Showing 180001 words to 183000 words out of 247770 words

Chapter 61 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10451

da yake tsaye jingine jikin mota, kaman an dasa shi, mu kawai ya zuba ma idanu.

Ganin inda nake kallo ne, ya sanya shi shima maida idanun shi wurin.

"Oooh! Wancen shine saurayin naki da aka je nema mashi auren matata jiya?"

Ya faɗa cikin I dont care tune.

Sadda kaina na kuma yi ƙasa ba tare da nace mashi komai ba.

Salon da yayi ya matuƙar burge ƴan matan dake tsaye, kowacce tana fata da burin ina ma ace ta mallaki ya Ameen ɗin.

Tsaye sukayi suna mai more ma kallon shi, wanda suke gani a gidajen talabijin yau shine a zahiri a cikin makarantar tasu.

Tsam naga ya miƙe yana nufar inda Sir Salim ɗin yake tsaye.

Hannu ya miƙa mashi sukayi musabaha.

Sai kuma yace "kaman naso in gane ka ko?"

Da mamaki Sir Salim ɗin ke kallon shi, lallai jin kan wannan gayen ma yayi yawa, watau haka dai yake kenan ko a zahiri, lokacin da suka haɗu dashi a library bai kamata ace har ya manta shi ba, da kuma duka yaushe ne suka gaisa dashi ya maido Suhan ɗin makaranta?

"Eh kwarai kuwa ka gane ni, ba kai ne yayan Suhana ba?"

"Eh kwarai kuwa nine. Malam ko?" ya furta cikin salon muryar shi da ba mata ba kaɗai har maza burge su takeyi.

"Sosai kuwa nine"

Al'ameen ɗinne ya sake bashi hannu suka gaisa, kowa da Abunda yake ƙunshe cikin zuciyar shi.

Juyawa yayi ya koma inda ya tashi, baki sake nake binshi.

Lura nayi da dogarawan sun fara korar ɗaliban da suke tsaye suna kallon mu, wanda wasu daga ciki har sun fara fiddo waya suna haska Ya Ameen ɗin.

"Nace zanzo ki shirya ma zuwan nawa, sai gashi kuma na tadda ke a haka? Me ya same ki? Kaman ma kinyi kuka ko?"

Ya faɗa cikin tsattsareni da idanun shi da suke sanya jikina ƙara sanyi.

Ɗan kallon jikin nawa na kuma yi a karo na biyu.

Sai kuma kunya ta kama ni, Amman sai na share ina mai cewa" Yaya daga lecture fa na fito yanzu, to wacce kwalliya zanyi kuma?" na faɗa cikin ɗan narkewa alamun ƴar shagwaɓa.

Da kallo yake bina. Na matuƙar burge shi.

"Bana son Yayan nan, ya zuwa yanzu nasan kin fahimci matsayi na a wajen ki, so don haka ina buƙatar a cenza mani suna"

Ni dariya ma ya bani, Amman bari ayi mashi boko, mugani idan zai iya kubce wa.

"Wanne matsayi kenan yaya? Ban fahimta ba? "

Na faɗa cikin wayancewa.

"au baki gane ba?kina so inyi abunda saisa kowa ya tabbatar da matsayin nawa ne? "

Shima ya faɗa cikin wani salon na basarwa.

Kai tsaye nace mashi "Eh" ban ko rufe baki ba, naga ya nufo fuska ta da fuskar shi, fuskantar Abunda yake niyyar yi ne ya sanya ni ja baya, ina mai faɗin "Nagane yaya, Allah na gane"

Yar dariya ya saki yana mai ɗan wayancewa ya kauda fuskar yana mai faɗin "Matsoraciya kenan, ai naso ki bari har shi Wancen saurayin malamin naki ya fahimta, duk da yanzu nasan ya riga ya janye, mai wuri yazo ai dole mai tabarma ya naɗe"

Da kallon mamaki nake binshi, wai Ya Ameen ɗin da na sani ne da kuwa?

Kaman ba shine ya saki jiki yana zaro maganganu haka ba.

