Showing 129001 words to 132000 words out of 247770 words
YAKE MACUCI NE KAWAI LITTAFANMU IS FREE 1 NE KAWAI NA KUDI,KUMA DA YACE YANA BA KUNGIYARMU KUDIN REGISTER DIN DA KUKE BIYA DOMIN MU TURA MASHI SABBIN LITTAFAN MU,TO WALLAHI DUK KARYA YAKE MANA MU BAMU DA MASANIYA AKAN WANNAN B'ARNAR DA YAKE MANA SAI DAGA BAYA MUKA JI,SANNAN KUMA INA SON KUSAN NUMBER DIN SHI SABODA YANA NAN YANA SHIGA GROUPS NA MATA DA SUNAN MACE SABODA HAKA KU KIYAYE GA NUMBER DIN SHI NAN (08107707692)*
*Laweexar ina matuƙar jin daɗin comment ɗinki, nagode Allah ya bar ƙauna. Saƙon gaisuwa gareki keda Ammin Islam daga bakin Ya Ameen, yace a sanar daku cewa yana sane daku a rayuwa, kuma watan watarana zai kawo maku ziyara shida Suhan ɗinshi, Amman fa sai bayan komai ya kwaranye idan ya samu nasarar auren ta. Lol*
*Page ~38~*
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Tin da na farka da safe gabana ke yawaita faɗuwa, har sai na dafe gurin nayi a'uziyya sannan nake samun sauƙi
Har dai khadeeja ta kula da hakan ta shiga tambaya ta ko ina da wata damuwar ne, da zasu taimaka mani wajen magance ta?
Gyaɗa mata kai kawai na shiga yi, ina mai cigaba da shiryawa ta. Har na kammala na fita domin zuwa hall, sai kuma na dawo ɗaki na ɗaura niƙab, gami da zura zumbuleliyar hijab ɗita har ƙasa, duk da zafin da akeyi, na kwammace hakan tinda munyi da Sir Salim akan anjima zai zo yayi mani wata lecture bayan la'asar.
Ta jikin motar ta Ya Ameen nabi na ratsa na wuce har zuwa department ɗin namu. Hatta da idanuna ba'a ganin su, hakan ce ta sanya ba kowa ne zai iya gane ni ba farat ɗaya.
Fitowa yayi daga cikin motar gami da kulle ta, Admin block ɗin ya nufa direct, ya kuwa ci sa'a ya tadda HOD ɗin namu.
Bayan sun gaisa ne, ba zai iya shaida fuskar Ya Ameen ba, saboda face mask baƙa dake fuskar shi, Amman wannan karon ya cire tabarau ɗin.
Photo na ya nuna ma HOD ɗin Mai suna Malam Sani, cikin ɗan girgiza kai bayan ya gama kallon hoton nawa ya dubi Ya Ameen ɗin.
"Wannan itace yarinyar da wani yake yawan zuwa nema a makarantar nan, kuma mu kanmu bama da masani ya a kanta, tin bayan shudedden lokaci bata kuma dawowa makarantar nan ba"
Ya faɗi haka ne saboda doka ce, kuma Sir Salim ya roƙeshi akan ya ɓoye dukkan wani abu daka iya bayyana wanzuwar Suhan ɗin a makarantar saboda wani dalili, kuma shi kanshi malam Sanin da ya kasance aboki ne ga Sir Salim, ba zai taɓa lamuntar abunda ka iya jawo cikas a al'amarin abokin nashi da matar da yake da burin aure ba.
Cikin kallon tuhuma ya Ameen ya fara kallon shi, bai ce ƙala ba, har Malam Sani ya kai aya a zancen nashi.
Yana da wata irin baiwa ta daban da Allah ya bashi, wadda ba kowa ne yaba irin ta ba, muddin ka faɗa mashi ƙarya ko abunda ba haka bane a cikin zuciyar ka, to kuwa lokaci guda farat ɗaya zai gano ka, saidai idan yayi niyyar share wa ne kawai ya share.
Ba tare da yace komai ba, ya miƙe gami da zaro complement card ɗinshi ya ajiye bisa teburin HOD ɗin.
