Showing 138001 words to 141000 words out of 247770 words

Chapter 47 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10464

baya yi, saidai ta bar hakan da ko gajiya ce da yayi.

"Son ka ƙarasa part ɗinka kayi wanka ka huta ko, zan sanya maree ta kawo maka abinci yanzu, kaman na san kana hanya na sanya ta jiya ta gyara ɗakin."


"No mom, bana buƙatar komai, kada ki aiko ta, bana son yarinyar nan na shiga man sashe" ya faɗa yana mai miƙewa da niyyar wucewa.

"OK ita ce baka so tana shigar maka ko? Da yake ba waccen koɗaɗɗar bace ba ko?

Ta faɗa tana mai bin shi da kallo, cikin matuƙar ƙuluwa, to saidai da yake ƴar duniya ce ta ƙarshe, bata bari hakan ta bayyana ba akan fuskar ta.

Ɗan murmushin gefen baki yayi, yana mai wucewa zuwa ga fita kai tsaye. Ɗann kaɗa kanshi yake yi da makullin da yake hannun shi, yana rayawa a cikin zuciyar shi "Mom kibar ma wannan maganar ta kusa zama surukar ki da izinin Allah" ya faɗa a fili yana mai idasa ficewa daga sashen nata.


Koda ya isa ɗakin nashi, bai iya yin wankan ba saida ya kira Alhajin nasu domin yaji ko yana ina yaje ya same shi.

Da mamaki Alhajin ke tambayar Son ɗin nashi yana ina ne.?

Cemashi yayi yana gida.

Cikin mamaki Alhaji Mustapha ɗin da yake zaune a guest House ɗin nashi shi da Bilal yake ce mashi ya zauna gida gasu nan zuwa shi da Bilal.

Sai da gaban shi ya faɗi jin an ambaci sunan Bilal ɗin, amman dai koma miye zai tsaya yaji wane uziri zai bashi kuma.


**********************



Har washe gari bana da wata walwala, haka kawai sai in tsinci kaina da wata irin muguwar faɗuwar gaba.

Ban san dalili ba, sai ga hawaye na shatata a idon nawa, alhali ba wanda yace man komai, hasalima su Raihanan na lecture.

Ban ƙwari kaina ba, nayi mai isata, sannan naje na wanko fuska ta, bansan dalilin kukan ba, kuma ba zance ga dalili ba.

Wata yarinya ce tayi sallama ta kawo mani wayata wai inji Sir Salim yace tace man zai kira in amsa mashi.

Da "To na bita, yayin da ta juya tana mai ficewa.

Komawa nayi na kwanta lamo bisa gadon nawa.

Ilai kuwa sai ga wayar shi ta shigo, har ta katse ban ɗaga ba.

Sake kira yayi, cikin kasalar jiki na ɗaga kaman bana son yin magana.

" Assalamu Alaikum" na faɗa murya ta cen ciki sosai.

Daga ɗaya ɓangaren ya amsa mani.

"Good morning sweet heart"

"morning Sir"

Abunda na iya bashi amsa kenan, ina mai jan bakina nayi shiru.

"Dear ta ko baki lafiya ne? Naji muryar taki cen ƙasa"

"Lafiya ta lau"

Na bashi amsa, har yanzu muryata bata fita sosai.

"me ya hana ki attending lecture ɗita yau? Gashi har nayi accesment"

Ya faɗa daga ɗaya ɓangaren.

"Hummm" kawai na samu zarafin ce mashi. Bai gaji ba ko nuna ƙosawa akan rashin amsa mashi sosai da banayi, ya sake cewa "Sweat Heart ko nayi laifi ne?uhm idan nayi laifi ne a yafe mani, in kuma maganar nan ta jiya ce, ki barta kawai ni na janye tambayoyin nawa, bana son abunda zai kawo mana matsala a tarayyar mu, inaso ki fahimceni, ni ba zargin ko wani abu nakeyi ba, kawai dai tsabar sonki da kishin ki ne nakeyi, amman tinda kince yayan ki ne abarshi a haka, ina fatan na wanke kaina yanzu?

