Showing 30001 words to 33000 words out of 247770 words

Chapter 11 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10404

Dr Ashafa ɗin yana biyo shi a baya tare da kayan aikin su na likitoci

Sake shigowa naga sunyi shi da likitan, watau sai da ya kira likitan kenan? Haka na cigaba da rayawa a rai ina mai janye idanu a ga barin kallon su, bakin gadon suka ja suka tsaya, hakan yayi daidai da farfaɗowar umman tawa.

"Ƴan mata zo ki taimaka ma umman ki ta tashi zaune kinji, zamu auna ta ne" likitan ya faɗa yana mai waiwayowa ya kalle ni da nake zaune ina aikin binsu da idanu da nayi nayi ga barin kallon su Amman na kasa, Ya Ameen ɗin yayi kyau, wani abu ke taso man cen ƙasa rai duk lokacin da ya bayyana inda nake, tasowa nayi a hankali na kama umman tawa ta zauna sosai, shi kau gogan ko kallo na ma bai yi ba, kaman ma bai san ina ta wurin ba, ya koma mani Yaya Al'ameen ɗin da na sani tin cen baya, da baya ɗaukar wargi, fuskar shi Sam babu walwala saɓanin yanda ya fita ba daɗewa.

Aune aunen su na likitoci ya shiga yi, sannan ya ɗago yana mai faɗa ma Ya Ameen ɗin komai normal, za ta iya cin komai, kuma ta kula da shan maganin ta akan lokaci, zamu iya tafiya gida, Amman nan da sati ɗaya mu dawo a sake gwada ta a gani, dokoki sosai aka shinfiɗa ma umman tawa, sannan aka hana ta cin wasu abubuwa da dama; wayyo likita, bai san ma abincin sai wanda aka ga dama aka bamu ba, in kace ba zaka ci ba sai yunwa ta kashe ka babu mai sani.

A haka na kama umman tawa muka fito, bayan motar na saka ta, ta ɗan kwanta na koma na kwaso sauran kayan da suke mallakin mu, har da take away ɗin da yayo mana da ko kallon shi banyi ba, balle in buɗa inga Abunda ke ciki.

Har zan shiga bayan ya tsattsare ni da idanun nan nashi masu rikita dani, sannan ya mani alama da in shiga gaba, haka kuwa aka yi shiga nayi na takure, masalan ma ga umma ta acikin motar kuma idanun ta biyu ba bacci take yi ba.

Kai tsaye naga mun nufi hanyar kasuwa, ban da hurumin tanka wa balle in tambaya me zamu yo a kasuwa, ƙila uzirin shi ne zai kai shi; parking yayi bakin tanƙamemen suoer market ɗin da yake bakin kasuwar, fita yayi ya shiga ba dadewa sai gashi ya fito yaron shagon na biye dashi a baya, hannun shi niƙi niƙi da kaya, but ya buɗe mashi tare da Sanyawa ya rufe, ya zagayo ya tada motar muka shiga cikin kasuwar, nan ma soyayya yayi sosai, cikin ni da umma ta babu mai tankawa, kowa da abunda yake saƙawa cikin rai.

Gida muka nufa kai tsaye, yayin da yake parking ya yafito mai gadi da hannu, cikin hanzari ya iso inda muke ƙoƙarin fitowa daga cikin motar; umarni yayi mashi da ya kira mama talatin a sashe namu na masu aiki, aiko ya ruga cikin hanzari, sai gashi da mama talatun ta taho cikin sauri, umarni yayi mata da ta kama man umman tawa mu kai ta ɗaki mu kwantar, yayin da ya kirayi mai gadin da isa da yake tsaye yana gyaran flowers da suka taimaka wajen ƙayata gidan, kayan yace su kwashe su shigar mana dashi cikin ɗakin mu, yayin da ya ja motar shi yana mai barin gidan.