Shima bai kuma cewa ƙala ba, ya sanya hannu ya ɗauka gami da dubawa, a ɗan firgice da kuma alamar mamaki ƙarara kan fuskar shi yake duban Ya Ameen ɗin, kaman ma dai bai gasgata abunda ya gani ba rubuce a bisa katin.
Lura da hakan da Ya Ameen yayi Ya sanya shi, zare face mask ɗin a hankali daga fuskar shi, ai tini Malam Sani ya miƙe cike da tsantsar girmamawa, hannu na rawa ya miƙa ma ya Ameen ɗin suyi musabaha
Bai ƙi ba, shima ya miƙe gami da miƙa mashi hannun, fuskar shi ɗauke da ɗan murmushi irin wanda ke ƙara ƙawata fuskar tashi.
A tare suka kuma zama, saidai har yanzu tsantsar mamaki bai saki Malam Sani ba, tinani yake yi wai ita wannan yarinyar wacece da har ake nemanta haka? Shin ma menene dalilin Sir Salim ɗin na roƙon shi Malam Sanin akan ya ɓoye labarin Suhan ɗin koda wani zai zo nema?
"Nine Muh'd Al'ameen Almustapha Dambulan. Yarinyar da nake nema ƙanwa ta ce, tayi mana ɓatan dabo ne bamu san inda ta nufa ba, ita da mahaifiyar ta, wannan ne dalilin da ya sanya kace ana zuwa nemanta nan, kuma muna da yaƙinin tana makarantar nan, shi wanda ke zuwa nan ɗin Sunan shi Bilal Amini na ne, kuma ɗan uwana, inaso ka bani haɗin kai, wajen shaida mani inda Suhan take domin mu sadu da ita da gaugawa. Mun zaɓi zuwa nan ɗinne ta ruwan sanyi, domin munsan dukkan bayanan da muke nema kana dasu"
Ya faɗa cike da ƙwarin guiwa, ƴar fara'ar dake kan fuskar shi tuni ta kau, saboda baya ko fatan Abunda kan kawo tarnaƙi a haɗuwar shi da Suhan ɗin.
Malam Sani ne ya shiga jinjina kai, sannan ya ɗora da cewa
"Tabbas Yallaɓai tana makarantar nan tamu, to saidai su da kansu ne suka nemi da muyi hakan, zan ji daɗi ace koda ka gano ta, ka nuna bansan da zancen ba, hakan shine kawai alfarmar da zan iya roƙa a wurin ka"
Cike da gamsuwa Ya Ameen yashiga jinjina mashi kai ba tare da ya kuma cewa komai ba.
Miƙewa Malam Sanin yayi yana faɗin, Yallaɓai me za'a kawo maka kayi break fast dashi?
Girgiza mashi kai Ya Ameen ɗin yayi, domin shi dai burin shi ya sadu da Suhan ɗin a daidai wannan lokacin.
Komawa Malam sanin yayi ya zauna, gami da jawo wani folder ya buɗa, tiryan tiryan har yazo kan files ɗin na suhan.
Jawoshi yayi, gami da miƙa ma ya Ameen.
Cikin ƴar taƙamar da ta zama jinin jikin shi, da kuma sarauta dake yawo yanzu a jinin shi ya sanya hannu ya amsa. Malam Sani dai yana kallon shi, burge shi yake daɗa yi, abun alfaharin shi ne, ace yau kaman Ya Ameen ɗin Yariman Matasan Arewa ne zaune a office ɗin nashi, a kuma gaban shi.
Ajiyewa yayi, yana mai zaro wayar shi ya kwafi number ɗinta, sannan ya miƙa ma Malam Sani File ɗin, godiya ya shiga yi mashi kaman baya son sake magana, ya miƙe da niyyar ficewa bayan ya sake ba Malam Sanin Hannu.
Har waje bakin motar shi ya raka shi, yana gaba shi kuma yana binshi a baya, saboda girmamawa Malam Sanin ne ya buɗe mashi ƙofar motar da kanshi, wadda tin fitowar su daga Office ɗin Ya Ameen ɗin ya buɗe motar ta hanyar ɗan maƙullin dake hannun shi.
Shi kanshi motar ta bala'in tafiya da imanin shi, in ko haka ne, dole ya nemi abokin nashi Sir Salim Yayi mashi murnar ƴar babban gida irin haka da zai aura, duk da shima yana da abun hannun shi sosai, kuma ya fito daga babban gida, Amman sai yake ganin kaman wannan daya zo ya dama su ya shanye har romon nasu.