Ya faɗa yana mai sakin ɗan murmushi da yake al'adar shi ce


Wata irin kunya ce ta kama ni, idan ma laifi ne ni na san nice nayi, kuma nice na cencenci in bashi haƙuri, ba shine ya cencenci ya bani ba, ko ba komai babu wani laifin da yayi mani. Tabbas nuna kishi akan abunda abunda kake so ba haramun bane, hasalima hakan sunna ce mai ƙarfi. Kuma ko ba komai yanzu ne na tabbatar da haƙiƙanin son da Sir Salim ɗin yake mani.

Shikau gogan Ya Ameen isa da mulki ma ba zasu bari ka fahimci haƙiƙanin Abunda yake zuciyar shi ba, harda wani ce mani ma wai ga dukkan alamu ban iya gaisuwa ba, kuma ma wai ba wurina yazo ba, to sai kace ma kiran shi nayi.

Gashi ina zaman zama na, duk da naji daɗin ganin shi, ko ba komai na san wata waraka ce ta sake dawo mana a karo na uku a rayuwa, tinda samun Sir Salim itace waraka ta biyu da muka samu a rayuwar mu, duk da yanzu ma zan iya cewa Alhamdulillah babu Abunda Sir Salim da mahaifiyar shi Hajiya Khaltum suka rage mu dashi.

Amman gashi zuwan nashi yana neman dagula mana lissafi gabaki ɗayan mu, to ko in yaje gidan namu ma mai zai ce ma umman tawa?

Jin nayi shiru ne har yanzu bance mashi komai ba, ya sanya shi sake cewa "Hello Jaan kina juna kuwa. Ko sai nazo ne lallashi?"

Ƴar ajiyar zuciya na sauke ina mai faɗin "Ina jinka Sir, komai ya wuce, nima kayi haƙuri idan na ɓata maka"

Dariyar jin daɗi yayi, domin gaskiya jiya ko barcin kirki bai samu ba, wayar ta ita ce ma ya rungume yayi bacci, yana mai shinshino ƙamshin ta ta jikin wayar.

Koda sukayi waya da Ammi taji yanda muryar shi take kaman ba'a daidai ba, ba irin tambayar da bata yi mashi ba, amman bai faɗa mata ba, baya so taga kaman Suhan ɗin na wahalar dashi ne, kada ta fara wani tinani daban, sanin irin son da takeyi mashi, kuma bata son dukkan wani abu da zai taɓa mata tilon yaron nata.

Saidai ko da bai faɗa mata ba, ta fahimci wani abu, faɗa ne dai irin na masoya ba'a shiga, tana zaman zaman ta za'a ce mata an shirya.

Dariyar jin daɗi ya kuma saki, nan ya shiga jana da fira, da labarin ban dariya, har saida yaji na dara, na saki jiki kuma mun cigaba da fira.

Na daga cikin abunda kan ƙara sanya ni amincewa da Sir, Salim ɗin, na san banyi zaɓen tumun dare ba, komin yanda bana cikin walwala ko nake cikin damuwa, indai zan biye mashi muyi magana ta minti biyar, to duk hanyar da zai bi yaga na saki jiki, kuma na dara sai yabi, mutum ne mai barkwanci, gashi mutum ne mai sanyin hali, sam baya da damuwa, lallai matar shi ba ƙaramin asara tayi ba, irin su Sir Salim ɗinne baka fatan ya faɗa son wata, saboda komin yanda budurwa ta kai da jin kai ko jan aji idan ya fara sonta, ya san ta duk yanda zaibi ya shawo kanta, ta faɗa tsananin son shi tsundum, harma in suka samu saɓani ta shiga damuwa, saboda zata rasa wannan barkwancin nashi koda na yini guda ne.

Bai kashe ba, har saida yaji alamun na warware, kuma yaji maganar su Khadeeja a ɗakin alamun sun shigo.

To baya son yana fira dani sosai a gaban su, ko ba komai dai su ɗaliban shine, kuma ba wani sanin haƙiƙanin halin su yayi ba, gudun halin su na ɗalibai yake kada aje ana yayata shi,ko ba komai yana gudun wulaƙanci da surutai daga wurin ɗalibai.