To ada ma idan ance man ya iya magana haka ai bazan iya yarda ba, yo to ai ni kallon miskilanci nake mashi, ashe ba kowa yakeyi mawa ba? Ashe ba a ko'ina yake miskilin ba.

"Anyway ya kamata inyi Abunda ya kawo ni, don naga kin faɗa komar tunani."

Ya faɗa yana mai gyara zaman shi, sai kuma ya ɗan haɗe fuska, alamun maganar ba wasa a cikin ta.

Bai bani damar magana ba, sai ma cigaba yayi da cewa *"All the way from Abuja na taso yau, ba don komai ba kuma sai domin in ganki, bana buƙatar sake tambayar ki amincewa akan batun auren nawa, Amman All what i want is your Love. Soyayya nakeso mai tsafta, Soyayya mai ƙunshe da ƙauna, bana son ƙauyanci fa, zaki ajiye wannan Kunyar taki ne a gefe, saboda ni ban ganin abun Kunyar indai har muna son juna, we have to show it and prove it a gaban kowa, hakan ne zai sa iyayen mu su yarda mun amince da juna. Maganar soyayyar ki tada, ki mance da ita, ki ajiye ta gefe, salon zai cenza ne a wannan karon, I am Al'ameen Almustapha Dambulan as u know, so ba lallai ki iya ganewa ba, Amman zan iya ce maki bansan micece soyayya ba sai akan ki, bansan ya ake yin ta ba, na ɗauke ta shirme ce, na ɗauka sai marasa abun yi ne suke wata abu wai ita soyayya. Amman yanzu duk ba haka bane, na fahimci kuskure tunani na, tin shigowar ki rayuwa ta. Ina Sonki Suhan, zan aureki, kuma zan kasance tare dake a kowanne hali. Da fatan zaki bani goyon baya kema, zan bari kiyi tunani a koda yaushe zaki iya ganin na dawo, domin a yanzu na fahimci cewa garin masoyi baya nisa ko ina yake a faɗin duniya"*

Tabɗiiiiiiii

Ya Ameen ne yau zaune a gaba na, a gaban ɗumbin mutane haka yake faɗa mani irin waɗannan kalaman? Ina miskilancin? Ina sarautar? Ina haɗuwar? Ina izza da kuɗin?

"Duk ya ajiye su a gefe."

Wata zuciyar ta bani amsa.

Idanuna cikin nashi, hakan ne ya sanya ni saurin janye nawa idanun.

Ya Ameen ya haɗu iya haɗuwa, hatta da fuskar shi ba zan iya jure ma kallo ba, balle kwayar idanun nashi.

Kallona na maida wajen da motar Sir Salim take.

Baya wurin, kaman yanda ban ma ji ko tashin motar tashi ba.

A hankali na sauke kwayar idanuna gefe, sai kuma na saki wata nannauyar ajiyar zuciya kaman wadda aka shaƙe sannan aka saki.

Yakai tsawon minti biyar yana kallo na, har saida Naji kallon yayi mani yawa, ga kwayar idanuna tana yawo a ƙasa, kaman wadda take ƙoƙarin gano wani abu.

Wani Ya tafi wani Ya zo.

Ikon Allah kenan.

Lallai rayuwa tana garawa dani kaman garin tayar yaro.

Miƙewa tsaye naga yayi, yana mai ɗan sakin murmushi iya gefen baki, wanda ya ƙara ƙawata mashi fuskar tashi, lokaci guda yana mai ƙoƙarin saka glashin idanun nashi.

"Muje ki raka ni ko?" ya furta a hankali cikin wata irin salon murya, kai kace da wata sarauniya yake magana.

Ban miƙe ba, kaman yanda ban kalle shi ba.

"Kada kisa inyi Abunda zai baki kunya fa"

Ya furta cikin wani irin salo, na san zai iya aiwatar da Abunda ya faɗa ɗin.

Zumbur nayi na miƙe, ina mai kwasar litattafai na, sannan ce "To yaya muje, yi haƙuri"

Ƴar dariya ya saki, muka fara takawa a hankali yana mai ƙara gaya man wasu kalaman da ni fa ina tunanin saida ya rubuta sannan yayi haddar su.

