Showing 33001 words to 36000 words out of 247770 words

Chapter 12 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10403

Bilal yayo ne suka nufi masallacin da yake gefe ta jikin ɓari ɗaya na gidan nasu.

Ƙarfe biyar daidai sukayi shirin barin garin, yayin da Al'ameen ɗin ya tara dukkanin ma'aikatan gidan domin bar masu jan kunne tinda za'a bar gidan ba kowa sai mu kaɗai.

Ni da umma ta ce kawai bama wurin, ja masu kunne yayi sosai akan su kula da komai, Bilal ɗin na tsaye gefen shi yana ta murmusawa domin ya san abokin nashi kwarai da rashin son wargi, gashi dai ya iya mu'amala da ma'aikata dama cen, sai dai shi mutum ne mai son taka tsantsan da kula.

Bayan ya gama dasu ne, ya nemi Bilal ɗin da ya raka shi ɗakin namu domin ƙara duba jikin umman tawa.

Kwarai Bilal ɗin yayi mamakin ina yake nufa haka da yake ta ratsa sashen ma'aikata haka, sai dai bai ce mashi komai ba ya cigaba da bin shi a baya har zuwa bakin ƙofar ɗakin namu da yake tsaf a share tas,

Sallama sukayi, yayin da umman tawa ta basu izinin shiga, kai tsaye suka cusa kansu cikin ɗakin namu da babu wadatar abubuwa.

Miƙewa nayi ga barin karanta littafin *Jinnul Ashique* (na Harira ƴar fillo) domin littafin ya tafi da hankali na akwai tsantsar soyayya da abun al'ajabi da ban mamaki cikin shi, ina ma nima zan samu wanda zai gwada man irin wannan soyayya haka? (zaku iya neman shi ku karanta, zaku same shi online)

Darduma mai ɗan girma na shimfiɗa masu lokacin da nake ficewa a ɗakin, Sam bazan lamunci zama na wuri ɗaya dashi ba, ƙamshin shi, idanun shi, ba ƙarami makami bane da kan taimaka wajen ruɗewa ta ba.

Jikin umman tawa ya duba, Alhamdulillahi sauƙi ya samu sosai, faɗa mata yayi tafiya ta gaugawa ta taso mashi, da fatan dai babu abin da muke buƙata? Babu umman tawa ta bashi amsa sannan ta ɗora da godiya ta haɗa har da Bilal ɗin da tana ganin shi jefi jefi a gidan Amman sai ayi shekaru ma, in ba Al'ameen ɗin na gari ba.

Harda Bilal ɗin a cewa babu komai Allah ya ƙaro sauƙi, kusan ma zamu iya cewa Bilal ɗin yafi gogan naku magana har ma da murmusawa, domin yau ƴan miskilancin na akai.

Miƙewa sukayi suka baro ɗakin, tarin tambayi yi fal acikin ran Bilal ɗin, Amman ba lokacin yi su bane, matar ta burge shi, to wacece yarinyar da ta shimfiɗa masu darduma ta fita bayan ta gaishe su?

Tsafta da ƙamshin ɗakin sun burge shi, abun ya ƙawatar dashi, matar kaman ya santa cikin ma'aikatan gidan fa, amman fuskar tata kaman ta ɓace mashi, any way🤷🏻‍♀ zai tambayi aminin nashi in sun natsu.

Ta inda nake zaune jikin ɗan dandamalin flours suka zo suka gitta ni, tin daga nesa Naji tahowar su ta dalilin ƙamshin Ya Ameen ɗin da ya fara isowa hancina kafin ƙarasowar tasu, sadda kaina kawai nayi ƙasa har suka wuce, bansan barin garin zasu yi ba, wannan ce ta sanya ban masu adawo lafiya ba, kuma koda cen ma ba halina bane yawan tanka ma maza aduk al'amurran da basu shafe ni ba, sai dai ina ƙara ganin girman mutumin da ya kasance mana kaman uban gida ne a gare mu bama mu kaɗai ba, duk wani da ya kwana ya tashi ya amsa sunan ma'aikaci a gidan.

