami da zama, ya shiga gaida su harda ƙawayen mahaifiyar tashi, cikin fara'a suka gaida shi suna tambayar shi wajen aiki, ya amsa masu da lafiya, yana mai tambayar su hanya, duka lafiya suka shaida mashi, miƙewa yayi gami da cewa "Mom zan ɗan fita kafin ki gama dasu, ina dawowa anjima"
Bai jira cewar ta ba, ya fice daga falon, cen ƙasan ranshi, haushi fal na abokan mahaifiyar tashi, domin shi fa in ba zuga ta ba, da ƙara kambama mata kai baiga abinda suke yi ba, baiga dalilin ta ba ma na kwasar su su wani tafi siyayyar aure ba, Abunda ko daga nan gida nigeria zaka iya Kyi order ɗin duk abinda kake so, ya iso maka kuma har gida, salon ɓarnatar da kuɗi kawai, da son neman suna😒
Da kallo suka bishi dukan shi, har ya idasa ficewa a falon, ajiyar zuciya suka shiga sauke wa, sa'ilinbda Hajiya sa'a ta kalli Hajiya Kubra, "Lallai Hajiya ta, Al'ameen ne ya ƙara girma haka? Kina me da har yake neman jawo maki magana da raini, ta hanyar auren waccen koɗaɗɗar? Kiyo iya yin ki duk yanda zakiyi kiga kin daƙile wannan maganar wallahi, yaro mai jini a jiƙa kaman wannan ga naira ga kyau ga gayu? Tabɗi gaskiya kinyi sake, ni ba ma ga amfanin zaman da suke yi a cikin gidan ba, har ma zai dinga iya ganin ta kullum, kiyi amfani da damar ki, tin kafin kina kallon ruwa kwaɗo yazo yayi maki ƙafa, kina dai gani irin waɗannan yaran su ne