Showing 60001 words to 63000 words out of 247770 words
tinanin ko cen ya faɗa.
Gyaran murya yayi a hankali, cak na ja na tsay, in ba kunne na bane yake man gizo, kaman gyaran muryar Yaya Al'ameen ɗin nake iya jiyowa.
Kasa juyowa nayi, kurkusa nake jin shi, kaman ma ya shigo ɗakin, a slow na juyo, aiko idanuna suka faɗa cikin nashi, kasa ɗauke idanuna nayi akan shi, aiko kafe ni yayi da mayatattun idanun shi, wani irin kallo ya shiga bina dashi a hankali ya shiga takowa zuwa inda nake tsaye.
Ja na shiga yi da baya ina yarfe hannu, na shiga uku kada fa ya ɗauka sata na shigo yi mashi, buɗe baki na shiga yi da niyyar kare kaina.
Hannu ya ɗaga man alamar inyi shiru baya son jin komai, kuma har yanzu bai daina matsowa ta inda nake tsaye ba.......
~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
*Page ~22~*
*Wannan Page ɗin sadaukar wa ne ga ɗaukacin WRITERS ɗin Golden Pen, Allah ya ƙara mana ɗauka ka, basira, da zaƙin hannu, Allah kuma ya bamu ikon rubuta Abunda zai amfani Al'umma baki ɗaya. AMEEN*
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Ban dena ja da baya ba ina yarfe hannu, haka shima bai dena matsowa inda nake ba, har saida na dangane da bangon ɗakin, ba arziƙi na ja tsaya ina ta ƙwalalo idanuwa kaman uwar da yaranta suka ɓata.
Daf dani ya ja ya tsaya, har ina iya shaƙo ƙamshi turaren da ke jikin shi, saurin sadda kaina ƙasa nayi, yanda ƙjrji na ke bugawa, har ina jin kaman zuciya ta zata tsago ƙirjina ta fito tsabar yanda take bugawa.
Bai ce man ƙala ba, nima bance mashi ba, sai ma nake ganin dukkan abunda zan faɗa don kare kaina ba yarda zai yi ba, tinda tin farko ya nuna man baya buƙatar hakan.
Hannun shi ya sanya a aljihu wandon nashi gami da ɗauko waren ɗan kunnen nawa da yake ta walwali cikin hasken farin ƙwan dake ɗakin yana ta sheƙi da walwali.
Miƙo man yayi, kaman wadda ƙwai ya fashe mawa a ciki na sanya hannu gami da amsa, duk da yanda zuciya ta ke bugawa, hakan bai sanya murna da farin cikin da nake ciki sun ɓoyu ba daga fuska ta, murmushi na saki, har saida siririyar wushirya ta ta bayyana, fararen haƙora na da suke jere reras ya bi da kallo, lokaci guda yana mai ɗauke idanun shi gami da juyawa yana nufar ƙofar fita cikin salon takun tafiyar shi.
Kaman ance ya tsaya, ya kuwa ja ya tsaya, gami da juyowa, Allah sarki, ta kuwa ƙure warin ɗan kunnen wanda yake cikin tafin hannun ta da idanu, ga dukkan alamu dai taji daɗin ganin abun kunnen, kuma ko babu komai ya ameen ya gane dalilin bincika mashi ɗaki da ya tadda ta take yi.
"Sai ki gyara man ɗaki na tsaf, kaman yanda kika tadda shi" Abunda ya faɗa kenan gami da juyawa ya idasa ficewa zuwa falon.
Da kallo na bishi, zuciya ta na raya man, wai in gyara mashi kaman yanda na tadda, kaman ba nice na gyara ɗin ba😠
Cikin sanɗa ma shiga bin shi a baya, bayan na maƙala ɗan kunnen nawa a mazaunin shi watau kunne na.
Leƙawa nayi falon a hankali, hango shi nayi zaune bisa kujera mai cin mutum biyu, gaban shi da laptop yana ƙoƙarin kunna wa, ga dukkan alamu aiki zai yi cikin ta.