Brown emvelop ya miƙa ma Malam sanin, yana faɗin
"wannan tukuicin ka ne, saboda nuna mani ƙanwata da kayi, sai mun sake haɗuwa"
Hannu na rawa Malam Sanin ya sanya ya karɓa, bakin shi har kunne sai zuba godiya yake yi, dama gashi wata yayi tsakiya komai ya tsaya. Har saida yaga fitar motar Ya Ameen ɗin daga makarantar sannan ya juya ya koma office ɗin nashi da zummar kiran abokin nashi.
****************
Hankalin Bilal idan yayi dubu ya tashi, har saida ya dafe ɗan madaidaicin teburin da Abie ɗin yake kai, lokacin da yake labarta mashi tafiyar Ya Ameen ɗin Nigeria.
Shima Abie ɗin kwatsam saidai yaga Bilal ɗin a office ɗin nashi, aiko nan ya titsiye shi akan ya faɗa mashi inda Ya Ameen yake, sanin Bilal ɗin ko wanene a gurin Ya Ameen ɗin ya sanya Abie ɗin sanar dashi gaskiya kawai.
"Subhanallah, me yake faruwa ne Yaya?"
Abie ɗin ya faɗa cikin sauri yana mai kamo Bilal ɗin ya nufi wata sofa dake gefe ajiye ya zaunar dashi, komawa yayi ya ɗauko mashi ruwa cikin wata gora haɗi da mug fari tar, ruwan ya tsiyaya mashi ya miƙa mashi. Baiyi gardama ba ya amsa ya kwankwale, sake zuba mashi yayi, nan ma shanyewa yayi tas, ko da dai Abie ya kula kaman ruwan bai ishe shi ba, sai ya miƙa mashi gorar ruwan baki ɗaya, aiko amsa yayi ya kafa kai, saida ya shanye ta tas, sannan yayi jifa da robar gefe yana faɗin.
"Why why?"
Zanewa yayi ya kwanta, shi dai Abie yana tsaye yana kallon ikon Allah, Amman kanshi gabaki ɗaya ya kulle, tambayoyi yake son yi ma Yayan nashi, Amman ya kasa ta ina ma zai soma farawa?
Saboda haka ya juya ya koma wurin zaman nashi, gami da zama ya jawo laptop ɗin tashi ya cigaba da aikin shi.
Bilal ɗinne ya miƙe tsaye gami da faɗin "Ni zanje gida Abie, sai ka dawo" bai jira cewar Abie ɗin ba, ya juya haɗi da ficewa daga Office ɗin.
Da kallo ya raka shi, yana mai girgiza kai, dole da akwai wani abu dake faruwa ko dai yake shirin faruwa, waya ya jawo domin ya faɗa ma Dad ɗin nashi, tin kafin komai ya kwaɓe dashi a ciki.
Aiko cikin sa'a Dad ɗin ya ɗaga, tiryan tiryan Abie ɗin ya feɗe ma Dad ɗin biri har wutsiya, shima hankalin shi ya matuƙar tashi, kashewa yayi yana mai cewa bari ya nemi Bilal ɗin yaji koma menene.
To shima Bilal ɗin, koda Dad ɗin ya kira shi bai ɓoye mashi komai ba, ai abokin kuka ba'a ɓoye mashi mutuwa, in ma bai sanar da Dad ɗin ba wa zai sanar mawa?
Cikin tsantsar ɓacin rai da Alhaji Mustaphan kan daɗe bai yi ba, yake sanar da Bilal ɗin cewa kada ya sake ya faɗa ma kowa, kawai su haɗu a nigeria ɗin asan abun yi.
Kashewa yayi gami da kwanciya domin ya huta, kafin anjima ya tashi yayi wanka ya ɗauki hanyar komawa Nigeriyar.
Mama Talatu an saki jiki a gida ana zuba isa da mulki, idan Hajiya Kubran bata nan, ita ce kan gaba akan komai, ta samu yadda take so, wani lokaci ma har ita ake ba ɗan ihisanin da ake ba ma'aikata ta rarraba, sai kuma Abunda taga dama take kawowa ta basu. Ta ɗaya ɓangaren kuma Maree har yanzu tana kan bakanta na son auren ɗan masu gidan ko ta wacce hanya ce, jiran dawowar shi ƙasar kawai take yi, ta aiwatar da abunda ta ƙumso tin tini tana zaman jiran zuwan nashi.