Kuma gashi da akwai waɗanda suke son shi da jin haushin shi, jira kawai suke wani abun magana ya ɓullo daga ɓangaren shi a cigaba da yayatawa, saboda kawai yace yana son Suhan ɗin kuma da aure.

*To dama haka rayuwar ta gada, abincin wani gubar wani,duk yanda ka kai da tarin masoya dole ta ɗaya ɓangaren a same ka da maƙiya, fatan mu dai a rayuwa shine Allah yayi katangar ƙarfe mai ƙwari tsakanin mu da maƙiyan namu, ta yanda saidai su dunga hango bayan mu cen nesa dasu. Ameen*


*************************


Har yayi wanka ya shirya cikin riga fara ƙar mai samfarin amless da wando tree quater mai ruwan ƙasa sosai wanda ya ciza, yayi kyau matuƙa, kaman a ƙasar waje yake. Sai tashin ƙamshin nan nashi mayatacce yake yi.

Harabar gidan ta ɓangaren ɗaya inda akayi wani ɗan ƙaramin lambu shimfiɗe da grass carpet tsanwa shar da ita, ga wani ni'imtaccen ƙamshi da yake tashi ta jiki fulawoyin da aka yima wurin ado dasu. Zama yayi bisa wata kujera mai kyau da akayi da zallar duwatsu, harda ɗan table a tsakanin kujerun shima na duwatsu ne.


Ɗan lemon power horse ne a hannun shi riƙe yana ɗan sipping a hankali, hankalin shi kacokam na kan wayar da yake ta latsa wa. Motar tasu ta shigo gidan a guje.

Da kallo ya bita, har zuwa lokacin da tayi parking kusa daf da sashen Alhaji Mustaphan.

Bilal ne ya fito a mazaunin dreba, sai Alhaji Mustapha da ya fito daga kujerar baya.

Ɗan tsayawa yayi yana kallon yaron nashi da ya taso yana nufo ta inda suke tsaye.

Gaban Bilal ne ya cigaba da faɗuwa, ta yanda zai haɗa idanu da abokin nashi kawai yake yi.

Ƙarasowa yayi, yan mai ɗan duƙar da kanshi ga Alhajin nashi ya shiga gaida shi cike da girmamawa.

Sannan ya juya yana mai kallon Bilal ido cikin ido, miƙa mashi hannu yayi ba tare da yace komai ba.

Ko bai faɗa ba, kallon tuhuma ne yake yi ma Bilal ɗin, kuma shima ya fahimta, to saidai sanin da yayi ne cewa Al'ameen ɗin bai san komai dake faruwa ba, indai ba bayan ya dawo bane ya sani.

Amman a majiya mai tushe ai an sanar dasu cewa bai ko zo gidan ba, kenan dai ba wannan ce ta kawo shi ƙasar ba.

Alhaji Mustaphan ne ya jawo hannun shi, yana mai faɗin

"Muje ciki ka amshi hukuncin wahalar damu da kayi nida abokin naka wajen neman ka"

Duk da cikin ƴar zaulaya yayi maganar, Amman saida abun ya nasheshi a cikin zuciya, to ta yaya akayi suka san yana ƙasar da har ma suka ce ya wahalar dasu wajen neman shi?

A haka ya shiga bin Dad ɗin nashi, Bilal ɗin na bayan su har zuwa cikin tanƙamemen falon Alhaji Mustaphan daya kasance girma ɗaya ne sashen nashi ɗana Hajiya Kubra. Wanda daga baya ne aka ƙara faɗaɗa sashen Alhajin tinda ada bai kai na Hajiya Kubran ba.


Bayan sun zazzauna ne, Alhaji yace Bilal ya miƙo mashi lemo a cikin fridge.

Lemon roba na 5alive Bilal ɗin ya ɗauko haɗi da cup, ya ɗora a bisa wani ɗan trey mai kyau da ƙyalƙyali.

Saidai fa duk yasha jinin jikin shi, yanda ya kula da duk abunda yake yi hankali da idanun Al'ameen ɗin na akan shi, yana mashi wani irin kallo cike da tuhumomi kala kala.