Rufe ɗakin nayi, gami da murza mashi key, a hankali ya ɗago jin ƙarar sanya key a ƙofar, ɗan murmushi ya saki na gefen baki, yana girgiza kai bayan ya kauda idanun shi daga ƙofar ɗakin zuwa laptop ɗin.
Nikau dalili na nayin hakan, ba zan juri in gyara mashi ɗaki harda gado ba, alhali yana cikin sashen kuma mu biyu da gani sai shi, ina ai ba zai yuwu ba.
Gyaran da nayi ma yafi na farko wanda nayi, saboda wannan karon ɗakin ya samu canje canje da nayi, hatta gadon na canza mashi mazauni, da ba a saitin taga yake ba, gashi muna yanayi na zafi, wannan ce ta sanya na maida kan gadon saitin taga, yanda fresh air zata ringa shigowa, zai samu sauƙi kunna ac ɗin da yake yi, wanda kowa ya sani tana da illa ga lafiya ɗan adam.
Ina gamawa, ban jira komai ba, na fito da niyyar ficewa, yanzun ma ban tanka mashi ba, shima bai ko ɗago ya kalle ni ba, duk da yaga gittawa ta, Amman ƴan maganar basa kusa, koma suna kusa me zai ce mata? Yarinyar da ƙiri ƙiri ya nuna bata yadda da shi ba a zahiri.
Ina daf da ficewa na tsinkayi muryar shi yana cewa "Ki kira man Hafsat in kin fita" & an waiwayowa nayi ina cewa to gami da idasa ficewa gabaki ɗaya a part ɗin.
Fita ta ne yayi daidai da fitowar maree daga babban sashen gidan, direct ɗakin Ya Ameen ɗin ta nufa, Nikau da idanu na shiga binta, wasu irin kaya ne ta sanya matsattsu, dinkin ya kama ta sosai, bayan nan kau an wawashe kusan rabi, haka ma gaban rigar, kai abun dai babu kyaun gani, ɗan gyale ne ta yafa wanda dashi gara babu, takalman ta masu tsinci ne, wannan tasanya duk takon da tayi sai ya bada sauti "ƙwas"
Itama bata yi sanya ba ta bini da kallo, mamaki fal a cikin ranta, me naje yowa sashen Yayan ne? Gashi kuma ni kaɗai ta gani, wani wulaƙantaccen kallo ta shiga jefo man, tanayi tana tauna chewin gum tana ƙas ƙas dashi tana farfara idanu tana wata yatsina, ni wallahi sai ma ta bani dariya.
Wucewa nayi ina mai waiwaye ta, lallai kuwa ɗakin ta ke da niyyar shiga, Amman taja ta tsaya tana ƙara gyara zaman riga da skirt ɗin a jikin ta, ikon Allah, yau ina kallon abu, to me zata je yowa sashen nashi a haka?
Har ga Allah dai na san duk da ba'a shedar ɗan mutun, na san shi ya Ameen ɗin bai da wannan ɗabi'ar, kuma ma dai na san ko neman matan zai yi, ba zai tsaya ma wannan ballagazar ba, wanda ko jirin kirki da kyaun kirki bata da.
Ban aune ba naga har na isa ɗakin namu, sallama nayi na shiga, naki yi sa'a umman tawa bata nan ta fita, Hafsat kawai na tadda a zaune tana ta faman yin waya da wanda zata aura, murmushi tayi gami da cewa "Laa gata nan ma muna maganar ta" miƙoman wayar tayi tana faɗin "gata ku gaisa ma"
Amsa nayi ina mai ɗan harararta cikin wasa, alamar ban shirya ba haka kawai ta dunguno man wayar tana dariya shaƙiyyanci.
Ba laifi mun gaisa cikin raha, harda ɗan wasa haka, yana tambaya ta "ya shirye shirye biki, tace yau zaku fara ko?" da eah na bishi don bansan ta kan zancen ba, muka yi sallama yake faɗa man ya kusa shigowa ƙasar zai zo mu ƙara tattauna wa.