Ita ko Hajiya Kubra ma bata ko kula da komai dake faruwa ba, su Hajiya Sa'a da Hajiya Laila sun ƙara zama mata aminnai, koda Hajiya Zainab suka koma Abujan da zama ba kasafai ma suke haɗuwa ba, shima sai dai ita Hajiya zainab ɗin taje gidan Hajiya Kubran, har dai ta gaji, ta kula cewa ita ce zata dinga zuwa gidan ƙanen mijin nata? Alhali babu abunda take nema daga matar gidan?
Sai ta haƙure ma kanta, indai wata sabgar ta haɗa su, sun gaisa, ko da yake ma ba komai ne da akeyi ba kankiyar wanda Hajiya Kubran ke zuwa, kuma a haka kowa ya sanya mata ido, to tana da kuɗi, tafi ƙarfin wulaƙanci ta kowanne fanni.
Hannun jari ta zuba sosai a kamfanin matatar mai ta Nigeriyar, arziƙin yanzu fa yaci uban nada. Ko ina kayi labarin irin shaharar Hajiya Kubran akeyi, ya zuwa yanzu ta kuma samun ƙawa da take mai irin halin ta komai da komai, kuma itama tana da masifar kuɗi, sai suka ɗinke suka zama su huɗu kenan idan kaji ana cewa 4Hajiyas to su ake nufi, ciki da bai na Abuja babu inda labarin su bai karaɗe ba, mata ne masu ji da kansu, wanda duniya take kaɗa masu gangi a tsakar ka, basu damu da su taka wanda suke so ba, su muzgunawa wanda suke so, ko wanene kai, kuma ko me kake taƙama dashi indai ka shiga shirin su 4Hajiyas to fa ka bani, ka kaɗe har buzun ka.
********************
Ƙarfe biyu muka tashi lecture ta farko, salla kawai mukayi muka koma ta biyu, sai 4 muka fito, ina fitowa ne text ɗin Sir Salim yana shigowa wayata, akan in shirya zuwa 5 yana zuwa, domin yanzu mun cenza akalar inda muke karatu, library muke zuwa domin mun fi sake wa a cen muyi Abunda zai amfane ni.
Ɗan murmushi na saki, ina mai cewa "Hooo Sir Salim, ba hutu kenan? Gaskiya fa kada ka fasa man ƙwaƙwalwar saboda karatu"
Da haka na isa ɗakin, wanka kawai nayi, na jawo biscuit da fresh Yoo nasha, ban cika cin abinci ba sosai, duk da kasancewa ta ba mai rama ba, jikina yunwa ko wahala baya sanyawa ya cenza daga yanda yake.
Wanka nayi gami da shiryawa, a karo na farko kenan a rayuwa ta da zan fara yima Sir Salim kwalliya, ya sha roƙo na akan hakan, ni kuma sai nake ganin ba kwalliya ko soyayya ce ta kawo ni ba.
Tsayawa nayi na tsara kwalliya mai tafiya da hankali, riga da skir na wata jar atamfa mai ratsin shuɗiya na sanya, riga da skirt ɗin sun ɗan kama ni, hakan ce ta sanya na fara tsarguwa da kaina, da tunanin ba zan iya fita a haka ba.
Su Raihana ne suka shiga koɗa ni, ganin ina shirin tuɓe kayan in cenza ne, ya sanya suka shiga yiman magiya akan in bar shi, ai hakan ma ba wata damuwa, ko ba komai ya kamata in ɗan dinga yima Sir Salim ɗin kwalliya, tinda shi dai namiji ne mai son gayu, gashi ɗan gayu, dukkan matan dake skul ɗin bai zaɓi kowa ba sai ni.
Da haka ne yasanya sukayi comvincing ɗina akan in bar su, na bar su ɗin amman nace hijab zan sanya, nan ma nunawa sukayi basu yarda ba, khadeeja ce ma mai jawo mani shuɗin gyale, harda ƙoƙarin yafa mani, Raihana na fesa mani turare.
