Showing 45001 words to 48000 words out of 247770 words
mama uwani ta fito ta bi bayan Suhan ɗin, saidai cikin rashin sa'a ta tadda Al'Ameen ɗin ya fice cikin motar shi, da matsananci gudu yayin da ita kuma suhan ɗin tabi ta gefen titi tna tafiya alamar ma tafiyar tasu bata zo ɗaya ba, tinda su a tinanin su ko Al'Ameen ɗinne zai ɗauki suhan ɗin su tafi tare da ita.
Abinda duk basu sani ba shine, Al'Ameen ɗin dukan su tara su yake yi, lokaci yake jira yazo da dukkan su zai shayar dasu Madarar mamaki.
_Masu karatu kada fa ku manta har yanzu fa a cikin ma'aikatan gidan, babu wanda ya san da maganar auren Suhan ɗin da Al'Ameen ya bijiro da ita, har ita kanta suhan ɗin da umman ta_
~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:36 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
*Page ~17~*
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Tini rahoto ya isa kunnen Hajiya kubra, wannan ne ya sanya ta wakilta mama talatun da ta kai mata tsogumin zuwa ɗakin namu ta duba mata me ke wakana, domin dai ita dakanta ba zata iya taka sashen masu aikin ba.
Cikin sa'a kuwa, ko da ta isa ta tadda umman tawa zaune bakin katifa tana jan carbinta a hankali yayin da idon ta yake kulle haka ta jingina bayan ta da jikin bangon ɗakin, bata yi sallama ba har saida ta isa tsakiyar ɗakin tana mai ƙare ma dukkanin lungu da saƙo dake cikin ɗakin kallo, cikin matuƙar mamaki umman tawa ta buɗe idanun ta tana mai bin mama talatun da kallo wadda har ta samu gefen katifa ta zauna, Amman duk da haka bata bar bin loko loko na ɗakin da kallo ba, ko zata hango wata leda ko wani abu.
"A'a Talatu ce yau a ɗakin namu? Sannu da zuwa" umman tawa ta faɗa cikin ɗan murmushi haka kaɗan a fuskar ta, domin dai ta san me ya kawo mama talatun ɗakin namu
"Eh wallahi kuwa Maryama, nazo duba jikin naki ne, ya ƙarfin jiki?" ta faɗa cikin ɗan ruɗewa kaɗan kama ta da umman tawa tayi tana mata kalle kalle a ɗaki.
"Aikuwa Naji sauƙi sosai Alhamdulillah wallahi Talatu, kinga kaman ba ni ba Naji ƙarfin jiki na, Allah dai ya saka da Alkhairin sa"
Umman tawa ta faɗa tana mai komawa ta jingina da bangon, daga haka ta ja bakin ta ta tsuke, hakan da mama talatun ta fahimta ne ya sanya ta cewa "Madalla Madalla, Allah ya ƙaro afuwa" ta miƙe cikin hanzari zata fice yayin da umman tawa ta bita da ameen tana mai kallon bayan ta, gami da girgiza kai a hankali a hankali
Daidai bakin ƙofa muka haɗu da ita, gaida ta nake yi ma, Amman Sam hankalin ta na ga ƙatuwar ledar da na ciko mana ita taf da siyayyar abinci da zamu ci kafin muyi tinanin mafita.
Har na gitta ta na shige ɗakin tana tsaye tana bin ledar da kallo, domin sanin menene ciki, niko ba ta ita nake yi ba, sanin halin ta da nayi, sai ma na tsinci kaina da baƙin cikin shiga ɗakin namu da tayi, koda yake ba zuwan kanta bane turo ta aka yi.
Jiki a matuƙar sanyaye ta wuce direct zuwa sashen hajiya Kubran ta zauna zaman jiran ta fito, domin taji ba'asin aiken da tayi mata.
Ta ɓangaren mu kuwa ba ma ta ita mukeyi ba, abincin mu muka ci cikin jin daɗi, da sanya ma Ya Ameen albarka, ko babu komai ya zo mana a lokacin da muke buƙatar shi, mu bamu damu da halin mahaifiyar shi ba, ko ma me zata yi ai yunwa bata da hankali.