Itama ɗin sallama tayi dashi, bayan na miƙa mata, ta ƙagara taji ina na samo ɗan kunnen da ta hanga a kunne na bayan na cire hijab ɗin dake wuya na.
Aikau na kwashe komai na faɗa mata, na ƙara she da faɗa mata saƙon na yayan namu.
Me ko zata yi in ba dariya ba, nan ta shiga zaulaya ta, ta miƙe tana cewa bari inje inji kiran da yayan namu yake yi mani, in kaji kiran shi ai samu ne wallahi, kiyi maza ki shirya lokacin fitar tamu ya ƙarato.
Sallama tayi cikin shaƙaƙƙiyar murya, ga dukkan alamu ba ƙaramin ƙoƙari tayi ba wajen siranta muryar tata, bai ko ɗago ya kalle ta ba, shi duk a zaton shi hafsat ce, gashi kuma yaga ana nufo inda yake zaune ba tare da ɗar ko wani shayi ba, tin daga ƙafafun nata yake bi da kallo, sun kuwa sha mai sunyi da bare da bare abun su🤣🤣 sai sheƙi suke yi cikin man da ta shafa.
Aiko cikin hanzari ya ɗago yana bin sauran jikin nata da kallo, har zuwa kan fuskar ta, runtse idanu yayi gami da juyar da kanshi, ko babu komai dai yayi mugun gani, domin kuwa kusan rabin nonuwan ta a waje suke, show me your breast kenan🤔
"Keeee" ya miƙe a fusace yana mai daka mata tsawa, sannan ya ɗora da faɗin "me ya kawo ki nan? Wani abu kike buƙata? Ko wani ne ya kira ki? Ya faɗa cikin fushi da matuƙar ɓacin rai.
Rau-rau da idanu tayi alamar tausayi, wanda hakan da tayi ne ya ƙara ƙular dashi ma, sannan ta shiga faɗin" Suhan ce ta ce inzo wai kana nema na" ta faɗa cikin yanko ƙarya tana mai lailaya mashi.
"Get out from here" ya faɗa yana nuna mata ƙofar fita, ba ke nace ta kira mani ba, Hafsat nace, ke me zan maki in nace ta kira mani ke? Ko ni kike ma aiki ne?" ya faɗa yana mai jefo mata tambaya kaman zai make ta.
Girgiza mashi kai ta shiga yi, har ga Allah jikin ta yayi sanyi, domin ko kafin tazo nan saida ta shisshirya, hatta wankan da tayi da ruwan magani tayi shi, tayi matse matse da dama, domin tana tinanin Al'ameen ɗin kanwan lasa ne, da har zata jawo hankali shi ta ruwan sanyi haka.
"A'a yaya, kayi haƙuri" ta faɗa kaman wata baiwar Allah, sannan ta juya tana wata irin karairaya har zuwa ficewa ta a ɗakin. Da kallo ya raka ta yana mai jan wani irin tsoki, baya son wulaƙanta mutum masalan ma wanda yake ƙarƙashin shi, Amman wannan dole ce ta sanya, in banda tana sakarya ma ya za'ayi ta yi irin wannan shigar sannan tazo gaban shi tana karairaya kaman zata faɗo mashi?
Sallamar Hafsat ɗin ce ta katse mashi dogon tinanin da ya shiga, zama yayi yana mai amsawa a hankali, rufe laptop ɗin yayi yana mai kurɓar ruwan tatattun ƴaƴan itatuwa masu sanyi da suke gaban shi yayi.
Ɗan nesa da shi kaɗan ta samu ta zauna tana mai cewa "yaya gani Suhan tace kana nema na"
Da idanu ya bita yana mai ƙirƙiro murmushi dole cikin son kauda ɓacin rai da yake ciki, kenan waccen Yarinyar da ta fita yanzu ƙarya take ma Suhan da tace ita ce tace tazo yana neman ta?
Sake kauda tinanin yayi cikin ranshi, yana mai gyara zama ya fuskanci hafsat ɗin sosai, tambayar ta ya shiga yi shirye shirye da sauran abubuwan da take buƙata wanda bata idasa ba, yana gargaɗar ta da kiran nasu gidan domin neman wani abu, duk Abunda take so yana iya yi mata, ta tunkare shi kai tsaye kawai.