Kai tsaye ɗakin namu muka nufa da umman tawa da take ɗan iya taka wa a hankali a hankali, kwantar da ita muka yi, yayin da su isa suka shisshigo mana da kayan namu suka fice suna ma umman tawa sannu da Allah ya kyauta, ina kallon mama talatun tana jinjina kai tana mai ƙare ma niƙi niƙinbkayan da ta gani tare da mu, ta dai san wannan aikin Alhaji ƙarami ne, wato dama ya ƙi bin su Hajiya Babba ne domin ya tsaya bauta mana kenan ko? Wai menene haɗin shi da mu ne? Su dai basu ga wata alama da ke alamta masu akwai wani abu tsakanin Suhana ba da Alhaji ƙarami ɗin balle ace dan ita yake yi? Koma minene zata yi ƙoƙarin sanar da hajiya ɗin, me hakan ke nufi ne? Ya kamata hajiyar tayi wani yunƙuri akai wallahi, ita ta ma ga sanyar Hajiyar wannan karon akan yanda ta santa da in ta ƙi abu duk yanda zata yi akan taga bai faru ba ta sani, tana cike da tsantsar mulki da kuɗi, naira shegiya ce, mai maida tsoho yaro ta maida yaro babba.


(Humm🤔🤔 Ya Allah kayi mana tsari da Hassada, ƙyashi, ganin gari da munafunci ameen ya Rab🤲🏻)

Bayan duk sun fita ne, na gyara komai a ɗakin na adama komai inda ya kamata, kayan ciye ciye ne da basu da illa ga masu ciwon zuciya irin wanda likita ya bada umarnin aci, su ne ya kwaso mana su sosai da sauran kayan buƙatu har da kayan marmari ma da zasu yi ma mai rashin lafiya daɗin ci, gyaran ɗakin nayi nayo wanka na shirya kaina cikin baƙar doguwar riga mara nauyi na tattara gashi na na ƙulle cikin ribom sannan na ɗaura ɗan kwalin rigar a bisa kai na, nayi kyau daidai misali, sannan na ɗauko ledar take away ɗin da yayo mana tin asibiti na buɗe da niyyar zuba mana muci ni da umma ta, lafiyayyen chips ne da plantain, sai soyayyen ƙwai da miyar kayan ciki, sai ƙamshi take har yanzu da sauran zafin shi, saboda mazubin na glass ne, da gani dai abincin zai yi tsada, sai dai baya cuwuwa ga umma ta saboda farin mai da aka yi using wurin suyar, kaina kaɗai na zuba mawa na fidda sauran ga ƴan uwa na ma'aikata da har yanzu sun gagara shigowa yi mana koda sannu saboda tsabar hassada, Abunda na san zata iya ci wanda likita bai hana ta ci ba na zuba mata, saida na tabbatas taci na ɓalli maganin ta na bata tasha sannan na gyara mata kwanciyar ta, na koma gefen katifa na zauna ina ya ƙunar abincin ahankali

Fira mukeyi jefi jefi da umman tawa da take bina da kallon tsantsar ƙauna ga ɗiyar tata, addu'a dai kam Al'ameen ya sha ta daga bakin umman tawa, godiya take jerawa wanda hakan ne ta sanya ni ɗan murmusawa a hankali dai ina ci gaba da cin abinci na; Sallama yayi daga bakin ƙofar ɗakin yayin da umma ta ta bashi izinin da ya shiga daga ciki, lokaci ɗaya tana mai umartata da shinfiɗa mashi darduma.

Kasa tashi nayi, domin jikina babu hijabi babu gyale, gashi rigar mai bin jiki ce ta fidda duk surar jikin dake Sanye da ita, kuma a zahiri bai kamata ya ganni haka ba, saboda shi ɗin ba muharrami na bane, hakan ce ta sanya na shiga bin ko ina na jikina da kallo kaman mai son gano wani abu.

