Showing 141001 words to 144000 words out of 247770 words
lokaci guda yana mai ɗan zare jikin shi daga Bilal ɗin, sai kuma ya sake rungume shi yana mai faɗin
"Kace mun kusa zama Dads, ƙilama kafin lokacin na angwance"
Da dukkanin farin ciki Bilal ɗin ya sanya hannu yana mai zagayo Aminin nashi zuwa gareshi sosai, yana mai jin daɗin shiryawar tasu, farin ciki fal a zukatan abokan biyu, kuma aminan da suka taso tun ƙuruciya babu mai jin kansu.......
~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
*Page ~41~*
*Hahaha Lol, kaji wai ƴan Team Ya Ameen har sun haɗa masu suna wai _Suhameen_ kaji fa ko daɗi babu, to mu ƴan Team Sir Saleem mu kuma munce _Suhaleem_ don Allah Fans wanne yafi daɗi nan ciki?*
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Da misalin ƙarfe uku na yamma saƙon shiga yajin aiki ya iske ɗaukacin ɗaliban makarantar, kuma ana umurtar ɗalibai da su tattara su tafi gida har sai an buƙaci ganin su.
Hakan baiyi mana daɗi ba, domin duk wani ɗalibai mai kwazo da son karatu baya fatan abunda ka tsaida mashi karatun nashi.
Hakan ce ta sanya mu fara tattara komatsan mu. Kiran Sir Salim ne ya shigo wayata yana sanar dani in maza in shirya zai ajiye ni sannan ya wuce.
Ko awa ban ɗauka ba, na shirya komai nawa, sallama mukayi dasu Raihana wanda har gaban mota suka rakani, sannan suka juya suma domin idasa shirin barin makarantar.
Cikin ƴar walwala na gaida shi, ya kuwa tsare ni da idanu, domin shi a ganin shi har ya zuwa yanzu walwala ta bata koma yanda take ba ada.
"Lafiya Lau Jaan, sai kuka ji an shiga strike ko?"
"uhmm, Sir, ai mu hakan baiyi mana daɗi ba, masalan mu da muke ƙoƙarin cenza aji"
"To ya za'ayi ai sai haƙuri, gwamnatin ce bata da cika alƙawari, muma ba da son ranmu hakan ke faruwa ba, saidai fatan Allah ya kyauta kawai, ƙasar ce gabaki ɗaya sai yanda Allah yayi kawai"
Ya faɗa cikin ɗan murmushi da kan ƙara ƙawata fuskar shi.
Sir Salim mutum ne da yake da kyawon hulɗa da jama'a, Sam bashi da tsanani irin na sauran maza, hakan ce ta sanya yake lallaɓa ni kaman kwai, ko yanzu da muke tafiya shine yake ta bani labari, wasu inyi dariya, wasu inyi murmushi.
Mune bamu isa ƙauyen namu ba, sai wajen ƙarfe takwas na dare, wai a hakan ma domin lafiyayayar mota ce muke ciki.
Umma ta tayi matuƙar mamakin ganina a daidai wannan lokacin, shaida mata nayi tare muke da Malam Salim, miƙewa tayi ta shige ɗaki, haɗi da sanya hijab ɗinta sannan tace ince ya shigo, dama Hajjo batanan ta tafi gidan su da akayi masu rashi, bata dawo ba har yanzu.
Har cikin gida ya shiga, zama yayi bisa tabarmar da umma ta shinfiɗa mashi gefe, cikin girmamawa yake gaida Umman tawa, hakan na ƙara sanya ni jin daɗi, ko ba komai na san Allah ya haɗa ni da wanda ko nan gaba ba zanyi wani kuka ba a rayuwa.
Bayan sun gama gaisa wa ne ya miƙe haɗi da fita waje, saboda har yanzu ummata bata wani sakin jiki da Sir, Salim ɗin, ina jin Kunyar sarakuta ce take nuna mashi.
But ya buɗe, haɗi da ciro kayan masarufi masu yawa, shiga dasu cikin gidan ya fara yi da kanshi, ina taya shi da abunda zan iya ɗauka.