Bayan ya zuba mashi Lemon ne ya miƙa mashi, kujerar da Ya Ameen yake kai ya koma shima ya zauna, yana mai ɗan sadda kanshi ƙasa. Ya san halin mutumen nashi sarai da shegiyar zuciya ta tsiya, ga zafafa abu idan ya faru ko da kuwa ace ba da son ran mutum ba, saidai shi zai yi ƙoƙarin ganin yayi controlling ɗin kanshi koda kuwa ace shi Al'ameen ɗin ya hau, ta yanda zasu fahimci juna, kuma su fuskanci koma menene a tare.

Gyaran murya Alhaji Mustaphan yayi cike da dattako, bayan ya kurɓi ruwan lemo da ya wadata da zallan lemon zaƙi.

"Son Meyasa kayi haka? Me yasa ka taho ba tare da ka sanar dani ba? Takamaimai ma ina son sanin abunda ya sanya ka baro ƙasar ka taho ba tare da sanar damu ba"

Ɗan guntun murmushi yayi iya leɓo, shi ba maganar da yake so ayi ba kenan. Shi ba abunda ya kawo shi ba kenan, beside ma yana ganin ya girma ya kawo ƙarfin da zai iya zartar ma da kanshi hukuncin abunda ya dace dashi, ba don ma iyaye na iyaye ba.

Bai ce ƙala ba, sai ma duƙar da kanshi da yayi ya shiga wasa da hannun shi alamun ba maganar yake son ayi ba.

Abun ka da ɗa da mahaifi, tuni Alhaji mustaphan ya gane abunda yaron nashi ke nufi, tun yana yaro wannan itace alamun da yakan yi idan baya son maganar da akeyi mashi.

Ɗan murmusawa yayi yana mai gyara zama, sai kuma ya saki gyaran murya yana mai ɗan kai kallon shi kan Bilal ɗin alamun za'a shiga daga fa!

"Al'ameen ya zuwa yanzu dai na san ka fahimci me yake faruwa a cikin gidan nan, tinda Allah ya kawo ka, Bilal yaƙi sanar da kai ne a bisa umurnina, nima kuma nayi hakan ne saboda rashin lafiyar taka da kake fama da ita, to saidai fa yanzu haka cikin binciken inda suka shiga muke, muna fatan zaka yi mana uzuri"

Bai katse Alhajin nashi ba, har saida ya kai aya, sannan ya muskuta, yana mai cewa


"Dad duk naji wannan, kuma na ga su to saidai nima ina da Alfarma guda ɗaya, wannan karon bada wasa nake ba, ba kuma zan koma nace na janye maganar ba, sannan inaso ayi dukkan abunda za'ayi cikin lokaci, sannan bana so a tsaya sauraren Mom, tinda dai nine mai yi, kuma nace zanyi ɗin."


Alhajin ne yake kallon Al'ameen cikin matuƙar mamaki akan fuskar shi.

Shima Bilal ɗin dukkanin idanun shi da hankalin shi na akan abokin nashi.

Bai tsaya sauraren suba gabaki ɗaya, ya cigaba da cewa

" Dad inaso in ƙara sanar da kai cewa inaso a nema man auren Suhan a karo na biyu, ba zan janye ba, ba kuma na faɗa bane wannan karon saboda tausayi ko wani abu ba, *Ina Son ta ina ƙaunar ta* nine zan zauna da ita, bana son Mom ta san abunda yake faruwa, saboda bana son ta rikita mana abun akaro na biyu"

Gabaki ɗayan su su biyun, babu wanda gaban shi bai ruguje ya faɗi ba, ya ana mashi maganar ba'a gansu bama, shi yana maganar a nema mashi auren ta? To ina za'a nema mashi auren? Wajen wa za'aje a nema mashi?

"Son ana maka maganar ba'a gansu ba fa, ba'a san inda suka shiga ba, amman ana kan binciken inda suke ɗin"

"Dad naji dukkan bayanin ka, kuma nace na gamsu, saidai Dad kasan garin masoyi baya nisa. Ni na gano su, na gano inda suke kuma naje har inda suke, infact ma daga inda suke nake"

Baki Alhaji Mustapha ya buɗe yana sauraren shi, sai bayan har daya kai aya ne Alhajin ya dunƙule hannu ya watsa mashi daƙuwa cikin ɗan mamaki haka, Shikau gogan sai ma sunnar da kanshi da yayi, yana mai sakin ɗan murmushi, duk da shima sai bayan daya faɗi kalmar sannan kunya ta kama shi. Saidai a fannin so, masalan ma shida yake sabon shiga a soyayyar yana ganin babu gaban wanda ba zai iya faɗa ba.