"Hauwa'u dake fa nake magana fa, nace ki shinfiɗa mashi darduma ya zauna kin bar shi tsaye" umman tawa ta faɗa tana mai yunƙuri tashi, a haka ta samu ta zauna daidai domin Nidai na gagara koda motsi balle in taimaka mata har ma nayi mashi shimfiɗar

Hankalin shi ya maida kanta da take ajiye plate ɗin abincin kaman mai tausayin ƙasar, ta shiga miƙewa a hankali, lura da yayi da Abunda take ɓoyo ko ji ma kunya ne ya sanya shi kauda kanshi gefe, ya maida hankalin shi kan umman tawa yana mai ɗan sakin guntun murmushi iya laɓɓa, ko me take ɓoyo? Wannan mitsitsiyar yarinyar ma, da yake kyautata zaton garin jiki ne ya kwashe ta, ita har tana ganin ma ta cika ta kai mace, ƙara murmusawa yayi daidai lokacin da take shinfiɗa dardumar ɗan nesa kaɗan da katifa tasu.

"Nagode" ya faɗa iya maƙoshi maganar tana mashi wahala, yana mai zama ya tanƙwashe ƙafafun shi irin zaman salla, lokaci guda yana mai gaida umman tawa, cikin sakin fuska ta amsa mashi, sannan ya ƙara mata ya jiki da Allah ya sauwaƙe.

Godiya ta shiga jera mashi da kuma fatan nasara da cigaba a rayuwa, harma da iyayen shi, hakan ce ta sanya shi jin daɗi, yana mai ƙara ƙaunar matar da son taimaka mata da duk ahalinta.

Ikon Allah, abikan aikin mu da tin ɗazu suka kasa leƙowa su ga jikin umman tawa su gaida ta, sai gashi ɗaya bayan ɗaya yanzu da suka ga shigar Ya Ameen ɗin ɗakinmu suna shigowa gaida ta da ganin ƙwam, kowa ya fita kuma sai ya ƙara da abin da ya gani gaba.

Sake natsuwa yayi yana mai ɗan yin gyaran murya a hankali, sai da ya maido kallon shi inda nake rakuɓe bisa katifa gefen umman tawa, sannan ya saki wani ƙayataccen murmushi ganin ta sanya hijabi da shi bai ma kula da lokacin da ta ɗauko shi ba, haƙuri ya shiga ba umman tawa, da mata Alƙawarin hakan ba zata sake faruwa ba, ya faɗa mata afnan ce ta sanar dashi komai; ɗan faɗa umman tawa ta shiga yi tana faɗin hajiyar ta isa ne ya sanya tayi masu faɗa, ai ba wani abu bane, gyara ne take so ayi, kuma mun ɗauka insha Allah.

Haƙuri ya ƙara bata sannan ya shigo mata da maganar makarantar tawa, ta bacin yardar ta ta ƙara bashi, sai dai tana mai shawartar shi da yayi komai a hankali kada ran hajiyar ya ɓaci, ya alƙawarta mata komai ya wuce kuma babu abin da zia faru insha Allah.

Maida kallon shi yayi yana mai cewa "Ki ɗauko man takaddun naki in gani ko, don mu san ta yanda zamu ɓullo ma al'amarin" ya faɗa yana mai kauda idanun shi daga kaina kaman ma ba dani yake magana ba.

Miƙewa nayi cikin ɗan sanyi gami da nufar wardroop ɗin tawa, gami da janyo ƴar ƙaramar folder da takaddun tawa suke na miƙa mashi.

Amsa yayi yana dubawa, mamaki fal a ranshi na yanda yarinyar take da ƙoƙari, gashi dai makarantar masu hannu da shuni tayi, saboda Alhaji Mustapha ne ya sanya ta a makarantar har ta gama, kafin abubuwa sukayi mashi yawa ya tafi wani aiki ƙasar Indiya daidai lokacin da Jarabawa tasu ta fito wannan shine ya sanya ya shafa'a da karatun yarinyar koda ya dawo kunsan mnyan mutane, ita kuma Hajiya Kubran bata tina mashi ba, a cewar ta hakan ma ya isa, wa yace ƴaƴan masu aiki na makarantar jami'a (🤔🤨😏 ke kika hana ko Hajiya Kubra)

Takaddu sunyi kyau ya shiga faɗi da ɗan murmushi shi irin na miskilai, kai kace ma bai yi ba, sannan ya miƙe dasu a hannun shi yana mai cewa za'a siya jamb sai in cike tare da course ɗin da nake so, in naga ban iya ba sai in same shi ya koya man (kun ji ba Bigboo, ko ya manta da halin gidan nasu ne?) da to muka bishi da umman tawa, kuɗi ya ajiye kusa da umman tawa masu ɗan dama yana faɗin ko zata buƙaci wani abu, sannan ya ƙara jaddada mata kar taci Abunda likita ya hana, idan muna nuƙatar wani abu muyi mashi magana.

