Showing 81001 words to 84000 words out of 247770 words

Chapter 28 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10443

ɗin kama ni tsam, duk nabi na tsargu kaina, yayin da su kuma sauran suka ruɗe da ganin ƙirar da Allah yayi mni suna cewa dama su.

Gyalena da takalma na masu tsinci duk blue ne, yayin da siririyar sarƙar dake wuya na ta kasance fari tar ɗin duwatsu da kar ta Orange, lallai munyi kyau, kaman yanda vail ɗina yake blue haka na kowa dake ɗakin namu ya kasance, banda Hafsat da ita kalar golden ne gabaɗaya jikin ta hatta sarƙar gold ɗin dake wuyan ta da Sadeeq ɗin ya zubo mata su cikin lefe kaman ba kuɗi ne ya siya ba.

Masu aiki ne suka leƙo sashen namu gami da faɗa mana mu fito za'a fara cin abincin kaman yanda aka tsara.

Tin daga nesa ake kallonmu, domin dai yau duk hassadar ka ba zaka kushe mu ba haka ma amaryar tamu, runfuna ne guda bakwai kaman yanda aka tanada, Hajiya Kubra, Hajiya Zainab, Kaka Zuwaira da tawagarta, sai ta Saudat, Nihal Da Hafsat ɗin. Kowa da tawagar shi yake zaune.

Hajiya Kubra ce na fara hangowa, saboda wani irin kwarjini da cika idanu da take yi, ta kame ɗaya daga cikin kujerun Alfarmar dake ƙarƙashin haɗaɗɗiyar rumfar tata da taji ado da silkin yadi da balam balam.

Sanye take cikin wani ɗanyen pink ɗin lace anyi mata ɗinkin bubu, wuyan nan nata babu Abunda yake yi in banda walƙiya, haka ma kunnuwan ta da hannayen ta da suke cike taf da zobuna da abun hannuwa na gold

Yau ko gyalen ma babu a wuyan ta, sai ƴan fadan ta da suke zaune kujerun da suke gefen nata, sauran kuma duk kansu kujerun ƙarfe ne anyi masu ado da fararen ƙyalle in ka cire na kaka zuwaira da na Hajiya zainab, sai na amare da suke royal chairs kaman na kamu haka.

Rumfar da babu kowa sai kujeru muka nufa gami da zama idanun kowaa kammu masalan ma ni da bani da alama da ƴar aiki ayau, ba wata wata ma'aikata suka fara serving ɗin mutane, baka jin komai sai ƙarar chokulla, ni kau na kasa cin ma abincin sai juya cokali nake ta faman yi.

Da na ɗaga idanu na kuwa sai su faɗa cikin na Hajiya Kubra, data ƙure ni da kallo tana so ta gano Abunda yaja hankalin yaron nata a jikina, saidai duk iya kallon nata bata gano komai ba, domin in hasken fata ne ko hanci babu kalar wanda yaron nata bai gani ba har cen ƙasashen ƙetaren

Da mun haɗa idanu kuwa zan saurin sadda kaina ƙasa saboda irin kallon tsanar da take bina dashi, sa'a ta ɗaya ummata bata wurin domin dukka ƴan aiki acen sashen nasu suke in abincin, hakan ce ta sanya su zama sashen namu, ita kau ummata ma ɗaki ta shiga gami da kwanciya saboda ta gaji gashi har juwa take ji..

Ƙarfe biyu daidai dubban mutane suka shaida ɗaurin auren Saudat Almustapha da Kamal jamu, akan sadaki naira dubu Hamsin, sai Zuwaira (Nihal) da Nuradden Baffa itama akan sadaki naira dubu hamsin, sannan Hafsat Auwalu da Abubakar Sadeeq Muftee itama akan sadaki naira dubu Hamsin ɗin Sannan na Aleeyj Auwalu da Khadeeja Ibrahim akan sadaki Naira dubu ɗari domin su ne suke da alhakin sanya ma ɗiyar tasu sadaki ba Alhaji Auwalu ba, tinda su cewa sukayi ba kuɗin ke gaban su ba albarka auren da ɗorewa shi suke so.