Hatta da ruwa masu yawa ya kawo mana nasha, ummata kuwa sai godiya da shi albarka take zuba mashi, domin dai ya riga ya kawo ba zata ce bazata amsa ba.
Ko bayan da na raka shi, kuɗi masu yawa ya kawo ya bani, a cewar shi, zaiyi ke wata kuma idan an koma zai zo da kanshi ya ɗauke ni.
Ƙin amsa nayi, ina mai cewa "haba abun ai sai yayi yawa"
Saida ya nuna mani tsananin ɓacin ranshi sannan na amsa ina mai ƙara mashi godiya.
Akan idanuna yaja motar tashi yabar ƙofar gidan namu.
Nima da kallo na kuma bin gidan namu, rayuwa kenan, wai ace ni da nake zaune a wannan kangon har Sir Salim ya ganni kuma ya amince da aure na a haka ba tare da yayi dubi da tsananin talaucin mu ba, har mahaifiyar shi tana iya kwana a wannan ruɓaɓɓen gidan da katangar ban ɗaki ce kawai ta ƙasa, sauran duk danni ne, domin kuwa ko ɗakin da muke kwana na bukka ne.
Babu Abunda zance da Sir Salim saidai godiya, ya so ni haƙiƙa, ya nuna mani ƙauna, kuma sun mana halarci daga shi har mahaifiyar shi, ko da zai tafi saida yana yin fuskar shi ya cenza, lallai na yadda da ƙaunar da Sir Salim ɗin ke nuna mani. A zahirin gaskiya nima na yadda da auren nashi ɗari bisa ɗari, saidai fatan Allah ya bamu zaman lafiya.
Ko dana ba ummata kuɗin, faɗa ta hau yi kaman zata burgeni, wai "bana da tunani, abun ai yayi yawa, tinda ba siyenki zasuyi ba, ko kwanaki da Ammin shi tazo ai baki ga iyayen abun alkhairin da tayi mana ba, kar in sake inga kin kuma karɓar wani abu daga hannun shi in ba haka ba sai na saɓa maki wallahi"
Nidai da kallo nake binta, yanda ta fututtuke tana faɗa, kai kace roƙonshi nayi, to abun bai ma dameni ba, saboda na san halin kayata, dole in lallaɓa ta in samu mu rabu lafiya tinda abu ya kusa saura ƙiris ya rage.
Hajjoma da ta shigo ta tadda kaya tuli tsakar gida, saida ta girgiza, to koda ummata ta nuna mata kuɗin itama faɗa ta hau yi, a cewarta itama gaskiya abar amsar abun hannun su, har sai ran da Allah yasa aka mallaka masu ni.
Hajjo mutuniyar kirki ce, Sam bata da baƙin hali, lafiya ƙlau suke zaune da ummata kaman wasu ƴan uwa, to shima malam ɗin haka yake, ko ba komai zuwan namu ya ɗan sama masu waraka daga cikin halin da suke ciki, sune yanzu harda cin shinkafa ƴar gwamnati da shan ruwan roba? Ai sai Sam barka wallahi.
A haka muka kwana firar makaranta da ummata, tana daɗa jan hankalina akan in maida hankali akan Abunda ya kai ni, banda kula ƙawaye barkatai ko samarin makaranta. Ce mata nayi wace ni? Yanda duk makaranta ta ɗauka akan cewa ni Budurwar Sir Salim ce, kuma ni ce wadda zai aura, ai su kansu ma samarin shakka ta suke yi, domin Sir Salim ɗin a makarantar Malami ne daya san Abunda yakeyi, Sam bashi da kula ƴan mata duk kuwa da barkwancin shi, samarin ma baya sake masu sai ƴan kaɗan gudun raini irin na ɗilibai.
*****************************
Basu tsaya neman abunda zasu ci ba a cikin gidan, a tare da Bilal ɗin suka fita zuwa nashi gidan, saidai duk yadda ummi ta kai da son Al'ameen yaci abincin nata, saidai ya yabuɗa, shi kau Bilal sakin jiki yayi ya kwashi girkin matar tashi, sannan suka sake fita zuwa kamfanonin su domin su duba ayyuka, duk da an tashi aiki kuwa.