Ƙarya da gaskiya ta shiga zayyane ma Hajiya Kubran, yayin da ita kuma take zaune hakimce tana sauraren ta, take gyaɗa kai a hankali, lokaci guda ta sallami talatun da take faɗa mata ƙarya da gaskiya gami da kiran hajiya Laila aminiyar ta, kuma maganin kukan ta.
****************
Washegari tin da sassafe sai ga mudi driver ya mana sallama, gami da miƙo man fararen takaddu ƙal dasu, yake shaida man Alhaji ƙarami yace in cike zai aiko shi ya amsa anjima
Amsa nayi gami da mashi godiya, na koma cikin ɗaki fuska ta fal da annashuwa, farin ciki nake yi sosai matuƙa, domin dai ko ba komai na fahimci ya danganci karatu na ne, umma ta na shiga nuna mawa, itama tayi murna sosai, gami da ƙara gode ma Al'ameen ɗin da ya tsaya ma Al'amarin mu kai da fata.
Bamu kaɗai yake ma haka ba, kowa a cikin gidan yana taimaka mashi, muddin abun ya sha kai, domin kwanaki ma sai da ya biya maƙudan kuɗi aka yi ma yarinyar mama saude mai girki aiki, muma cikin gida ne muke ta jin raɗe raɗi, da irin taimakon da yake ma ma'aikatan baya ga albashin su.
Cikewa na shiga yi, da gani dai kaman Jarabawa ce zan rubuta watau Jamb, inda naga ban gane ba sai in tsallake, a haka har na gama na maida cikin folder ɗin na ajiye jiran mudi yazo ya amsa.
Wannan ce ta bani damar yin aikace aikace na cikin jin daɗi, lallai ina dab da cika buri na, abun ya matuƙar ƙarfafa man guiwa, saidai na nazo wajen zaɓen choice na Abunda zan karanta tsallakewa nayi, na bar mashi ya zaɓa man, duk abinda ya zaɓa man daidai ne.
Zuwa azahar na gama komai, har list ɗin abinda zanje in sissiyo mana na buƙata nayi, wanka nayi cikin shiri na simple ba mai ɗaukar lokaci ba, doguwa riga ta material ce jiki na, Afnan ce ta bani ita cikin kayan da ta kawo mani kafin ta koma, da gani ma bata taɓa sanya ta ba, ta amshe ni matuƙa, gyale na ɗauko zan yafa, umma tayi man wani irin kallo, ba arziƙi na ajiye ina ƙumshe dariya a ciki na, oh umma bata so taga nayi gayu, ita har kullum gani take yi ba'a matsayin kowa muke ba, in ana ganin ka ƙwas-ƙwas ma sai ayi ta gulmar ka acikin gidan, dama ga shi ga irin zaman da mukeyi acikin gidan.
Sallamar mudi ce ta katse man dariya da nake yi a zuciya, ɗauko takaddun nayi na miƙa mashi ina ƙara mashi godiya, amsa yayi yana dariya tare da ƙara ma umma ta ya jiki, saboda ɗazu da yazo basu gaisa ba.