Bilal ɗinne ma naga kaman zai tsaya sai kuma yaga abokin nashi bai tsaya ba, ya wuce kai tsaye zuwa ga motar tashi yana mai kwala ma Idi driver dake cen bisa kujeru dake wajen gate suna fira da mai gadi.

Dagudu ya taso ya wuce ta inda nake zaune, hankalin shi ma bai kai kaina ba, ga motar ya isa yana mai russunawa tare da faɗin "gani yallaɓai" makullin motar ya miƙa mashi yana faɗin "airport zaka kai mu sai ka dawo da motar"

"To" yace yayin da ya amshi makullin ya shiga mazauni driver ɗin, Bilal ɗinne ya shiga gidan gaba, yayin da Al'ameen ɗin ya shiga gidan baya, shiru ya ratsa motar in ka ɗauke ac dake yin aikin ta a hankali a hankali.

Ban jira tashin motar tasu ba, na miƙe a hankali cikin salon tafiyar tawa na nufi sashen namu; ta gefen idanu ya bita da kallo yayin da suke ficewa daga cikin katafaren gidan nasu, shi kau Bilal juyawa yayi ya bita da kallo har suka fice yana ƙissima abubuwa da yawa a ranshi.

Ƙarfe biyar da rabi jirgin nasu ya ɗaga zuwa Kaduna daga cen za'azo ɗaukar su domin ya ma mom ɗin tashi waya tin ƙarfe huɗu da ta turo driver ya ɗauke su.

Shidda da wani abu suka isa, sun tadda driver na jiran su, basu wata wata ba suka nufo gidan nasu kai tsaye, da yake lafiyayyar mota ce sai gashi bayan isha'i da kaɗan sun isa state ɗin tasu ta hauhuwa, (Katsina ta Dikko kenan, garin tudu ɗan marna, ɗakin kara kunya gare mu ba dai tsoro ba)

Mama zuwaira tayi murna da zuwan jikokin nata, masalan Al'ameen ɗin da Bilal dama ta kwana biyu bata ga Bilal ɗin ba, saboda ba yawan zuwa yake yi ba, family ɗinshi duka suna cen ƙasar, har ma da kakar tashi mace tinda namijin ya rasu.

Aiko babu wata wata ta ta sanya masu aikin ta suka shirya masu teburin cin abinci, kala kala, duk da cewa da suke yi sai sunyi wanka sun huta hakan baisa ta kyale su ba, jikin tsufa ya kama ta dole su lallaɓa ta, haka suka ɗan yayyabiɗa sama sama, suka tashi, shi Al'ameen ɗin ma yafi shan coffe da salak ɗin da yaji ƙuli-ƙuli, 🤣kunsan gidan tsofaffi ko da me ƴaƴan su zasu zama, sun fi son abincin su na gargajiya da muhalli su na gado🤣

Da yake shi Al'ameen a nan gidan Alhaji Isuhun yake da part, wannan ce ta sanya basu haɗu da sauran ƴan uwan nashi da iyayen ba daidai zuwa safe.

Bayan sun gama komai ne na al'adar kwanciya a ɗakin da yake mallaki Al'ameen ɗin suka kwanta domin gajiya ta baibayesu na zaman mota ga doguwar tafiya (a cewar su)

Bilal ɗinne yayi gyaran murya yana daga kwance gefen gadon, hakan ce ta sanya Al'ameen ɗin miƙewa zaune yana mai fuskantar abokin nashi, da ya daɗe da Miƙewa zaune shima.

Natsuwar da yaga yayi ce ta sanya shi gane cewa maganar mai muhimmanci ce, hakan ce ta sanya shi tattara dukkan Natsuwar shi shima a kan abokin nashi.

"Bros ina so ne muyi wata magana da tin ɗazu nake so inyi maka ita, Amman na zaɓi nan ne saboda naga yafi da cewa muyi ta a natse"

"Ehen ina jinka friend faɗa man minene kake son ji da baka san shi tattare dani ba"

Al'ameen ɗin ya faɗa yana mai gyara zaman shi gami da jingina bayan shi da makarin gadon.

Bilal ɗinne ya gyara zaman shi daga kan gadon sannan ya cigaba da faɗin "Ina so ne in san wacece matar nan da muka shiga ɗazu sashen ma'aikatan gidan ku muka dubo? Kuma wacece yarinyar da muka tada ɗakin? Menene alaƙarsu?"