Hajiya Kubra bata bi ta kan Alhaji Mustapha da yake ƙasar ba, ta sanya kai tayi ficewar ta wajen harkokin ta, su 3hajiyas ne ma suka zo suka ɗauke ta har gida. Akan idon shi suka fita, hakan ce ta sanya shi shima shiryawa ya fita zuwa wajen Alhaji Auwalu domin su tattauna akan batun Al'ameen ɗin.
To koda ya same shi akan batun, bai hana ba, domin dukkanin Abunda ke faruwa Hajiya Zainab ta faɗa mashi, hatta da halin yarinyar da nagartar mahaifiyar yarinyar, basu da matsala akan tarbiyyar yarinyar, domin haka ne ya sanya suka yanke shawarar nema ma Al'ameen ɗin ita yarinyar, alabasshi asalin nata a hankali zasu nemo shi.
Kiran Al'ameen ɗin sukayi da misalin ƙarfe takwas na dare, lokacin suna tare da Bilal a hanyar su na komawa gidan Bilal ɗin domin ya sauke shi.
Karkata kan motar yayi zuwa gidan Alhaji Auwalun, a tare suka shiga da Bilal ɗin har cikin gidan.
Hajiya Zainab suka tadda zaune a falo tana kallo, gaida ta suka shiga yi cikin girmamawa, itama amsawa takeyi cikin sakin fuska tana tambayar Bilal iyali, tana tambayar Al'ameen ƙarfin jiki.
Bayan sun amsa mata ne, ya sanya ta cewa su shiga Falon Alhajin suna ciki.
Sallama sukayi, suka koma gefe cen ƙasa suka zauna, Al'ameen harda duƙar da kai ƙasa, suka shiga gaida iyayen nasu.
Alhaji Auwalu ne yayi gyaran murya
"Al'ameen mahaifin ka yazo ya same ni akan wani batu, alal haƙiƙa naji daɗin jin wannan zance daga gareka, kuma ko ba komai muna alfahari da kai ta wannan fannin, kaf zuri'ar mu babu yaro mai tunanin manya da hangen nesan ka, saboda haka mun yanke shawarar gobe idan Allah ya kai mu, zamuje da kai ka nuna mana inda ita mahaifiyar yarinyar take, sannan magana ta biyu, kaman yanda kace baka so mahaifiyar ka taji, to ba zamu taɓa bari taji ba, sannan muna so, duk Abunda Kaga mun aiwatar ka sanya mana ido, kaidai yarinya kake so a aura maka, kuma insha Allahu zamuyi dukkan iya ƙoƙarin mu, muga ka same ta kaman yanda ka buƙata. Allah yayi maku Albarka ya sanya kufi haka, ya baku ikon taimakon na ƙasa daku a ko'ina kuke a rayuwa"
Haƙiƙa ba Al'ameen ba, har Bilal yaji daɗin wannan maganar ta wan mahaifin shi, yana matuƙar Alfahari da iyayen nashi a ko'ina yake, su ɗin masu son su ne, masu girmama ra'ayi da muradin su ne, dama ko ba komai ya san Alhaji Auwalun da mahaifin nashi ba zai taɓa samun matsala dasu ba, ga dai wadda za'a sha dabi da ita cen duk ranar da taji, saidai koma minene ya shirya ma hakan, ya shirya ɗaukar dukkan wani ƙalubale da tarnaƙi da kan iya tasowa anan gaba.
Muryar Mahaifin nashi ya tsinkaya yana tambayar shi ko da akwai wani abu kuma?
Girgiza mashi kai ya shiga yi, yana mai godiya da sanya ma mahaifn nashi albarka, shima Bilal ta ɓangaren shi, daɗi yake ji, ko ba komai yanzu ne zai shawo kan abokin nashi tin bayan shigar shi soyayyar.
Umurtar su sukayi da su tashi su tafi zuwa goben zasu wuce.