Da yake akwai fahimta sosai tsakanin su da ƴar shaƙuwa, yana son hafsat ɗin, ko don sanyin halin ta da kuma girmama na gaba da ita, ba kaman sangartattun ƙannen nashi ba, ta shiga zayyane mashi dukkan abubuwan da take buƙata, take yayi mata trnsfer na kuɗaɗen duk da zasu isheta ta kammala hidima ta har ma tayi saura, sannan ya shiga sanar da ita hukuncin Alhaji na cewa ba zata koma gida ba, har sai an ɗaura auren nata, suma duka sauran mutanen nan ba da daɗewa ba zasu tarkato su taho Abuja acen za'ayi duk wasu shirye shirye da hidima bikin, hatta da su kaka zuwaira duk nan za'a taho dasu domin suma su ɗan shaƙata, zaman wuri ɗayan ya isa hakanan.
Ƴar fira sukayi kaɗan kaɗan, abun ka da wanda bai damu da magana ba, hakan ce ta sanya ta yi mashi godiya gami da miƙewa ta fice harda tukuicin ja mashi ƙofar, wani ɓari na zuciyar ta na tambayar ta me maree taje yi sashen yayan nasu?
*************
Maree da take zaune ɗakin mama talatun da ta kasance ita ce mahaifiya ta, Amman ba kowa ya sani ba, ƙwalla take share wa, cikin ƙunan rai ta shiga zayyane mata Abunda ya Ameen ɗin yayi mata, aiko ashar ta lailayo ta zunduma tana faɗar baƙaken maganganu, "kika ce har Suhan kin gani a sashen nashi?" ta jefa mata tambaya, tana daga tsaye riƙe da ƙugu.
"Eah mama, na ganta lokacin da ta fito, har ma harara ta ta dinga yi.... " ta faɗa cikin ƙunar zuciya, uwar tata ce ta katse mata maganar da take yi "ke dallah ja cen ki ba mutane wuri, ki tabbata duk yanda zakiyi kiyi, ki jawo hankalin yaron nan a gareku, ki tsaya kallon ruwa kwaɗo yayi maki ƙafafu, ki dai san a nan gidan babu wanda ya san nice na haife ki, ko shiga hidimarki kika ga bana yi, bana so kwabar mu tayi ruwa, Amma billahillazee duk yanda zamuyi sai mun mallaki ƙaramin yaron nan attajiri, sai mun mulka da juya gidan nan fiyee ma da yanda Kubra keyi" ta faɗa tana huci da hurtai.
"Kyalesu, na san abun yi, ba dai ke ya wulaƙanta ba,? Zai dawo ne yana neman soyayya ki da roƙon ki, a yayin da zamu juya shi kaman waina a cikin tanada, goge hawayen ki, ki koma bakin aikin ki kada su dawo su tadda baki kammala Abunda suka sanya ki ba, ina so ne ki shiga jiki su, kaman yanda jini yake gudana a jikin nasu, kuma ki tabbatas duk magungunan da na baki kina zuba masu a abincin da suke ci, ki kula fa, kinsan kukun nan basu da mutumci, kinsan ƴan kudun nan, shegu ranakun banza" ta ƙara she tana gyara zaman za in ta da har ya warware tsabar bala'i gab yake da faɗuwa, har ɗan kaman ta kana iya hange.
Da too mareen ta bita, tana mai tashi ta fice daga ɗakin, ko da zata gifta ta inda ɗakin nasu Suhan yake saida ta wurga mashi harara kaman Suhan ɗin ce a ciki.