Da kallo Al'ameen ɗin ya bishi na tsawon mintina biyu, ganin abokin nashi na so ya ɗauko mashi dogon labari gashi shi kuma bacci yake ji.

Ganin da yayi abokin nashi ya shiga koma ta tinani ne ya sanya shi sake faɗin" kayi haƙuri fa idan na shiga hurumin da ba nawa ba, Amman matar ta burge ni iya matuƙa, sannan bansan dalilin barin yarinyar ɗakin ba lokacin da muka shiga"

"Huh" Al'ameen ɗinne ya gumtsi fuska ya fesar lokacin da yake zamewa ya kwanta akan bayan shi yana rigingine yana kallon pop ɗin dake liƙe sama ɗakin da aka ƙawata da fitili masu matuƙa kyau, sai dai a kashe suke saboda dare yayi bacci suke so suyi, hannun shi duka biyu yasa ya tallafo kanshi dasu yayi matashi, lokaci ɗaya yana mai lumshe ido cikin sanyi halin shi na miskilai, a hankali ya buɗe bakin shi ya shiga furta "Frnd bacci nake ji mu bar maganar nan zuwa safe, ni yanzu tinani na yafi karkata akan dalilin da ya sanya umma ta kiraye ni cikin gaugawa"

Bilal ɗinne ya sauke dukkan ƙafafu nashi ƙasa daga kan gadon yana mai cewa "OK as you wish Bros, Amman ka sani na san halinka, baka komawa kan magana muddin aka yi ta ta wuce kenan, na lura baka son faɗa man ne, ina mai baka haƙuri akan shiga al'amurran ka da nayi, duk da na lura kana taka tsantsan" daga haka ya miƙe gami da shige wa toilet ɗin da yake ta cikin ɗakin.

Tinani da tarabbabi ya sanya Al'ameen ɗin ciki, tabbas bai kyauta ma aminin nashi ba, ya so kanshi da yawa, babu abin da suke ɓoye ma juna, abokan shawarar juna ne, ko wanne hali ɗaya ya shiga suna taruwa ne su warware natsalar su a tare, me Bilal ɗin ke son sani?shima bai san ita ɗin ko wacece ba, bai san umman Suhan ɗin ba kaman yanda ita ma kanta ɗiyar bata san kanta da ko ita wacece ba.

Bilal ɗinne ya fito yana tsane fuskar shi da ɗan ƙaramin towel, yayin da ya isa ga ƴar ƙaramar hangar kusa da mirror ɗin da ya mamaye kusan rabin bango ya maƙale shi cen, ya taka a hankali ya isa ga gadon gami da kwanciya yaja blanket ɗinshi mai taushi ya lulluɓe kusan rabin jikin shi

"Suhan, Umma Maryama"

Abunda Al'ameen ɗin ya faɗa kenan sound so husky, hakan ce ta sanya Bilal ɗin lamo yana sauraren shi, yayin da ya yi tsammani ma bacci ya kwashe shi, domin a yanda ya tafi ya bar shi a haka ya dawo ya iske shi, da alama ma ko matsin kirki baiyi ba, juyowa yayi yana mai fuskantar Al'ameen ɗin daga kwance.

"Nima ban san su ɗin ko su wanene ba," Al'ameen ɗin ya cigaba da magana ba tare da ya jira cewar Bilal ɗin komai ba, to shi ɗin ma baiyi niyyar tankawar ba, saboda ya san halin aminin nashi sarai.