Bayan kammala ɗaurin auren ne, haka dubban jama'ar suka shaida naɗin ya Ameen ɗin a matsayi *Yariman Matasan Arewa*

Bayan kammala naɗa mashi rawani ne da miƙa mashi sanar girma sai aka lulluɓa mashi alkyabba fara ƙal da surkin royal blue

Tini fa Yariman namu ya Faso, cikin salon tafiyar shi ta ƙasaita, yau kam tafiya ta tabbata, shi ba gadon sarauta ba Allah ya ci dashi, bayan ya kai gaisuwa ne ga dukkanin sarakunan dake wajen mai girma shugaban ƙasa ya mallaka mashi makullin dunƙulalliyar mota ƙirar royce - royce 2019 da lambogini 2019 collection a matsayi kyautar shi shi kuma, nan fa aka yi ta mashi kyaututtuka, fadawan da aka mallaka mashi suna mashi godiya, a haka ya nufo cikin gidan Bilal ɗin na take mashi baya domin zuwa kaima tashi mahaifiyar gaisuwa.

Matasa kuwa ya gansu kowa so yake ya gaida shi, don ma fadawan na buɗe mashi hanya, a haka ya ratso dimbin mutanen nan har zuwa cikin gidan nasu.

Tin daga nesa mahaifiyar tashi ta hango shi, Miƙewa tayi gami da isa wajen shi, baiyi wata wata ba kuwa ya sunkuya ya kai gaisuwa gareta, itama bata yi wata wata ba ta sunkuya gami da rungumo shi cikin ƙirjinta ta miƙe tsaye dashi, sowa aka ɗauka da tafi kowa sun burge shi, yanyameshi aka shiga yi ana ta kai gaisuwa, abokan wasa na yankar shi, hatta da kaka zuwairan da take tafiya daƙyar saida ta taso ta iso gareshi.

Sa hannu yayi ya rungumo ta gami da ɗora mata peck a tsakiyar kai, dungureshi tayi tana mai cewa "ja'iri girma ya hau kanka yanzu saura mata"

Haka yabi yana rungume ƙannen nashi amare da suka kai gareshi Hafsat ce kawai bai runguma ba, saidai ya kamo mata hannu yana mai cewa "Congrat ƙanwa ta" da murmushi ta bishi tana mai cewa " Same Yaya"

Duk yanda dogarawan nan suke kaffa kaffa da daƙunar da ake kai mashi, dole suka haƙura, domin sabon babin ɗaukar hotuna ne aka buɗe kowa so yake ya shiga ayi dashi, masalan dangin Hajiya Kubran da suke ji su wasu isassu ne.

Nikau da nake zaune sai sarkin murmushi nake yi akai akai, domin sun matuƙar burgeni, sarauta yayan namu tayi mashi kyau matuƙa, sai naga har girma kaman ya ƙara da cika ido, sai faman murmushi yake yi, shi kau Bilal bakin nan nashi kaman gonar auduga.

Maida kaka zuwaira aka yi aka zaunar da ita, domin ta gaji sosai gashi shi kin rana suke sosai, domin duk sun baro wurin zaman nasu.

Binshi kowa ya shiga yi da idanu ganin ya sulale ya fara tafiya, ƴar razana nayi ganin ya nufo inda nake zaune, waigawa na shiga yi domin ganin ko akwai wani kusa dani da yake nufo inda nake zaune.

Ganin da gaske yake yi ni yake tunkaro wa ya sanya ni sauke kaina ƙasa ina wasa da yatsun hannuwa na duka biyu, bansan ma me zanyi ba, wane kalar tinani zanyi, gashi dai kowa mu yake kallo.

Hannuwan nawa Naji an kama, bansan lokacin da na miƙe tsaye ba, jana ya shiga yi zuwa wajen mai ɗaukar hoton, saboda tsabar ruɗewa ni kuwa har gyale na yana sumɓulewa, daidai cikin taron jama'a yaja burki ya tsaya, hakan ce nima ta sanya ni tsayawa don dole, uwa ƙasa ta tsage in shige nake ji, gashi kowa ya zuba mana idanu, Hajiya Kubra kuwa kaman idanun ta zasu faɗi ƙasa saboda tsabar yanda ta ƙwalalo idanu tana kallonmu.