Sai da na gama kitsawa sosai, sannan na ɗauki ƴar jikka ta gami da takadda ta list ɗin abubuwan buƙatar, sallama nayi ma umma gami da ficewa daga ɗakin namu kai tsaye zuwa ga barin gidan cikin salon tafiyata da lokutta da dama umma ta kace Allah yayi mani nawar tafiya, su kuma sauran ma'aikatan kance ya ga ce, kai ba kowa kowa ba Galadima kashi🤣
Tin daga nesa na hango shi tsaye jingine jikin motar shi, mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali, baƙa ce wuluk sosai, saidai gilassan ta masu sauƙi duhu ne, ni ban ma taɓa ganin shi a cikin wannan motar ba, da gani dai sabuwar siye ce, to abu da masu abunsu
Sanye yake cikin riga ƴar shara, da wando dogo har ƙasa, kanshi babu hula saidai baƙin gashin shi da akoda yaushe yake kwance luf bisa fatar kanshi, hannun shi na riƙe da makullan mota da takaddun nawa a hannun shi yana dubawa,
Baƙin sun glass ɗin da ya sanya ma idanun shi, su ke katange ka daga kallon cikin ƙwayar idanun shi, kaman kullum dai yana tsaye cikin kwarjini shi, da kamalar shi, Al'ameen mutum ne da idan ka kalle shi sai ka ƙara kallon shi
Duk da ba ni yake kallo ba hakan saida ya jaza mani harharɗewa, cikin son gyara tafiyar tawa na isa daidai saitin inda suke tsaye shi da mudi driver "Ahaf, yallaɓai ai gama ta nan tafe" mudi ya shiga faɗa mashi, ga dukkan alamu magana suke yi ko kuma aika mudin yayi ya kirawo ni.
"OK ce mata tazo ina kiran ta" Abunda ya faɗa kenan, har yanzu idanun shi na kan takaddun ko sau ɗaya bai ɗago ya kalle ni ba,
Kwala man kira mudin yayi "Ke Suhana, kizo yallaɓai na kiran ki" chak naja na tsaya, da ɗan ɓacin rai a fuskanta, in ma kiran ne ai sai ya isa inda nake ba ya kwala man kira ba haka gatsau kowa na saurare.
A hankali na juya akalar tafiyar tawa daga nhfar gate ɗin zuwa wurin su inda suke tsaye, da sallama a bakina na isa lokaci guda ina mai gaida shi "Yaya ina wuni?" bai ɗago ba har yanzu idanun shi na kan takaddun yana nazari su ya amsa mani da "Lafiya" a gajarce
Gyara tsayuwa ta nayi duk a takure nake wallahi, kwarjini shi kan ƙara ruɗani, ɗan guntun murmushi naga ya saki, yana mai juyawa kai tsaye zuwa ga bakin motar tashi ya sanya makullan da suke hannun shi ya buɗe tare da ɗauko wasu biruka guda biyu ya dawo inda nake tsaye
Still bai kalle ni ba, ya shiga man tambayoyi wasu ina bashi amsa, wasu ina yin shiru dan ban sani ba.
Choice ɗina ya tambaya na Abunda zan karanta, nan ma shiru nayi mashi, murya ta har rawa take idan zan bashi amsa da ya kula, inda Allah ya taimake ni mudi da yake tsaye ta gefen mu yana sauraren mu.
Maimaita man tambayar yayi, cikin san kauda shirun da nayi na duƙar da kaina sannan na shiga faɗin "Yaya na bar maka zaɓi, duk abinda ka zaɓa man, ni bani da wani zaɓi, ko wane course ne dai insha Allah zan iya kuma zanyi"
Ɗan shiru yayi jin ta kai aya, ɗagowa yayi a hankali ya zare glashin dake manne a idanun nashi yayi, kafe ni yyai da idanun shi, aikau na ƙara sadda kaina ƙasa, ko alama bana iya ɗago fuskata balle in kalli cikin ƙwayar idanun nashi da har wani zaiba zaiba suke yi
"OK zaki iya tafiya" Abunda yace kenan ya maida idanun shi kan paper ɗin, alamar ya sallame ni kenan
Cikin ƴar sassarfa na bar wurin ina mai hamdala da tambayoyi ba suyi tsawo ba, ba zai iya fahimtar yanda nake ji da aduk lokacin da magana ko tsayuwa ta haɗa mu wuri ɗaya dashi ba.
