Showing 117001 words to 120000 words out of 247770 words
kawai, Amman ace mace kullum ta fita sai taje gidan su? Wata rana ma acen take kwana koda kuwa yana ƙasar? Kuma iyayen ta na kallon ta ba tare da sun saɓa ko tsawatar mata ba? Shi a gaskiya ba zai iya ɗaukar wannan rainin wayon ba, gashi ace mace bata iya komai ba, duk tabi gida ta cika da ƴan aiki maza da mata, duk da hakan ba wai baƙon shi bane ba, amman shi sam baya da ra'ayin masu aiki barkatai a cikin gida saboda halin tsaro na rayuwa.
*****************
Cikin Hafsat ya tasa inda Sadeeq ɗin ya maido ta nigeria ɗin yace ta zauna, saboda yana ji da cikin baya son dukkan abunda zai dame shi ko ya taɓa mashi lafiyar ɗa, to itama ɗin tafi son hakan, domin yanzu idan Kaga Hafsat ba zaka ce ita bace, tayi ɓulɓul duk da dama ita ɗin ba wai mai rama bace dama cen, fatar ta ta kuma haske da sheƙi, yanzu ta samu aiki da Federal Goverment, mijin nata shi ne ya sama mata, saboda rage zaman kaɗaicin.
Hafsat tasha kuka lokacin da taji labarin ɓatan su suhan ɗin, kuma tayi imanin ba banza ba, hakanan Umma ba zata buƙaci da su bar gidan ba, a daidai gaɓar da Suhan ɗin zata tafi makaranta. Tana addu'a Allah ya bayyana su, ya kuma saka masu zaluncin da aka yi masu a koda yaushe. Bata da kaɗai ci sosai, yanzu Alhaji Awwalun da Hajiya Zainab sun tattara sun dawo gidan da dangin Sadeeq ɗin suka basu nan Abuja ɗin, kaman yanda su kuma kamfann Al'ameen ɗin suka ɗauki matasan da aka alƙauranta masu aiki daga cikin dangin sadeeq ɗin.
Hafsat ɗin na zaune da dangin mijin ta lafiya, kowa na son ta yana yabonta, to su ɗinma mutanen kirki ne, sun san haƙƙin ɗan adam, masalan ma ita da take mata ga ɗan uwansu, suna mata kallon kaman ɗan uwan nasu duk da sun kasance sun fi su Hafsat ɗin komai hakan baisa suke nuna mata sun fita ba, ko kuma wariyar launin fata.
*****************
Haka rayuwa ta dinga garawa,awanni sun shuɗe, kwanaki sun shuɗe, makonni sun shuɗe, gashi har muna fuskantar wata biyu da zuwa makaranta, karatu nakeyi ba ji ba gani, duk da yanzu na fahimci dukkan Abunda Sir, Salim yake yi mani da biyu yake yin shi, tinda sau da dama zaka ji labari na tashi wai ni budurwar shi ce, babu Abunda ke shiga tsakanin mu in ka ɗauke taimako wani lokacin da kuma ƴar fira ta barkwanci haka, to nidai ta ɓangare na babu Abunda zan iya cewa ina ji game dashi, duk da yake kasancewar shi mai barkwanci da yawan ban dariya, bayada matsala da kowa da komai, saidai Abunda na kula, ki dai baya tare da matar shi, ko kuma baya jin daɗin ta ne, domin baya yadda ya bani labarin ta, kullum dai labarin bai wuce na Ammin shi ko kuma na Sholy da Usee, to nima nafi son hakan tinda sha'ani ne na iyali.
Har da Ammin shi ya haɗa ni na gaida ta, yanda naji muryar ta mai sanyi sosai, da yanda ta amsa mani kaman zata rungume ni cikin wayar hakan yayi mani daɗi, ashe a duniyar nan akwai wanda zai soni ya tattashe ni kaman yanda Sir, Salim da mahaifiyar shi suke yi, tin kwanaki da yaje gida, sha tara ta arziƙi da kuɗi sosai ta bashi ya kawo mani, da kam bazan amsa ba, har saida ya kira ta, aiko tace ya bani wayar, ya kuwa bani ta hau faɗa, wai ashe ban ɗauke ta uwa ba, da har zata bani abu inƙi ƙarba, haƙuri na shiga bata gami da yi mata godiya.