*Ke ba zaki zo ki ɗauki hoton bane da mijinki?*

Maganar da ya raɗa mani a kunne kenan daidai lokacin da ya zuƙunna yana mai ɗauko Gyalena daya sumɓule ya shiga yafa mani.

Ai bansan lokacin da na ƙwalalo idanu ina mai Binshi da idanu ba na shiga rufe bakina da hannuwa na ina girgiza kai na.

Ɗaga murya yayi sosai yanda kowa zai iya ji ya shiga faɗin

*Alƙasim ga mata ta ina son ka ɗauke mu ni da ita kaɗai bana son kowa ya shiga in banda amini na Bilal*

Ya faɗa da wani killer smile a saman fuskar shi yana yi yana cije leɓon shi guda ɗaya gami da kafa ma Mahaifiyar tashi idanu.....


🤣🤣🤣🤣🤣



~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._



*Page ~28~*


*A madadin ƴan Banfi ƙarfin ta ba Fans*

Gaisuwa da saƙon ta'aziyya zuwa ga ƙawarmu kuma ƴar uwarmu mai bada goyon baya da ƙoƙarin comment, (Salamatu Muhammad) a bisa rasuwar mahaifinta da tayi, Allah ubangiji ya jiƙanshi ya sanya ya huta y baku haƙurin rashin shi, ya sanya kwanciya hutu ce, ya bashi ikon amsa tambayoyin kabari,ya raya Abunda ya bari yayi masu Albarka Ameen. 🤲🏻


°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

Hajiya kubra wadda ta zabura da niyyar isa wurin da yake tsaye riƙe da hannuwan Suhan ɗin, da sauri Hajiya Sa'a ta riƙo hannun ta, domin ta kula sarai da niyyar hajiyar yanda take fitar da huci kaɗai ya isa ya shaida maka Allah ne kaɗai zai kare Al'ameen ɗin daga marukan da taso zazzagba mashi.

Ganin za'ayi abun kunya ne a wurin Hajiya sa'ar ta shiga jan hannuwan ta zuwa cikin gidan ba tare da kowa ya ankare ba, domin kuwa kowa hankalin shi na kan Al'ameen ɗin da dogarawanshi suka zage suna ta gyara mashi malum malum da take suɓulewa.

Rasa inda zan tsoma rain inji daɗi nayi, lallai wannan maganar tayi man tsauri, ƙwaƙwalwa ta har bana jin zata iya ɗauka, tini naga duniyar na juya mani, duk da hasknn flasher ta ko ina da take ta haske mu, ƙoƙarin zare hannuwa na nake yi domin in samu in ruga, na kula ma saboda tsabar yanda na tsorata numfashina har wani ɗauke wa yake yi.

Gabaki ɗaya hankalin ƴan matan dake wurin ya tashi, waɗanda ma basu kula da ko waceceni ba, son sanin ba'asi suke yi.

Ran kaka zuwaira kwal, lallai yau kowa ya shaida Al'ameen ɗin akwai wacce yake so, mutane da dama zasu dena yi mashi kallon mai ɗaga ma ƴan mata kai, saidai ita ɗin wannan wacece?

Daga baƙin ƙofar gate, makaɗa da mawaƙa ne da masu kirari suna ta wasa Al'ameen ɗin da mahaian shi, Abie ne ke ta masu ruwan kuɗi fuskar nan taf da fara'a, duk wainar da ake toyawa a harabr gidan ma bai sani ba.

Bilal ne ya zare jiki daga wurin da yake tsaye zuwa sashn Al'ameen ɗin, sannan ya ɗauko waya ya latso lambar Al'ameen ɗin.

Daga cikin Aljihu yaji wayar tashi na vibrating, hannuna ya saki da niyyar ɗauko wayar, ni kau ganin wannan damar ta samu na zare hannuwan nawa gami da nufar sashnn namu kai tsaye harda haɗawa da ƴar sassarfa.