Cikin san kauda tinanin na tare abun hawa na hau, ina mai faɗa mashi inda zai kai ni, saidai duk yanda naso inbar tinanin ya kasa bari na, ko wanne course ne zai zaɓa man ni suhan? Koma dai minene kuma koma dai wanene zanyi insha Allah, da haka har na isa inda zani,na gama abinda nake yi na juyo gida da tarin siyayya ta
***************
Abubuwa sunyi mana matuƙar sauƙi, yanzu kam Alhamdulillahi, kwana biyar kenan ban kuma jin ɗuriyar hajiya ba, balle ƴan baran dan ta, hidimar bikin su aunty Saudat aka shiga yi ga dan gadan, abun ka da masu dashi, bikin dududu sati huɗu aka sanya shi, bayan iyaye sun shiga al'amarin, matuƙa Hajiya Kubra taso Al'ameen ɗin ya fidda matar aure, Amman fir ya nace shi fa indai bata kyale shi ba, tau ya riga ya zaɓi mata, kuma a shirye yake a ɗaura auren shi ko ma yaushe ne, in ma dasu Nihal ɗin za'a haɗa duk ɗaya ne
Hakan ya tada hankalin hajiya, ta ƙara kafa mana karan zuƙa, gashi yanzu ta fiye ta fiye suke ta yi, yin oder ɗin kayan ɗakin su Nihal ɗin, nima na samu ɗan sauƙi, domin yanzu na rabu da wahalhalun su, bama kullum muke haɗuwa ba, duk da duk lokacin da zamu haɗu ɗin saƙon harara ne kawai za'ayi ta aike mun har sai na wuce sannan a bini da daigon tsaki wani lokacin harda tofar da miyau, sannan ace Allah shi kyauta mu haɗa iri da waɗannan mugayen talakawan ƙasƙantattu.
Duk da bana jin me suke faɗa, hakan na mani ciwo, na dai san magana ce marar ɗaɗi suke faɗa a kaina da umman tawa, wannan ce ta sanya bana ma rawar ƙafa ko ɗokin zuwan bikin nasu, duk da wani lokaci ina jin sanyi na zasu bar gidan zan ɗan samu sauƙi, saidai nima ɗin ai ba zamana kenan ba a gidan
Ƴar ƙaramar waya ta ce ta ɗauki ringin, ajiye gugar da nake yi nayi, cikin mamaki na ɗauki wayar ina duba number ɗin da ta kira ni, na kasa ɗagawa har ta katse, ɗan taɓe baki nayi na ajiye, cikin zuciya ta ina mai faɗin koma waye in ya masu ya kira, Nidai bana da kati a waya, kuma bana da wannan number ɗin a waya ta, dama in Naji kira, ko dai Afnan, ko Aunty Saudat, ko Aunty Nihal, sai kuma ita uwar gayyar Hajiya Kubra, ko cikin ma'aikatan banda number kowa sai ta Mama Talatu, itama dan ita ce shugabar mu.
Cikin ko in kula na cigaba da Abunda nake yi, ina kallon umma ta na bina da ido har wayar tawa ta sake ɗaukar tsuwwa, cikin natsuwa na danna madannin amsawa da sallama a baki na
"Assalamu Alaikum wa Rahmatullah" Abunda nace kenan naja baki na na kulle, shiru ne ya biyo baya na tsawon daƙiƙa biyar, cikin mamaki na ɗaga na kalli fuskar wayar, Still dai wayar na tafiya alamar ba'a datse kiran ba, har zan danna da niyyar kashewa ganin nayi sallama ba'a amsa ba, kuma ga dukkan alama koma wanene yana jinya yayi man shiru
Muryar shi ce ta karaɗe illahirin kunne na, cikin salon maganar shi dake tafiya da hankalin mai sauraren shi ya amsa man sallama cikakkiya kaman yanda addini ya koyar.