Kewar ummata ta addabeni sosai, ji nake kaman in buɗe ido in ganta a inda nake.
Ban ƙwauron baki ba, na faɗa ma Sir Salim kaman yanda ya zama abokin shawara ta a yanzu, duk yanda zai yi ya shiga jikina yayi, ina jinshi kaman ɗan uwanka yanzu uwa ɗaya uba ɗaya, masalan da na kula dashi kamilin mutum ne, ko a makarantar kaf an bashi shaida, ba dai kiji ance yana kula mata ko hulɗa dasu ba, duk da an sanshi da barkwanci, wanda barkwancin ma ne ya sanya ni sakin jiki dashi ba tare da na kula ba.
Kaf makarantar babu wacce zan nuna ince itace ƙawa ta ko aboki ya ta, saidai wanda muke ɗan gaisa wa dasu sama sama sai kuma ƴan ɗakin namu da suma ba hayaniya ce ta sha masu kai ba, kowa karatun shi yake yi hankali kwance.
Haƙuri ya bani gami da cewa insha Allah zanga ummata very soon, nidai kawai inyi karatu, ban da matsalar kayan abinci ko kuɗi, duk Ammin Sir, Salim ta aiko mani dasu masu yawa, tin bayan daya bata labarin gidan namu, da kuma ƴar fahimtar da yayi cewa karatun dai ne nakeso inyi aman ba tare da muna da ƙarfin hakan ba.
To itama dai burin Hajiya Khaltum ɗin shine dai yaron nata ya samu ya daɗa wani auren, ko hakan zai sa Ma'un ta cenza hali, domin Sam basa jin daɗin ta, mace ce wadda zamu iya cewa rako mata tayi. Sam bata da Sirrin kanta, batasan yanda zata zauna da kowa lafiya ba, ga bala'n kishi kaman zata mutu, kasancewar mijin ta lecturer, ya sanya ta sanya ana binciken shi ta bayan fage ba tare da ya sani ba.
Masifar ta tayi yawa, saboda haka ne, ko lokacin daya koma gidan ta same shi da maganar cewa ta san dukkan Abunda yake aikatawa a makarantar na neman wata yarinya, Sam bai ɓoye mata ba, yace aure yake so ya ƙara, aikuwa masifa da bala'i babu wanda ba'a sha ba, har barin gidan nashi tayi, ta kuma bar mashi yaran, hakan ce ta sanya ya kwashe su ya kai ma Ammin shi, to ita ɗin ba mai masifa bace, ce mashi tayi yake ya lallashi matar shi, da taga ya kafe ne akan ba zai je ba, sai tace mashi ya tafiyar shi, idan Ma'un ta huce ta dawo an maida mata yaran.
Haka kuwa aka yi ya sake juyo ma da Suhan sha tara ta arziƙi daga Ammin tashi, bai ƙara so ba saida ya tsaya ya taho da Ummana domin tazo taga inda nake karatu.
Yanzu kam ta fara yarda da Al'amarin yaron, tin bayan da suna cikin mota ya haɗa ta da Ammin shi suka gaisa sosai, har tana ce mata sai ta kawo mata ziyara har gida. Murmushi ummata tayi tana sake yi mata godiya da ɗawainiya da yaron nata yake yi da Suhan, sannan tace mata sai tazo, sallama sukayi suka kashe wayar, da ɗan murmushi ta miƙa ma Sir, Salim wayar da yake cen gaba yana driving, ita kuma ita da Hajjo a bayan motar har zuwa shigar su makarantar tamu.