Kai idan ka hango mu sai kace irin masoyan nan ne da suka shekara biyar suna soyayya har aka sanya masu rana.

Ko ba komai ni a wajena jerawa da Ya Ameen ɗin muyi tafiya a bigire ɗaya abun alfahari ne a wuri na, saboda haka sai na dayaye kawai, gudun kada ƴan tsogumi su fahimci halin da ake ciki.

Har bakin motar na raka shi.

Ni na buɗe mashi bayan motar, bai zauna ba, saida ya kalleni da wani irin ƙayataccen murmushi alamun ya gode, sannan ya shiga motar ya zauna yana mai kallo na.

"Nagode Gimbiya ta" ya faɗa cikin salon da ya ƙara sanyaya mani jiki.

Ɗan baya naja a hankali, har yanzu fa mamakin shi bai sake ni ba, Allah gani nakeyi kaman mafarki nakeyi, a hankali ya ɗan ɗaga man hannu alamun bye, sannan yayi salute ɗina, daidai lokacin da motocin suka juya a hankali suna mai barin cikin makarantar.

Tsaye nayi kaman wadda aka dasa, da kallo nake bin motocin har suka ɓace ma gani na, daidai lokacin da su Khadee suka ƙaraso inda nake tsaye khadeen ke faɗin


"wow Suhan wannan gayen kuma fa? Yariman matasa ne fa! Dama kin sanshi ne? Wallahi gayen ya haɗu, ya tafi da imani na, please ki haɗa ni dashi, wallahi lokaci guda son shi ya kama ni, ina yawan ganin shi a instagram, gayen yana da followers sosai wlh ga kuma naira"

A hankali na juyo ina mai maida kallona kan khadeen dake faɗin wannan kalaman.

Ga mamaki na kuma, sai kalaman nata suka bani haushi.

Bance mata ƙala ba, na shiga zagayesu ina mai wucewa kai tsaye zuwa ɗakin namu.

Zuciya ta a cunkushe, saboda na rasa ma tunanin da ya kamata inyi.

_Na tafiyar Sir Salim_

Ko

_Na zuwan Ya Ameen?_


~Toh Fans ga Suhn fa ta shiga ruɗu, ku bata shawara please~







_Please Share_



~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._


*Page ~51~*

*Salamatu wannan Page ɗin naki ne, kaman yanda na alƙauranta, kiyi yanda kike so dashi, kuma a dinga karantawa oga shima. Nagode Allah ya bar ƙauna*


°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°


Kai tsaye ɗaki na zarce, jina fa nake kaman na wani zauce,Ya Ameen? da kanshi?

Bakin gado na samu na ɗan ɗosana.

Sai kuma me?

Tafiyar Sir Salim ke mani kai komo.

Sai kuma hango tahowar Ya Ameen with full confidence.

*"Huh"*

Na saki wani irin huci mai tare da ɗan sauti.

Daidai shigowar su Khadee ɗin.

Gani na da sukayi zaune dafe da kai, ya sanya suka nufi inda nake.

Tsakiya suka saka ni, Khadeen ce ta ruƙo mani hannuwa,sannan ta fara cewa

"Suhan kiyi haƙuri, naga kaman kinji haushi don nace ina son Yayan cen naki, Nidai nasan ba wani abu tsakanin ku, tinda maganar Sir Salim ta riga taje gidan ku, kuma ni ina ganin wannan ba wani abu bane, wanda yace yana son naka ai kai yake so, wallahi ganina dashi na farko naji ya kwanta mani, tin kafin ma in ganshi a zahiri, duk da nasan cewa yanda yake da masoya, sannan gashi da kyau uwa uba yana da kuɗi, kada kiyi tunanin dalilin da yasa nace yayi mani kenan, a'a wallahi ko ɗaya, so ne na tsakani da Allah ya kama ni a take, ki taimaka mani koda number ɗinshi ce, insha Allahu ni zan ganin nayi ƙoƙarin na kafa kaina, duk kuwa da cewa ni kaina nasan ya wuce da ajina. Amman hakanan nake sonshi, koda kuwa zai wulaƙanta ni, haka kuma koda yana da mata uku, wallahi na yarda zan shiga a ta cikon huɗun"

Ban kalle ta ba, saidai tabbas nasan kalaman ta suna ratsa zuciya ta, wani kumbura naji zuciya ta nayi, sai kuma Naji kaman ƙofofin hancina na ƙara buɗewa, kaman iskan da nake shaƙa tayi mani ƙaranci.