"Shekarar su kusan sha bakwai a gidan namu, wannan baisa a san ko daga ina take ba tare da yarinyar dake hannun ta da take iƙirarin ita ce ta haife ta, sai dai sanin wanene mahaifi yarinyar, daga ina suke? Shine wannan sai ita umman, ciwon da Kaga mahaifiyar yarinya nayi Mom ɗita ce sanadi, wannan ce tasa Kaga ina basu kulawa daidai gwargwado" daga nan ya kwashe komai da ya sani ya faɗa ma Bilal ɗin na dangane da Rayuwar su Suhan ɗin, sannan ya ɗora da faɗin, "Bataso a taimaka masu ne ko alama, bansan minene matsala tata da hakan ba, na sha yunƙurin taimakon ta tana dakatar dani, Abunda na lura dashi ma, dukkan ma'aikatan gidan masalan matan, suna nuna masu wariya da ƙyarar su, Amman hali irin na Umman da take da haƙuri da tawakkali hakan bai nuna wata damuwa ko gazawa koda a fuskar ta ne kuwa, yanzun ma da ta amince da maganar karatun yarinya saida aka kai ruwa rana sannan, kuma ta gargaɗe ni da ɓoye duk wani taimako da zan masu dangane da karatun yarinya, ga dukkan alamu Mahaifiya ta ita ce babbar matsalar matar a gidan"

Dakatar dashi Bilal ɗin yayi gami da tambayar shi "yarinyar fa? Naga kaman bata son mu'amalan tar kowa a gidan ayadda na lura ko mutane ma kaman bata shiga, ka duba tin daga gaisuwar da tayi mana bata ƙara tankwa ba duk da a gaban idon ta muka gitta ta inda take zaune, ƙarshe ma Miƙewa tayi ta koma cikin sashen nasu"

Wannan karin, Al'ameen ɗin ne ya kalli Bilal ɗin ido cikin ido sannan ya shiga faɗin "Oho mata, ita wannan haka take, ban cika kula da al'amurran ta ba, Amman zan iya ce maka irin tarbiyyar da mahaifiyar tata ta bata kenan, bata saki jiki da kowa in ba mahaifiyar tata ba, hakan ya samo asali ne daga wariya da ƙyara daga sauran ƴan uwan nasu ma'aikata" ya faɗa yana mai ɗan taɓe bakin shi, sannan ya juya ya gyara kwanciyar shi gami da karanta addu'ar barci.

Ganin haka da Bilal ɗin yayi, ya san ba zai ƙara tankawa ba kenan ya kuma wuce da maganar kenan.

Shiru yayi shima yana mai hangen bayan kan Al'ameen ɗin da suma ta kwanta mashi luf abinshi, abun ka da farar fata sai yayi kaman wani ba'indiye, ta cikin haske dumlight ɗin da suka sanya mai ɗan duhu sosai kalar shuɗiya.

Shiru ɗakin yayi in banda ac dake aikin ta a hankali a hankali, sai kuma Bilal ɗin dake ta saƙa da warwara, idanun shi ƙyam akan murɗaɗɗen abokin nashi, da tini bacci yayi awon gaba dashi, yana ta sauke numfashi a hankali, a hankali.

Shima dai a haka baccin ya kwashe shi, washe gari duk suka haɗu a nan cikin gidan Alhaji Isuhun da duka nan suke karyawa da iyalan ƴaƴan nasu guda biyu watau Yaya Auwalu da Alhaji Mustapha Dambulan

Sai da kowa ya gama karyawa, har da Bilal ɗin kuwa sannan aka koma babban falon domin sake sabuwar gaisuwa ga iyayen nasu guda biyu da kuma sanya lokacin da za'a zauna meeting da ƙarfe biyu rana, wannan karo harda ƴan uwan nasu mata,watau Gwaggo Aisha da kuma Gwaggo Fatima dake aure nan cikin kankiya da kuma kannen su mata watau Hassana da Hussaina suma duk an masu waya, saboda irin wannan taron babban taro ne da yake ƙara haɗin zumunci da ɗabbaƙa shi, hatta da yaran su matan an kikkira su a waya, tinda ƴan uwan nasu duk sun zo har da waɗanda ke ma'aura ya kamata kowa yazo a gana a kuma ƙara sanin juna.

To sai mu ce Allah yasa ayi taro lafiya a kuma tashi lafiya Alhaji Isuhu family


~Oum-Deedat ce~
[8/5, 8:24 PM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._

*Page ~14~*

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

Zama ne da akan yi duk lokacin da ɗaukacin family ɗin suke nan, wannan ma karon kowa ya hallara, Alhaji Isuhu ne tare da ƴaƴan shi maza suka fara zama, sun tattauna abubuwa masu mihimmanci wanda mafi akasari Yaya Auwalun ne ke zartar da hukuncin, kasancewar shi babba namiji, sai da suka kammala tattauna war su sannan aka umurci kowa da ya hallara a babban falon sashen Alhaji Isuhun, kowa ya zazzauna Amman banda gogan naku, hakan ce ta sanya Alhaji mustapha ɗaukar wayar shi ya kirawo shi tare da umurtar shi da yazo sashen iyayen nasu.