A mota ne Al'ameen ɗin ke cema Bilal ya shirya lallai fa dashi za'ayi wannan tafiyar, gyaɗa mashi kai yayi yana mai cewa "Allah ya kaimu"
Har yanzu mamakin Al'ameen ɗin yakeyi, kai idan ada akace maka Al'ameen zai faɗa soyayya irin haka zaka ƙaryata, mutumen da ƴan matan da suka kawo mashi ƙoƙon barar su, ƴaƴan masu kuɗi, ga kyau ga ilimin boko, Amman shi duk basu yi mashi ba, Suhan ita yagani tayi daidai da muradn shi, to dama haka duniyar take, duk inda tausayi yake to fa akwai soyayya a tsakani, dama shi jin abokin nashi kawai yakeyi, Amman tabbas ya san wannan lokacin ya a zuwa.
Kuma ko ba komai dai Suhan ta cencenci a sota, ta cencenci zama uwar ƴaƴayen ka, yarinya ce mai tarbiyya da biyayya da girmama na gaba da ita, duk wani namiji wanda ya san abunda yakeyi zaiyi fatan ace Suhan ɗin ta zamo uwa ga ƴaƴayen shi.
Har ƙofar gida ya sauke shi, yana mai kaɗa kan motar shi zuwa nasu gidan.
Mama Talatu da maree an sha barbaɗe barbaɗe a cikin girki, an jera ma Al'ameen a dinin table ɗinshi, wanda hajiya kubra ce ta sanya su yin hakan a cewar ta idan ya dawo ba sai ya nema ba, saidai da ta san Abunda zasu barbaɗa ma yaron nata, to da ko kusa bata fara barin maree na shiga sashen Al'ameen ɗin ba idan baya nan.
Saidai kallo ɗaya yayi ma abincin yaji zuciyar shi na matuƙar tashi, duk kuwa da irin kyawon abincin da na momin da suke cikin miyar.Iro mai ba fulawowi ruwa ya kira a waya, yace yazo ya kwashe abincin suje suci idan suna so.
Da gudun shi ya taho ɗakin na Al'ameen domin ya san cimar da za'a shirya ma uban ɗakin nasu daban ce da wadda za'a basu, balle yanzu da mama talatun take ƙwange wajen bada kayan abincin masu girkin. Duk da harda ita za'a ci Amman ta kwammace suci ba daɗi tana tara sauran a ɗakin ta, in sun taru taba maree a sace taje cen wasu ƙauyakun ta siyar a banza.
Cemashi yayi idan sun cinye su bar warmers ɗin a wurin su, godiya ya shiga zubawa yana mai ɗauka ya fice.
Saboda mugun abu irin na mutanen yanzu, shi kaɗai yaje ya ɓoye yaci abincin shi yayi ƙat, harda halshe yake sanyawa yana lashe warmer ɗin, dama Al'ameen ya san irin ƙazantar Iro, hakan ce ta sanya shi cewa yabar su a wajen shi.
**********************
Washe gari zamu iya cewa Al'ameen ɗin ya riga kowa tashi, bayan ya gama sallolin shine ya koma ya ɗan kwanta, tuni bacci mai nauyi ya sure shi, zamu iya cewa bai samu baccin kirki ba, daya kulle idanun shi, Suhan ɗin kawai yake hangowa zaune da saurayi suna fira, har tana dariya, abun ya matuƙar tsaya mashi a rai, sai kuma maganganun umma da suke yi mashi amsa kuwwa a kunne, wai wannan da ya gansu tare shine saurayin ta, wanda har an nema mashi auren ta, kuma umman ta bashi.
Sai ya tashi zaune ya jawo fulo ya matse shi kaman zai yaga shi, sai kuma ya koma ya kwanta yana mai sakin ɗan guntun tsoki.
Mamakin kanshi yakeyi, wai ashe haka soyayya take. Ashe haka kowa keji? Tin farkon asalin asali me ya sanya shi janye maganar tashi saboda wani hargagi na Mom ɗin tashi? Ai gashinan wankin hula na neman kaishi dare. A haka dai ya kwana har aka kira sallar Asubahi.
Wajen ƙarfe takwas na safe ya fito cikin shirin shi na manyan kaya, fara ƙal ɗin shadda ce gizna sai tashin ƙamshi da walwali takeyi, anyi mata ɗinkin doguwar riga kusan har ƙasa, tasha aiki Golden a jikin ta, takalmin ƙafar shi ma golden ne haɗe da hular dake bisa kanshi.