Bilal wanda bai san lokacin daya buɗe baki ba, yana mai miƙewa tsaye, Al'ameen ɗinne yayi mashi wani kallo na ai sai ka zauna ko!

Zama yayi cikin sanyin jiki da mutuwar jiki. Lallai soyayyar Abokin nashi ga Suhan ɗin daban take, kuma daga Allah ce, tausayin shi matuƙa ne ya kama shi, yana mai jin cewa wannan karon zai mara mashi baya akan komai har ya kai da samun abunda yake da muradi. Duk da shima ta ɓangare ɗaya na zuciyar shi, yana kwaɗaita mashi suhan ɗin, kyawawan halayyar ta, da tarbiyyar dake gareta sukan ƙara mashi ƙaimi wajen ganin ta zama mallakin shi. Saidai ba zai taɓa iya cin amanar abokin nashi ba, masalan ma yanzu da yaga ya tsunduma tsulundum a soyayyar ta, ya zama wajibn shi, tilas ɗinshi yaso abunda Aminin nashi keso.

Shiru falon ya ɗauka kusan na minti biyar, kowa da abunda yake saƙawa.

Sai cen Alhaji Mustaphan ya nisa yana mai cewa su tashi suje, yaji dukkanin bayan an Al'ameen ɗin kuma zai duba akan su, sannan zai shawarci Alhaji Auwalun akan komai, saboda baya yanke hukunci karon kanshi sai ya shawarci yayan nashi da kuma mahaifan shi.


(Abunda masu kuɗin mu na yanzu basa yi kenan, suna ganin tinda Allah yayi masu nasibi ko luɗifi ba zasu iya bin kowa ba, su saidai a bisu, kuma basa jin zasu iya neman komai a wurin wani, bayan ba haka rayuwar take ba, gabaki ɗayanta ita rayuwa juyawa take, idan babu masu kuɗi babu talakawa, haka idan babu talakawan babu masu kuɗin, kowa na buƙatar kowa a sha'ani na rayuwar yau da kullum)


Miƙewa sukayi gabaki ɗayan su suna mai ficewa zuwa sashen Al'ameen ɗin.

Saidai fa babu mai cewa da kowa komai, har suka shiga sashen nasu.

Ganin da Bilal ɗin yayi Al'ameen ya share shi ne, ya sanya shi jawo hannun shi, yana mai maido shi baya.

"Kai don Ubanka laifin me na aikata maka haka ne da har kake mani wani shariya? Kasan irin wahalar da nasha wajen nemo maka budurwar taka? Ko kasan har America naje in sanar da kai gaskiya ba tare da sanin Dad ba, ganin kada in biye ma Dad ka cutu, Amman shine ka dawo kana ta wani basar dani. Pls kayi mani magana mana ko Naji sauƙi"

Ɗan ɗaura mashi idanu yayi, ganin ya idashe maganar tashi cikin damuwa da take har cikin zuciyar shi.

Ɗan zare hannun shi yayi yana mai wucewa, sai kuma ya dawo da baya ya dunƙule hannu ya kaima Bilal ɗin naushn wasa yana mai rungume shi yake faɗin "Komai ya wuce Friend, ai nace na gamsu da dukkanin bayanan da Dad yayi ne, dama don inga yanda zaka yi ne don Ubanka" ya faɗa cikin yalwatacciyar fara'a da yake jinshi saƙat tinda ya samu Dad ya faɗa mashi damuwar shi da dukkanin buƙatar shi.

Shima Bilal ɗin rungume shi yayi yana mai faɗin "kaji shegen bisa, ashe dama hawan ruwana ne kake so ya tashi, to kada dai ka karya ma Ummi ni, saboda kasan fa na kusa zama Dad"

Da mamaki Al'ameen ɗin ke kallon shi,

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login