A ɗan zabure na ɗaga wayar ina mai ƙara kallon number, kaman mai son gano ainahin kamannun shi a fuskar wayar, natsuwa na nema na sanya ma kaina, gudun kada ya gane mamakin da nake yi, ko ba'a faɗa ba shine, ina ya samu number na? Zuciya ta ta shiga saƙa man, "Afnan" wani ɓangare na zuciyar ya bani amsa, ganin ba zai ce komai ba, na kauda shirun ta hanyar gaida shi
"Yaya ina kwana?" "Lafiya" ya bani amsa a gajarce, ga dukkan alamun shi ne yin magana a gajarce, ya kauda man tinanin da nake yi ta hanyar faɗin "Ki shirya Gobe kuke rubuta Jarabawa, zan aiko mudi ya kawo maki abun buƙata, ƙarfe takwas na safe, in kin shirya ki kira ni da wannan Layin" yana gama faɗar haka ya datse kiran.
Da kallo nabi wayar, kaman mai son gano wani abu, a sanyaye na ajiye wayar daga kunne na, ina mai kallon umma ta d take bina da kallon tana buƙatar ƙarin bayani, "Eh umma, yaya ne, yace gobe zan rubuta jarawaba, muɗi zai kawo man abubuwan da zan buƙata" na ɓata amsa, ina mai sanya hannu na kashe Iron ɗin da nake gugar gami da silalewa na kwanta bisa tantagaryar tiles ɗin dake manne da ƙasan ɗakin, nayi matashi da hannuwa na.
Umman bata ce man komai ba, ta miƙe tsam gami da shige wa toilet ɗin dake cikin ɗakin tana mai mani addu'ar nasara acikin zuciyar ta.
Na daɗe ina muɗiɗɗika a tsakiyar ɗakin, nama rasa tinanin da zanyi, mudi yayi sallama a bakin ƙofar ɗakin, tsam na miƙe gami da buɗe ƙofar ina mai gaida shi, ya miƙo mani leda irin ta botique gami da cewa "gashi inji Oga"
Amsa nayi gami da gaida shi, ya man sallama ya wuce, yana mai cewa in gaida umma ta, da kallo na ishi, ko babu komai mudin yana daga cikin mutanen da nake ganin girma da daraja shi a idanu na, ganin cewa ban taɓa samun shi da koda alamun munafirci ba, irin na sauran drebobin gidan da zaka ga suna ƴan ƙusƙus da su mama mama Talatu da mama uwani.
Zaune nake ina ta juya ledar na gagara buɗewa, har u mata ta fito daga cikin banɗakin ga dukkan alamu dai wanka ta gama, "Menene haka? Kin Gaza buɗewa ki duba, ko kin fasa karatun ne?" umma ta jefo man tambaya tana mai zama gami da janyo kwandon kayan shafan ta tana mutsittsika mai a jikin ta.
Ban amsa mata ba, na shiga buɗe ledar bina fiddo kayan dake ciki, uniform ne ma su masifar kyau, da sandal da socks farare ƙal, sai ƴar ƙaramar jikka ta goyo Amman irin ta zamani an yi mata ado da flowers masu ƙyau da ƙyalƙyali, sai litattafai tili guda na karatu, da suka danganci physics, chemistry, biology, english mathematics ds.
A hankali na shiga warware kayan da suke a goge tas, da gani sababbi ne, skirt ne iyakar guiwa, sai riga longslip da belt da gani tok-in akeyi sai ƴar ƙaramar hijab, da zamu iya kiran ta kai tsaye da himar, cikin kwalalo idanu na kai duba na kan ummata da ta dakata da shafa man tana mai bina da idanu, baki na a buɗe na shiga girgiza kai, "bazan iya sanya waɗannan kayan ba, da gani ma wannan makarantar ba ta musulmai bace"
Umma ce ta wurga man wani irin kallo sannan ta shiga faɗin "kar ki sanya ɗin, sai ki canza wasu ai, tinda tsarin ki zasu bi, ko ba ta musulmai bace, ai rana ɗaya ne sai ki sanya dogon hijab, in kinje can kya cire, kada kiyi wasa da damar ki suhan"
Linke kayan na shiga yi ina mai jinjina yanda zan sanya kayan nan in rasa mutane, kaman wata ƙaura, Amman ba zance ba zan sanya ba, ko don gudun wasa da dama guda da Allah ya bani.
Haka na kwana karatu, lallai na yarda in ka bar karatu