Yayi masifar kyau, idan ka hango shi daga nesa zaka iya cewa ango ne, harabar gidan ya fito riƙe da waya da ɗan ma ƙullin sashen nashi da ya kulle, domin ya kula ana shigar mashi ɗaki idan baya nan, hakan ce ta sanya tin jiya ya aika aka amso mashi makullan ɗakin wajen mama talatun.
Bilal yake ta faman kira yana sakin ɗan guntun tsaki a fili saboda rashin ɗaukar wayar tashi da baiyi ba.
Gate yaga an buɗe sai ga motar Bilal ɗin ta danno kai a guje cikin gidan. Bayan yayi parking ne ya fito shima sanye da shadda ruwan Army Green sai ɗaukar idanu yakeyi
Da ɗan sauri ya ƙara so wajen da Al'ameen ɗin ke tsaye yana faɗin
"Ran ango ya daɗe"
Ya faɗa yana mashi alamar jinjina haka cikin wasa.
Ɗan tamke fuska Al'ameen yayi, yana mashi alamun to ya tona masu asiri, ɗan waiwayawa Bilal ɗin yayi bayan su, yaga babu mai kallon su, sai kuma ya saki dariya mai sauti yana faɗin "Shegen gora, wannan kyau haka kaman yau ne ɗaurin auren?"
Sai a lokacin ya saki ɗan murmushi yana faɗin
"bana cike da iskancin ka Friend, bakaji yanda gabana ke ta faman faɗuwa ba, gashi ina ta kiran ka baka ɗaga ba"
"Ai ina ganin kiran, to na riga na kusa ƙarasowa shine nace bari kawai in bari in iso, sai inji menene?"
Sashen Alhaji Mustapha suka ranka ya, sun tadda ya shirya cikin shadda skyblue mai babbar riga, shima yayi kyau ainun, dama Alhaji Mustapha ba dai kyau ba.
A tare suka fito, mudi suka sanya ya fiddo masu wata mota mai ƙirar jeep da tun jiya Al'ameen ɗin ya sanya shi wanke ta.
Bilal ne ya shiga mazaunin driver sai Al'ameen a gefen shi, yayin da Alhaji Mustapha ya shiga baya, suka nufi gidan Alhaji Auwalun.
Shima sun tadda ya shirya, ba ɓata lokaci suka ɗauki hanya, yayin da Alhaji Mustaphan da yayan nashi suke ta firar su daga cen baya, shi kuma gogan naka ya luluƙa duniyar tunani.
**************************
Nasha baccin ƙalula yau, ba tashi da wuri tinda ba'a makaranta nake ba balle ince lecture, kafin in tashi Hajjo da ummata sun gama komai, yau tea muka sha da bredi harda wainar kwai, bayan na gama karyawa ne na fita na share tsakar gida, haɗi da gyara ɗakin namu.
Ruwa Hajjo zata je ɗebowa, hakan ce ta sanya ni ce mata ta bari idan na kammala komai nayi wanka zanje in ɗebo mana, tinda na aikin gida ne, kuma naga da ɗan saura.
Sai kuma muka zauna muna ƴar fira haka da hajjon, ummata na sanya mana baki jefi jefi, sai kuma ta miƙe haɗi da yin wanka, a tare muka fita da ita wajejen azahar zata je gidan ƴan uwan hajjon yi masu gaisuwa da yake an yi masu rashi kwanaki, shine zata koma yi masu gaisuwa, hajjon ce ta zauna gida haɗi da ɗora girki.
Muna tafe muna ƴar firar mu, har zuwa inda zamu rabu da umman tawa.
Ko da na isa rafin, na ɗebo ruwa kwatsam ina cikin tafiya, sai na kula kaman ana bina, na ɗan waiwaya sai naga wasu samari su uku, ƙara sauri nayi, sai kuma Naji ana ta faman tsayar dani.
Ware ƙafa nayi zan taka da gudu naga sun sha gabana
"Haba ƴan mata, ya ana ta maki magana kina wani share mutane kaman baki ji ba?