Raihana ce ta maida kallon ta kan Ƙawar tata, ita mamaki ma take bata, daga ganin bawan Allah sai ki ruɗe har haka a kanshi?

"Khadee ki dena faɗar haka, sanin kanki ne cewa Al'ameen dambulan har Samira ɗiyar shugaban ƙasa tace tana sonshi ya ƙiya, ke shaida ce, ko a Instagram ma mata faɗa suke akanshi, ke wallahi akwai matan auren da naji suna cewa muddin Al'ameen zai kalle su yace yana so, zasu iya kashe auren su su koma mashi, Khadee kin daɗe kina wannan maganar tin ma kafin ki ga Al'ameen a zahiri, sannan tin ma kafin kinsan yana da alaƙa da Suhana, to don Allah kibi komai a hankali, tinda yanzu kin samu link ɗin haɗuwa dashi, insha Allahu komai zai zo maki dasauƙi"

Har yanzu dai zaune nake dafe da kaina da hannu ɗaya, yayin da Khadeen ke riƙe da ɗayan.

Ganin bam tanka ba ne, ya sanya Khadeen cigaba da magana.

"Raihana kin fi kowa sanin na daɗe da ƙaunar Dambulan acikin raina, ke shaida ce, nasha gwada yi mashi magana a kafafen sadarwa amman ko dubawa ma baya yi, nasan kuma ba ni kaɗai bace, muna da yawa. Suhan please ki taimaka ma Ƙawar ki, wallahi ina cikin wani hali"

Sai a lokacin na ɗaga idanu na na kalle ta, duk tabi ta koma kalar tausayi, lallai soyayya banzar abu ce, raɗaɗin rabuwa da Salim ɗin bai sakeni ba, gashi Khadeen kuma tana tara ta da wata magana ma marar amfani.

To koni dai daya ce yana so ban gama gasgatawa ba, gani nakeyi kaman yana da wani ƙudirin daban, ƙila so yake sai Mom ɗinshi ta yanka ni, ta kakkatsa namana sannan. Ummata ma da tayi aure a gidan don bani da yadda zanyi ne.

Daƙyal na buɗe baki na da yayi mani nauyi na fara cewa.

"Khadee kiyi haƙuri don Allah, ni yanzu ba wannan ne a gabana ba, Al'ameen da kike magana kuma Sam bashi gabana, saboda bana fatan kai kaina inda Allah bai kaini ba, kuma ko ba Salim bana tunanin zan iya yadda da Al'ameen, domin kuwa ni nasan yafi ƙarfi na"

Da mamaki duk kansu suke kallo na, masalan ma Khadee da bata kai ga fahimtar inda zancen nawa ya dosa ba.

"Excuse me Suhan, wai me kike nufi ne da wannan maganar taki? Bamu fahimce ki ba fa"

Cewar Raihana da tsabar mamaki ya cika ta.

Maida kallona nayi kanta.

"Eh Raihana, ina nufin iyaye na basu yarda da maganar aure na da Sir, Salim ba, Al'ameen shine wanda suka zaɓa mani, shine suke so in aura, kuma suna fatan ace nayi masu biyayya, ko wannan zuwan da Al'ameen ɗin yayi, yazo ne wai ya bayyana mani soyayya, Abunda bana tunanin kuwa mai yuwu wa ne"

Zumbur Khadeen tayi ta miƙe daga kusa dani.