Umman tawa ce ta shiga faɗin lallai ba zata amshi waɗannan kuɗi ba, cikin girmamawa ya shiga bata haƙuri da faɗin duk abin da yayi mana haƙƙinshi ne da yayi mana, wannan ba wani abun damuwa bane, duk ma in muna buƙatar wani abu mu tuntuɓe shi a shirye yake da ya taimaka mana.

Godiya ta shiga ƙara jera mashi da yabanma dukkan in hidima da yayi damu ɗin "ba komai umma, Allah ya ƙara sauƙi" ya faɗa yana mai taka wa ya bar ɗakin riƙe da Takaddu na a hannun shi.

Oh Allah🙏🏻 Ashe zanyi karatu a rayuwa ta? Ashe Ya Ameen na magana haka? Yanda naga ya zage suna ta fira da umma ta, kuma duk wata kalma da zai faɗa cikin taka tsantsan da girmamawa yake yin ta kaman yana magana da Hajiya kubra, murmushi na shiga saki akai akai, ina mai sauke ajiyar zuciya, mafarki a ya kusa tabbata, jikina na bani mun kusa fita daga cikin halin ƙuncin da muke ciki ni da umma ta, daga na gama karatu na samu aiki zan gina mana gida, na ɗauke umman tawa muje cen muyi Rayuwar mu, muma muci gashin kanku, mu rabu da takura da jaraba Hajiya kubra, Allah na gode maka, Allah ka saka ma wannan bawa da
Alkhairi a rayuwar shi, ka haɗa ci da mata ta gari, da zata kula dashi, kuma tayi haƙuri da halin hajiya Kubran.

"Tashi ki naɗe dadduman in kin gama murnar" u mata ta faɗa cikin murmusawa da ke nuna sallar jin daɗin ta, da farin cikin ta.

Yunƙurawa nayi ina mai da rawa a fili na shiga faɗin "umma ai dole inyi murna kin gama man komai, Allah ya cika mana burin mu, ashe da rabon zan yi karatu nima in samu ilimi kaman yanda kowa ke samu?"

Murmusawa tayi tana mai kishingiɗawa tare da faɗin "Ai wannan yaro ɗan albarka ne, Allah dai ya bamu ikon saka mashi da alkhairi kaman yanda yake mana shi da mahaifin shi, ki kauda kuɗin nan ki maida hankali ki ci abinci" da to na bita ina faɗin "ni wallahi ummana tsabar murna ma yasa naji na ƙoshi"

"ki dai maida hankali" umman tawa ta bani amsa tana mai lumshe idanun ta murmushi fal a fuskar ta.







Ta ɓangare guda kuwa Al'ameen ɗin na fita wayar Mom ɗin nashi na na shigowa, tare da umartar shi da cewa ko me yake ya tabbatas ya biyo jirgin yamma ya isa Katsina tana son ganin shi, shi kin mamaki ya shiga tambayar ta ko lafiya? "Lafiya lau" ta bashi amsa tana mai datse kiran, Layin Afnan ya nema gami da tambayar ta, ta faɗa mashi kawai dai taga an kira ta ne daga gidan Amman bata san ko wanene ba, kuma daga gani gulma aka kawo mata, "is OK" ya faɗa yana mai katse kiran ganin kiran babban Abokin nashi da zai kawo mashi ziyara yau ta shigo wayar shi.

Amsawa yayi cikin son kauda zargin komai daga ranshi, bayan sun gaisa ne yake faɗa mashi ya iso gashi a airport, cewa yayi ya jira shi yana zuwa ɗaukar shi.