Ganin Bilal ɗinne ya sanya shi ɗan juyawa bai hango shi ba, domin shi dai ya san tare suka shigo gidan, to ina kuma ya nufa? Bai ɗaga ba har ta katse, yana ƙoƙarin bin kiran wani ya sake shigowa ɗagawa yayi sannan ya kara akunne

"Malam wai me kake yi ne haka? Menene dalili ka nayin hakan? Baka gudun kaja ma yarinyar wata matsala kuma? Ka saki yarinyar mutane hakanan, kuma ka shirya amsar hukunci daga wajen Mom domin ba don Allah ya tsare ka ba an janye ta da kasha maruka a gaban bainar jama'a"

Bilal ɗin ya faɗa ta ɓangare ɗaya, shi kau gogan kasaƙe yayi da wayar har bai a san Bilal ɗin ya kashe ba, ƴar dariya yayi mai cike da yaƙe lokacin da yaji "ƴaƴan Goggo Fatima na yankar shi wai dole sai sun ɗauki hoto dashi tinda amaryar tashi mai kunya ce ta gudu, shi kau da baya da kunya dole ya tsaya.

Ganin da yayi zai ɓata ma kanshi lokaci ne wajen ɗaukar hoton ya sanya shi juyawa kai tsayezuwa ga sashen nashi, baya ma jin yunwa, ko da yana ji kuma baya tinanin ma in zai iya kai wani abu bakin shi.

Daga bakin ƙofa dogaransuka ja suka dogare, kai tsaye ya kutsa kanshi har cikin bedroom ɗin nashi inda ya tada Bilal ɗin nata faman kaiwa da komowa.

Da ƴar sassarfa ya isa inda Al'ameen ɗin ke tsaye, cikin ɗan ɗaga murya ya shiga faɗin "me kayi haka ne? Hakan da kayi kana ganin daidai ne? Kana nufin zaka ja da mahaifiyarka ne? Ta wanna sigar ya kamata ka ɓullo ma Al'amarin?" ya ƙarshe yana mai zagaye Al'ameen ɗin ya nufi jikin window ya tsaya ba tare ma da ya san ya isa wurin ba.

Yana tausaya ma abokin nashi, Abunda zai je ya komo baya hasashen idan zai zo ma abokin nashi da sauƙi, amsar shi kawai yake jira, saidai jin Al'ameen ɗin bai tanka bane ya sanya shi juyawa domin yaga halin da abokin nashi yake ciki.

Shi kau ta ɓangaren shi, duk da kalamnn abokin nashi sun Dakar mashi zuciya kuma ya jisu har cikin ƙwaƙwalwar shi hakan bai sanya yaji ko ɗar a cikin zuciyar shi ba, karaya da wuri ba nashi bane ba, wannan karon dole ne ya nuna ma magulmata cewa hassadr su da baƙin cikin su babu inda zasu kai su sai fagen nadama.

Takawa ya shiga yi har zuwa gaban gadon nashi, har yanzu bai ko tanka ma abokin nashi ba,baya so ne ya kai shi ga faɗin dukkan Abunda ke cikin zuciyar shi a fili, shi yafi so saidai kawai aga yana aikatawa.

"Kanajina malam kayi mani banza, wato baka ma da lokaci na ko? To inaso ka sani dukkan Abunda ya taso kar a ƙasa ran zaka tunkaro ni ka samu mafita, maganin kar ayi to fa kar a soma"

Bilal ɗin ya faɗa sannan ya juya da niyyar barin ɗakin.

Al'ameen ɗin da yake ta ƙoƙarin cire kayan nashi domin ya watsa ruwa, barin cire kayan nashi yayi sannan ya juyo a hankali yana faɗin "Dakata Malam"

Dakatawa bilal ɗin yayi ga barin ɗakin da yayi niyya.

A hankali Al'ameen ya shiga ta kowa kaman mai jin tausayin ƙasa, har zuwa inda bilal ɗin yake tsaye, a hankali ya sanya dukkan hannuwan shi ya dafa ka faɗar bilal ɗin, sannan ya shiga faɗin

"Ni Moh'd Al'ameen nine mazinaci, fasiƙi mai neman yarinya da lalata har cikin ɗaki na, ni take tallata ma kanta ni kuma nake biye mata alhali ina cikin hankali na...."

Bilal ɗinne ya dakatar dashi ta hanyar sauke dukkanin hannuwan da yayi amfani dasu wajen dafa kafaɗar bilal ɗin

" Dakata Friend, kana cikin hankalina kuwa? Kasan me kake faɗa? Ya zaka dinga jifar kanka da waɗannan mugayen kalaman? Ko dai ka fara shaye shaye ne ban sani ba?"