Kwatsam sai ga ummata daidai lokacin da na fito da niyyar zuwa masallaci sallah, aikuwa da gudu na ruga na rungume ta, kwalla na shatata a samn fuska ta, janye jikin ta tayi tana girgiza mani kai, Hajjo na gaida, gami da ɗan kallon Sir, Salim da ya kafe ni da mayatattun idanun shi, da a yanzu na fara jin nauyin su a kaina bansan dalili ba kuma.
"Zamuje ɗaki Sir, Nagode Kwarai" Abunda na faɗa kenan ina mai sauke kwayar idanuna ƙasa. Ɗan jinjina mani kai yayi yana mai juyawa ya shige motar shi gami da barin wurin bayan yayi masu umma sallama akan cewa zai je ya dawo.
Haka muka ranka ya har ɗakin namu. Ba kowa ciki duk suna wurin lectures, rasa inda zan ajiye su umma nayi, salla suka fara yi, ni kuma na fara nema masu Abunda zasu ci. Wata yarinya ce tayi sallama da manyan ledoji a hannun ta ta miƙo mani wai inji Sir, Salim.
Amsa nayi ina mai godiya gami da buɗe ledojin, take away ne manya, shinkafa ce jalop da taji kayan haɗi, sai manyan kaji guda biyu da lemuna masu sanyi, ai sai na kashe stove ɗin ba jawo plate na juye masu gami da sanya masu chokulla na ɗauko cups na shan lemon na ajiye masu.
Basu ɓata lokaci ba wajen cin abincin, so suke su juya saboda kada suyi dare. Nasiha da wa'azi da jan hankali babu wanda ban sha ba, nan umma ta kawo kuɗi dubu goma ta bani tana mai ƙara bani haƙuri, akan cewa yanzu taga wuri akai akai idan ta ɗan samu wani abu zata dinga zuwa tana kawo mani insha Allah.
A haka suka gama, na kira Sir Salim ɗin, cewa yayi yana waje yana jiran su. Kaman kar mu rabu haka naji, aiko saida bayi kuka sosai har na ƙaryar ma da ummata zuciya, itama saida tayi kwalla Hajjo ce taje bamu baki, haka na juye masu sauran naman da lemon nace ko Malam ne sa kai mawa, aiko Hajjon taji daɗi sosai ta yadda ban manta malam ba, to nikau ina zan manta mahaifi na? Tinda yanzu shine nake ma kallon uba a wuri na.
Har bakin mota na raka su, da kanshi ya fito ya buɗe ma ummata ni kuma na buɗe ma Hajjo, bayan sun shiga ne ya tsattsare ni da idanu wa alamar tuhumar kuka na menene nakeyi? Girgiza mani kai ya shiga yi, alamar kar nayi kuka, ya shiga motar yana mani inkiyar zai dawo.
A haka ina ɗaga masu hannu har motar ta fuxe daga harabar makarantar, juyawa nayi jiki ba kwari, zuwa ɗakin namu. Kuka nasha kaman ba gobe, ummata duk wahala ta sanya ta ƙara tsufa, kaman ba ita ba, Allah ya sani tausayn kanmu da kanmu ya kama ni, dole in maida hankali inyi karatu ko hakan zai zama silar fitar mu a wannan ƙangin rayuwar.
Saida ya tabbatas ya sanya su mota mai kyau ya biya kuɗin motar, sannan ya basu wani abu yace su riƙe su sha ruwa a hanya, ummata ƙin karɓa tayi, sai Hajjo ce ta sanya hannu ta karɓa, suka sake jaddada godiya, ummata ta sake bashi amana, sannan ya juyo ya dawo makarantar.