"What?, me? Me kike faɗa ne Suhan? Dambulan ne wanda zaki aura? Are u sure? Shine yazo bayyana maki soyayya kika tsaya kina tarabbabi?"

Tana gama faɗar haka ta buɗe ƙofar ɗakin ta fice a sukwane.

Raihana ce ta maido hankalin ta kaina, tin bayan da muka raka Khadeen da kallo.

" Masha Allah Suhan nayi maki matuƙar murna, baki buƙatar wani tunani, ki amince, Al'ameen ba irin mazan da zasu ce suna son mace bane ta tsaya masu yanga ko jan aji, wasu ma neman irin tasu soyayyar suke da kuɗi basu samu ba, ƙaramn musali ki kalli Khadee, yanzu ta zama abun tausayi, ta daɗe tana dakon soyayyar shi, maganar ce dai bamu taɓa yi ba, gashi yau da ta ganshi a zahiri ji take kaman ta bishi, kaman tayi hauka, kinsan da inda kuke zata je ta same ku? Nice na hana ta? Kiyi haƙuri Suhana kibi zaɓin iyayen ki, shi kuma Sir Salim Allah ya bashi daidai shi, Amman wallahi baki buƙatar sai na faɗa maki kunfi da cewa da Dambulan"

Itama kuwa kalaman nata sun ratsa ni matuƙa, to saidai....


Kallon ta nayi, ina mai cewa "Raihana please ki gaya mani ni ba mace bace? Ban kai a soni ba? To ta yaya zai ɓullo da kalmar soyayya a gareni da niyyar cimma wata manufa tashi?"

Da mamaki take kallo na.

"Shi wa?"

Ta tambaye ni.

"ya Ameen" na bata amsa kai tsaye.

Girgiza kai ta shiga yi.

"Ke kanki Suhan kinsan idan ba don soyayya gaskiya bace, to da babu Abunda Dambulan zaiyi dake, kiyi haƙuri ba cin zarafi bane"

"Kin fi kowa sanin irin matan da suke rububi da faɗa akanshi.Sai gashi duk ya tsallake su, ya kawo kanshi gareni, so bana tunanin ma idan har zaki wani tsaya ɓata lokaci wurin amsawa"

Har yanzu fa ina tababa.

Ga wani irin mugun tausayn Sir, Salim dake ratsa mani zuciya.

Bance mata komai ba, na jawo waya ta na shiga neman number ɗinshi.

Bugu uku ya ɗaga, cikin sanyayyar murya yake ce mani


"Suhan baƙon naki har ya tafi ne?"

Ban iya bashi amsa ba, sai ma rumtse idanu da nayi.

Da mamaki Raihanan ke kallo na, bata kai ga fahimtar wanda na kira ba, saida taji ina cewa.

"Am sorry Sir, wallahi ba laifi a bane, kayi haƙuri don Allah"

Cikin wani irin yanayi, shima tausayin ta yake ji, duk da yasan cewa wanda Allah ya bata, ya fishi komai, infact ma ko abota ya samu yayi da Al'ameen abun alfaharin shi ne.

Cikin wata irin murya ya shiga cewa

"I understand Suhan, please dont burder your Self, let the bygone be gone please, bama da zaɓi illa hakan"

Bai kai ga ƙarasawa ba wani irin kuka ya ƙwace mani.

Kashe wayar nayi, ina mai faɗa wa jikin Raihana. Rungume ni tayi tana bubbuga bayana alamun lallashi.

Shi kau ta cen ɓangaren kashe wayar ma yayi baki ɗaya, ko zai samu salama acikin zuciyar shi.

Ba daɗewa dama Ammi ta kira shi ta ƙara kwantar mashi da hankali.

A haka Khadee ta dawo ɗakin ta same mu, Raihana nata lallashi na, da kallon idanun ta kuka tayi, ko ba komai tasan ta rasa Al'ameen ɗin kenan, ashe ma tana rayuwa da wadda zata zama matarshi a ɗaki guda, ba tare da ta san hakan ba. Bata ce mana ƙala ba ta haye gadon ta ta kwanta.





*********


Ƙarfe

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login