Muna cikin wannan dramer ɗin shiryawar ne, sai ga kiran shi akan in fito yana jirana zamu wuce library.
A haka na fita, ina ta jajjan gyalena saboda rashin sabo. Gashi kaina a kwance yake, duk yanda nayi akan in rufe gashin, ɗan kwalin baya da girma, hakan ce ta sanya dole na haƙura, Amman sai na yafa gyalen bisa kaina, ni kaina na san nayi kyau, kaman wata amarya, ban ɗauke da jikka, saboda karatu zani ba biki ba, waya ta ce kawai a hannuna, sai litattafai na na text book da handout, a haka na fito har na isa ga motar.
Yana daga ciki ya sanya hannu ya buɗe mani. Shiga nayi ina mai sakar mashi ɗan ƙaramin murmushi, shima yayi kyau cikin dakakkiyar shadda mai ruwan makuba, kanshi sanye da hular ƙube, sai zuba ƙamshi yake da fara'a kaman yanda ya saba.
Jan motar yayi yana mai cewa
"Gimbiya ta barka da fitowa"
Sake sakin murmushi nayi, ina mai ɗan sunne kaina ƙasa.
Gaishe shi na shiga yi, da salon koyon magana ta ya shiga amsa mani, na daga cikin abunda ke ƙara burgeni da Sir Salim ɗin kasancewar shi mutum mai ban dariya, tin baka sakin jiki dashi, har sai ka koma kana sakin jiki dashi, har in ma baka ji ɗuriyar shi ba ka bincika, masalan in kana cikin hali na ɓacin rai.
Kai tsaye bakin library mukayi parking, littattafan ya amsa daga hannuna, muka jera har cikin library ɗin muka samu kujeru muka zauna.
Kowa dake library ɗin mu yake kallo da ban sha'awa, mun dace da juna sosai, gashi daka kalli fuskokin mu, kasan muna cikin zallar farin ciki.
Ba ɓata lokaci muka fara abunda ya kawo mu, har zuwa kusan ƙarfe shida. Littattafan muka rufe, yayin da Sir Salim ɗin ya kirawo Ammin shi video Call muka shiga gaisawa, ga dukkan alamu taji daɗin ganin yaron nata yana yaɗa manufar shi ga Suhan ɗin.
Ɗan barkwanci tayi mana tana mai kashe wayar haɗi da cewa bari tabar mu mu tattauna, ni sai ma duk ta sakar mani kunya.
Shi kaɗai ke surutun shi, nikau daga eh sai a'a sai murmushi da nake ta fama doka wa. Yaba ƙofar shigowa baya, yayin da ni kuma nake zaune ina fuskantar wanda suke shigowa, hasken fitilar library ɗin tar a kan fuska ta, masalan yanzu da marece ya soma kawo jiki.
A wayar tashi dai still ya buɗo hotunan yaran shi yana nuna mani, yaran masha Allah, farare tas dasu, kaman ƴaƴan larabawa, da gani dai wannan Hasken Ammi ne suka biyo yaran, tinda ko ita ma'un bata ko kai ni haske ba, gashi shima Sir Salim ɗin kai tsaye bazaka ce mashi fari ba, ko baƙi.
Yaran sun burgeni, har ƙanwar shi dake karatun likitanci a Sudan mai suna Asiya Saida ya nuna mani.
Amsar wayar nayi a hannu na ina kallo haɗi da faɗin
"Masha Allah, ta fika kyau, tayi maka wayau, ita ta biyo kyawon Ammi sak"
Na faɗa ina mai ɗan sakin dariya.
Shima dariyar yayi cikin wani irin salo, yana faɗin "Kedai faɗi gaskiya, ko kowa zai ce Lil ta fini kyau, ai ke ba zaki faɗi haka ba, ko kuwa?"
Ɗan jinjina kai nayi ina mai cewa "Umm gaskiya kam Yallaɓai salim"
"Wuuuuuuuuuuu"
Abunda naji kowa na faɗa kenan a library ɗin, ga dukkan alamu dai wani abu ne suka gani daya basu mamaki ko ya burge su, sai kuma naga duk suna Miƙewa mazan su da matan su.
Hakan ce ta sanya ni kai kallo na zuwa ga ƙofar da