Kirana yayi na fita, nan ya shiga sake lallashi na, da yake mutum ne shi mai barkwanci, sai gashi bamu rabu ba, saida ya sanya ni dariya sosai da nishaɗi. Sannan ya kira Ammin shi da yaran shi muka gaisa yana ce masu ga Auntyn su su gaida ta suka hau tsalle suna mani gwarancin da bazan iya ganewa ba, da yake Ma'un bata koma gidan ba har yanzu, ita kuma Ammi taƙi zuwa, tace ai tinda babu abunda aka yi mata idan ta huta ta koma da kanta. A haka mukayi sallama ta kashe wayar, ƙaunar yarinyar na malala a cikin zuciyar ta, ga dukkan alamu yanzu ne yaron nata ya samu mace mai hankali da natsuwa wadda zata iya kula mashi da gidan shi da yaran shi, don ita talaucin su ba matsala bane a wurin ta, tinda ta san mai duka ne ke yin komai.
Haka rayuwa take tafiya, ɗan adam ba don ya kula ba, saidai kawai yaji shi a cikin kabari. Gashi har zamu fara semester exam, karatu ya ɗauko zafi sosai, don ma Sir Salim na taimaka mani sosai, lectures take mani a duk lokacin da muke free bama komai, kuma ina ganewa sosai da sosai, kwatsam sai ga Ma'u a makarantar mu, lokacin muna zaune ta cen baya inda ɗalibai ke zaman karatu.
Mun duƙufa muna ta karatu sai naji an ja hijab ɗita ta baya sosai kaman za'a shaƙe ni, aiko da hanzari na ɗaga domin ganin ko wacece, ganin bansan fuskar ba, sai na zare hijab ɗin baki ɗaya na sakar mata ita a hannu, gami da miƙewa na fuskan ce ta ina mai cewa "Baiwar Allah lafiya kuwa? Me na aikata maki haka da zafi da kike beman shaƙe mani wuya?"
Da hannu ta nuna mani Sir, Salim wanda ya riga ya miƙe mamaki ya kama shi har ya gaza cewa komai
"Me ya haɗa ki da mijina?"
Ta jefo mani tambaya cikin hargagi ta nayi tana jijjiga jiki.
Kallona na maida kan Sir Salim da har yanzu ya gaza cewa komai
"Au Malam? To ai gashi tsaye shi zaki tambaya ba wai ni ba" na maida mata da amsa cikin son kawar da tsoron ta daga zuciya ta.
"Au dama kece yarinyar da akace kinbliƙe mashi kin hana shi saƙat a makaranta?" irin ku dama ba karatun ke kawo ku ba, neman mazan mutane kuke zuwa nan yi.... "
" Asma'u"
Sir, Salim ya katse ta cikin ɗaga murya yayi kanta kaman zai bugeta.
Sai kuma ya dakata yana faɗin "Me kike yi ne haka? Me ya kawo ki nan makarantar? Kinzo ne ki ɗaga mani hankali ne? Ki kiyaye ni fa, da izinin wa kika zo?"
"To dama da izinin wa kake so nazo ne? Ko har yanzu da bana zaune gidan ka nema kake yi in nemi izinin ka idan zan fita?"
Nikam sun ma ɗaure mani kai wallahi, gani dai tsaye ba hijab jikina yana hannun ta duk ta cukuikuye shi, inda Allah ma ya taimake ni kayan jikina doguwar riga ce mai faɗi, sai na sanya hannu na warware gyalenta ɗana ɗaura bisa kaina.
" Eh ko da baki gidana, ai da aure na a saman kanki, idan baki sani ba yanzu ki sani, kuma wannan ita ce yarinyar da kikaji labari, kuma ki sani ba liƙe man tayi ba, ba naniƙe mani tayi ba, hasali ma nine na liƙe mata na naniƙe mata, Abunda nake so ki sani, da batasan me ke faruwa ba, batasan dalilin da yasa nake tare da ita ba, Amman yanzu kinja zata sani. Wannan ita ce Suhan wadda kikaji labarin ina nema, kuma wadda na faɗa maki cen baya cewa *Son ta nakeyi, kuma auren ta zanyi har Ammi ma ta san da zancen* "
Cikin matuƙar tashin hankali da jin kalaman Sie, Salim ga matar tashi na ɗago idanu ina binsu da kallo, ga kuma student ta duk suka zagaye mu suna kallon mu, sai ƙus-ƙus suke yi, waɗanda dama cen sun jima suna son Sir Salim ɗin murna suka fara yi, suna gode ma Allah da basu ne hakan ta faru dasu ba.