Bilal ɗin ya faɗa cikin ɗaga murya, ga dukkan alamu kalaman abokin nashi sun ɓata mashi rayuwa gabaɗaya.

" Na sani Bilal, na san me nake faɗa, kuma waɗannan magangannn ba daga bakina suka fito ba, daga bakin mahaifiya ta suka fito, and kuma bansan wanene ya faɗa ba, shine naga tinda har neman yarinyar akeso inyi to zan fa nema ɗin Amman ba ta hanyar da su suke nemana da ita ba, ta hanyar da shari'a tazo mana da ita, watauta hanyar *Aure*"

Ya faɗa shima cikin ɗan ɗaga murya kaɗan, saidai Sam na bakin ƙofa ko na cikin falon ba lallai ne ya iya jiyo Abunda yake faɗa ba.

" Huh"

Bilal ɗin ya sauke ajiyar zuciya mai matuƙar ƙarfi, a hankali shima ya shiga takawa har zuwa gaban gadon, daɓas ya zauna yana mai dafe kanshi da yake sara mashi uwa zai rabe gida biyu, wannan shine dalilin rashin lafiyrr abokin nashi? To indai haka ne munafukan na acikin gidan, lallai tausayin abokin nashi da na yarinyar da ake neman a laƙaba ma sharri bata ji ba bata gani b ya tsira mashi har cikin zuciya.

Sake miƙewa yayi gami da isa ta inda abokin nashi ke tsaye ya haɗe kai da bango yana ta faman maida numfashi yayi, da dukkanin alamu ɓacin ran nashi ya sake komawa sabo fil a cikin zuciyar shi.

Da dukkanin hannuwan shi yayi amfani wajen kamo abokin nashi har zuwa lokacin da ya zaunar dashi bisa gadon nasu, shima zaunawa yayi a hankali, shi ya ma rasa tinanin me zai yi a ranshi, llai abokin nashi na buƙatar wanda zai taya shi wannan yaƙin da ya tunkaro ka, ace wai a wurin aiki baka samu matsala ba sai a cikin gida.

Ummata da take kishigiɗe bisa darduma, gama sallar ta kenan ta jawo cesbaha tana ja idanun ta a lumshe, tsulum na faɗa ɗakin namu ina ta faman haki, ni ban ma san umman tawa na cikin ɗakin ba, ai da bari nayi sai na saisaita kaina sannan in shiga.

Da hanzarin ta ta tashi tana mai cewa "ke lafiyar ki kuwa? Ko wani abu ne ya same ki? "

Ganin ban bata amsa ba ya sanya ta ficewa da niyyar zuwa taga menene yake faruwa, saidai bata fahimci komai ba, saboda ko da ta isa wurin mutanen ta tadda wasu suna ta faman cin abinci yayin da wasu ke ta faman ɗaukar hoto da Al'ameen ɗin. Hakan ce ta sanya ta dawowa zuwa ɗakin gami da share ni ta cigaba da laziminta, in na matsu na faɗa mata Abunda ya tashi hankalin nawa.

Ban gama warwarewa ba sai ga Hafsat da Afnan sun shigo cikin ɗakin, cewa sukayi in biyo su muje ko suyi mani tonon silili wurin umman tawa. Ba arziƙi na miƙe gami da yafa mayafi na na bi bayan su, ina kula da Afnan wacce take Ƙunshe dariya a cikinta. Da kallo umman tawa ta bimu tana kaɗa kai, koma miye in tayi wari taji.

Masifa da bala'i ba kalar wanda Hajiya Kubran bata sha ba cikin ɗaki, haƙuri suka dinga ɓata, kada ta ɓata taron bikin nan DON Allah, da ita cewa ma tayi aje a sallami kowa tinda an gama cin abincin.

Shawarwari ba kalar wanda ba'a bata ba, daƙyal suka samu tayi haƙurin zuwa dare ayi wacce za'ayi, cikin gidan zata ga mai zaman wani a cikin su ko ita ko su, lallai wannan aikin asiri ne tsab, kenan ma Abunda aka faɗa ɗin ya tabbata gaskiya ne, inko hakane wallahi Sam ba zata saɓu ba bindiga a ruwa.

Abunda ya faru ɗin sai ya sanya ƴan ƙanannn maganganu

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login