*******
Kammala shiryawa tawa, yayi daidai da shigowar Hafsat ɗin ɗakin namu tana mai cike da farin ciki, rungume ni tayi tana faɗin "kin gani ko Suhan, kingani dama nace maki kiran yayan Alkhairi ne a gare mu" kuɗin soyayya ya bamu wadda zamuyi har sai mun gaji da kashewa" cikin murmushi na zame jikina daga nata, domin tana niyyar kadan ne, na bita da kallo ina cewa "aiko kin gode wallahi hafsat, don Allah to karki kira gida a ƙara maki wasu tinda waɗannan sun isheki, ko shi Abdul ɗin (sunan saurayi hafsat ɗin wanda zata aura) kar ki amshi masu yawa a wurin shi." da to ta bini, tana mai ƙara gyara fuskar ta, sallama muka yi ma umma da take zaune tsakar gida tana sauraren radio sallama, addu'a tayi mana da sake faɗa mana kar mu kai magribawaje mu dawo da wuri.
Ranshi har yanzu a matuƙar ɓace yake, me Yarinyar ke nufi dashi ne? A cikin gidan nan ma zata dinga yin irin wannan shigar tana matsayi mai aikin gidan da yake wadace da ƴan aiki maza, kama daga masu gadi, drebobin da masu gyaran lambu da ba flowers ruwa da share gida?, miƙewa yayi gami da shigewa ciki domin canja kaya, so yake ya fita ko zai shaƙo iskar da zata sanyaya mashi rai.
Bai ko kula da yanda ta canja ma ɗakin tsari ba, har ya canja kayan ya fice, da yake wardrooo ɗin ta cikin bango ce, mai azabar kyau da ƙayatuwa.
Keys kawai ya zara, gami da kwasar wayoyin shi na hannu, ya fice daga sashen nashi, gami da murza mashi makulli ya rufe😅
Tin daga nesa ya hango su, ya sheda hafsat, Amman gudar ce bai gane ba, har saida ya matsa daf dasu, inda suke tsaye suna jiran driver yazo ya kaisu, saboda yau ba ita kaɗai bace, ita da hafsat ce ya sanya ta yadda zata shiga motar gidan, shima saida suka kai ruwa rana sannan.
Ƙala bai ce masu ba har ya isa ga motar tashi da take gefe tana ta ɗaukar idanu, horn ya danna masu, hafsat ɗin ce ta kula dasu yake kira, ƙara sawa tayi wurin shi, tambayar ta ya shiga yi tsayuwar me suke wurin, sheda mashi tayi driver suke jira ya ƙara so, yace ya kusa isowa gidan. (da yake muɗi sun fita da su Hajiya Kubra da amare)
"Ku shiga in ajiye ku, idan ya ƙaraso sai yaje ya ɗauko ku in kun gama" Abunda ya faɗa kenan yana mai bin agogon hannun nashi da kallo don sanin ko ƙarfe nawa.
Juyawa tayi gami da ya fito ni da hannu, a hankali na shiga taka wa gami da ƙara sawa inda take tsaye bakin motar
Hannu ta sanya gami da buɗe man gidan baya, "ki shiga, yaya ne yace zai kai mu, in mun gama mun kira driver ɗin ya maidamu"
Ba a son raina ba na shiga, "ya salam" na furta cikin raina, sanyi da ƙamshi motar sun tafi da imani na, ɗan lumshe idanu nayi, lokacin da Naji motar ta daidaita a saman kwalta.
Ta baya nake satar kallon shi, tuƙin ma a natse yake yin shi, yayi kyau cikin riga marar nauyi kamfanin Adidas da baƙin wandon jeans a jikin shi, kai shi duk yadda ya sanya kaya ma kyau suke yi mashi.
Duk yanda naso in hana idanu na kaiwa gare shi, basa jin magana, saidai in samu kaina dumu dumu ina mai ƙare mashi kallo tas, har baƙi siɗik ɗin kwantaccen gashin kanshi.
Wani irin sanyin ni'ima ne gami da gaurayayyen ƙamshi turaren shi ne yake busowa, hakan ce ta sanya ni lafewa daga baya, ina tsura ma kyakkyawar fuskar shi idanu ta cikin madubi, tunanin nika ne masu yawa suke kai komo a zuciya ta, inda na taɓa faɗa mashi a ƙirji, inda na taɓa cakumo