"Ai wallahi ko wacece ta san da zancen ba Ammi ba, bata da hurumi a gidana, baka isa ba, wallahi kayi kaɗan Salim, ni zaka tozarta ka wulaƙanta kan wannan ƴar abun?" ta faɗa tana mai nuno ni da hannun da hijab ɗin tawa yake kai, sannan ta ɗora da faɗin. "Wuuu Amman dai wallahi kaji kunya, inaso ka sani wallahi tallahi idan ta kuskura ta shigo gida na, sai ta kwashi kashin ta a hannu, kuma mu zuba mu gani shege ka fasa" ta faɗa tana mai maida kallon ta bisa kaina da nake tsaye kwalla ta cika man ido taf, Amman na kasa barin ta ta zuba, saboda gudun raini daga wurin ta, jefo mani hijab ɗita tayi tana mai kyasta mani yatsu alamun in kiyaye, sannan ta juya a sukwane ta nufi motar ta, ta shiga ta fisge ta da matsanancin gudu tabar wurin.
Rasa abund zanyi nayi, saidai na zuƙunna na shiga tattara litattafai na, da kayan karatu na, na ɗauki hijab ɗita da duk ta duƙunƙune ta, na juya da niyyar barin wurin.
Gabana ya sha, haƙuri ya fara bani, girgiza mashi kai na shiga yi alamun babu komai, wani tsumammen kuka yana mai taho mani, duk kunya ta gama kama ni, masalan da ma abun ya faru akan idon ɗalibai, yanzu makaran ta zata ɗauka, yanzu zan fara rashin sukuni a makaranta, ai bansan haka halin matar shi yake ba, da ko alama ma bazan yadda in saki jiki dashi haka ba sosai.
Zagaye shi nayi da ɗan gudu na, na nufi hanyar da zata sada ni da ɗakin namu, yayin da na bar shi na tsaye sororai abun duniya duk ya dame shi.
Dole ne kuwa yau yayi ma abun tufkar hanci, dole ne ya dakatar da kuma faruwar hakan, shima a matuƙar zuciye ya shiga taka wa kaman ingarmn doki zuwa wajen da motar tashi take ajiye ya shiga gami da fizgar ta kaman zai taka mutane haka yabar makarantar da matuƙar ɓacin rai.
Nasha kuka na, ƴan ɗakin mu na bani baki, lallai sunga Abunda ya faru dukan su, domin an taru sosai a wurin, saboda haka ne ma suka bani shawara da in ɗan ja jiki da Sir, Salim indai ina so in tsira da mutumci na, saidai fa har yanzu mamakin kalaman shi basu sakeni ba, yaushe ne ya fara sona har haka da har yake cewa Ammin shi ta sani? Yaushe yaje masu da maganar son aurena ni Suhan? Anya kuwa ba ɓatan kalamai yayi ba kuwa?
Da haka na zame na kwanta idanuna rufe ruf, babu abunda ke kai komo a ƙwalwa ta illa iyaka maganar da ya faɗa ma Matar tashi.
Wayata ce ta ɗauki tsuwwa, sunan Ammi na gani a bisa wayar, sai na Gaza ɗagawa, illa ma wani sabon kukan daya zo mani, gashi ummata bata da waya, koma tana da ita ƙauyen babu service da ko ita ce zan kira ta inji muryar ta ko naji sauƙi.
Daga wannan sai wannan, na rabu da cen da duk abunda ya shafi cen, sai ga kuma wata ta kunno kai nan, ya zanyi da rayuwa ta? Ya zanyi da wannan al'amari dake faruwa dani ne?
Karo na barkatai kenan da tinanin Ya Ameen ke faɗi mani a cikin ƴan kwanaki nan, tinani na ne ya tsaya cek, lokacin da Fuskar Al'ameen ɗin da yanayin shi suka faɗi mani a rai, ko