Ko da ya isa ya tadda abokin nashi yana jiran shi, cikin son juna da tsantsar farin ciki suka rungume juna suna mai mararin juna da tsantsar ƙauna ga aminan guda biyu, basu bar airport ɗin ba sai da ya yanka masu ticket guda biyu tare da kallon Bilal ɗin ya shiga faɗin "yaro yau ƙauye zaka kwana, ka taddani tafiya ta gaugawa ta taso mani" cikin murmushi Bilal ɗin ya kai mashi ɗan ƙarami duka a damtsen hannu yana mai cewa "To ya zanyi Friend" ai ko ruga ka kai ni dole in kwanta, ya zanyi tinda na riga nazo?"

Cikin walwala da jin daɗi suka bari airport ɗin direct gida ya wuce dashi domin yaje yayi wanka ya huta kafin lokacin sallar azahar ta ƙarasa.



~Oum-Deedat ce~
[8/5, 8:24 PM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._


_*Page ~13~*_

_To Readers_ --- *Abun da kuka ji da zai amfane ku ku ɗauka, wanda kuka ji akwai kuskure ciki, kuyi watsi dashi, mu ba muji wahalar zaunawa muyi amfani da idear ɗinmu ba mu rubuta maku labarin da zai amfane mu ba baki ɗaya ba, sai ku da zakuyi comment ƙarƙarinta layi biyu zuwa uku, shine zai ke maku wahala, Anya kuwa readers kuna kyautawa🤔? Muna maraba da gyara ko ƙorafi, Amman ba ta hanyar zagi, ko cin zarafi ba, kuskure kowa nayi indai kai ɗan adam ne, kuma ajizi, so saboda haka muna shawartar ku da ku dinga ƙarfafa mana guiwa, wadda kuma taga labarin baiyi mata ba, toh ta bar mana abunmu ba sai ta karanta ba, bamu sanya kowa dole ba, imfact ma babu dole sai rai yaso a rayuwa. fans muna godiya da irin supporting ɗin da kuke bamu 💓muna yinku over, Allah ya bar ƙauna, wannan saƙo ne daga ƴan ƙungiyar ~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

Fira sosai suka shiga yi da aminin nashi da bashi da kamar shi, kaman ba Ya Ameen ɗin da kuka sani ba, har yana zaulayar abokin nashi, akan zancen bikin nashi da za'ayi watanni ƙalilan masu zuwa inda anan Abuja zai auri yarinyar ya tafi da ita cen.

Sai da sukayi wanka suka shirya tsaf sannan suka wuce wani eatery mai bala'i kyau da tsada suka ci abinci sannan suka koma gida domin ƙara hutawa.

Al'ameen ɗin ba mai yawan yawo bane indai yana ƙasa, yafi ganewa ya zauna a gida a part ɗin nashi yayi aiki.

Yanzu ma hakan ce ta faru, yayin da ya jawo laptop ɗinshi ya shiga aiki, wannan ce ta sanya Bilal ɗin fahimtar cewa ƴan maganar sun bar kan aminin nashi, to ko wacce magana zai yi mashi fa zai yi mashi shiru ne, har sai lokacin da yaso tankawar kuma baya maido da zancen da ya riga ya wuce, wannan ɗabi'ar shi ce tin yana ƙarami, balle yanzu da ya girma.

Kwanciya Bilal ɗin yayi domin yana jin baccin gajiya gashi ya ƙoshi har wani lumshe ido yake yi.

Bilal ɗan gayu ne na ƙarshe, yana da hankali da tunani sosai duk da kasancewar shi cikin jajayen fata, hakan bai canza halin shi da mu'amala shi ba, wannan ce ta sanya abotar su da Al'ameen ɗin da take tin ta yarinta take daɗa ƙarko har kwanan zancen.

Aikin shi yake yi cikin salo da kwarewa yake sarrafa kwamfuta, kaman dama cen shi ne ya ƙera ta, to ai dama karatun shi kenan kada ku manta.

Kiran salla ne ya farkar da Bilal ɗin yayin da Al'ameen ɗin har ya ɗauro tashi alwalar, bayan

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login