Taro ne da aka buɗe da addu'a bayan zuwan Yaya Ameen ɗin, inda aka gabatar da gaishe gaishe da kuma ƙara sani ga juna duk da dai kowa ya riga ya san kowa.

Alhaji Auwalu ne ya fara da godiya ga Allah subhanahu wa ta'ala, sannan ya ɗora da faɗin, "Ba dan komai muka tara ku anan ba sai dan kuji maƙasudin tara ku anan da hukumci da tsarin da muka zartar, kasancewar kowa ya san ba shawara muke tambayar ku ba, amman dai hakan ba zai hana mu jin naku ra'ayin ba, idan mun gama sanar daku Abunda muka tattauna da shi Alhaji gashi nan" ya faɗa yana mai nuna farin tsohon da yake zaune bisa kujera irin ta alfarma yana ta faman murmusawa da kallon jikokin nashi har ma da surukkan nashi guda biyu watau Hajiya Kubra da Mama Zainab dake zaune ɓangare guda, duk da kasancewar Mama Zainab ɗin babba ga hajiya Kubran, Amman kai kace ita ce babba, saboda jin daɗin da gogewar kai harma da suturar ba ɗaya ba.

"kai Aliyu, munsan buƙatar ka na anema maka auren Khadeeja, wanda mun yanke hukuncin nan ba da jimawa ba zamu je a nema maka auren" ya faɗa yana mai kallon babban ɗanɗan nashi namiji da ya sunkuyar da kai yana ɗan murmusawa, Yaya Auwalun ne ya cigaba da faɗin "sannan ku kuma Saudatu, da Nihal sai Hafsat (Ɗiya ga yaya Auwalun ta uku domin ta biyun mai suna Amina itama tayi aure har ma da ƴaƴan ta guda biyu, kuma itama tana zaune ne a wurin) kuma muna da buƙatar ku turo mana da manema aurenku zuwa gobe ko jibi domin mu tattauna dasu kuma mu basu izini" gabaki ɗaya sunkuyar da kai sukayi yayin da saudat ta zumɓuro baki ita fa bata shirya yin aure yanzu ba, dama Nihal ɗince mai saurayi, sannan ita hafsat dama tana da maneman ta masha Allah kasancewar ta nutsattsiyar yarinya ga kunya da girmama na gaba da ita, kyakkyawa ce masha Allah, domin su Nihal ɗin babu abin da zasu nuna mata.

Dakatawa yayi yana murmusawa tare da cewa idan Alhaji mustapha yana da magana yayi yana sauraren shi, to shi ɗinma cewa yayi babu sauran wani abu sai dai ko a cikin yayyen nasu mata idan da mai magana.

Goggo Aisha ce ta shigo da buƙatar tallafin karatun ƴaƴan nata maza da suka gama makarantar secondry yayin da Goggo Fatima tace ita kam babu abin da take buƙata, duk buƙatocin nata ƙannen nata sun gama mata komai sai Sam barka, tau suma ɗin dai haka Aunty Hassan a da hussainar babu abin da suka buƙata, sai godiya da suka shiga yi.

Yayin da aka tambayi su Hajiya Kubran dake Zaune gefe, Hajiya Zainab dai cewa tayi babu komai, yayin da Hajiya Kubra ta buɗe baki cikin isa, ta shiga faɗin "Maganar Al'ameen fa? Banji kunce komai ba dangane dashi, shima ya kamata ya fiddo mata cikin wannan lokacin, in ba haka ba zan zaɓo mashi da kaina cikin family ɗin ƴan uwa na ko kuma cikin ƴaƴan ƙawaye na" Alhaji mustapha ne ya shiga kallon ta cikin ɗaure fuska yayin da Yaya Auwalun ya shiga girgiza kai a hankali yana ɗan murmushi, kasancewar duk sun san halin ta ne ya sanya abun

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login