Showing 99001 words to 102000 words out of 247770 words
yar barin gidan nasu Mama Maryam ɗin, domin shi fa jikin shi na bashi harda sa hannun Hajiya Kubran wajen tafiyar tasu. Domin yasan ko wacece matar tashi, in ta tsani abu, tau fa sai taga ta rabu dashi hankalin ta zai kwanta.
****************************
Wayar ta ce ta shiga burari alamar kira ya shigo, cikin barci ta sanya hannu da niyyar latse wa, saidai ganin mai kiran ne ya sanya ta tashi zaune sannan ta ɗaga.
Daga ɗaya ɓangaren aka yi ta magana, yayin da ita tayi shiru tana ta faman ɗaga kai, alamar gamsuwa da maganar da ake faɗa mata.
An kusa minti biyar ana maganar daga cen ɓangaren, lokaci guda Hajiya Kubran ta saki wata shu'umar dariya tana ɓaɓɓakewa da muguwar dariya cikin isa, har ta zuro ƙafafun ta daga bisa gadon gami da miƙewa ta nufi window ta zage labulayen da suke masu matuƙar kyau.
"Allah ya raka taki gona, kin biya ni Hajiya Sa'a, don haka ki saurari tukuicin ki zuwa anjima"
Abunda ta faɗa kenan ta datse kiran, hango Alhajin nata da tayi riƙe da hannun Bilal sun nuof sashen nata cikin sauri, wata shu'umar gajeriyar dariya ta saki tana mai sakin labulen ta koma gami da ɗaukar hular ta ta aza a kanta jikin ta sanye cikin lallausar farar doguwar riga ta barci, saidai bata kama jikin ta ba sosai.
Tana saukowa daga bisa benan suna isowa cikin falon, cikin salon Munafurci ta shiga tambayar Alhaji ko Lafiya?
"Kubra Inaso ne inji ina Su Maryama suka tafi ne? Don na san dai duk inda suka tafi da sanya hannunki ciki"
Alhajin ya faɗa yana jifan ta da wani irin kallon tuhuma idanun shi na a kanta ko ɗauke wa ba yayi.
Cikin ɗan firgici da son nuna bata san me ke faruwa ba ta shiga dafe ƙirji
"Alhaji ni kuma? To ina suka tafi? Wallahi bani da masaniya a cikin Al'amarin nan, ni fa tashina kenan yanzu"
"Yau ne aka tashi ba'a gansu ba, kuma banyi mamaki ba domin kinsha yin iƙirarin sai sun bar maki gidan ki, bayan kina manta wa cewa lokacin da zan gina gidan nan babu ko sisin ki a ciki"
"To fa Alhaji yau harda gori abun? To inaso ka sani ni bani da masaniya akan komai, tafiya kuwa sun daɗe basu tafi ba, ƙila gajiya sukayi ne Shiyasa suka cenza sheƙa, dama ai a haka muka gansu kwatsam sun zo mana, yanzun ma a haka kwatsam muka gansu sun tafi, menene na tada hankali a ciki? "
Da kallon mamaki ya shiga binta, shi kau Bilal da yake ta faman safa da marwa a cikin falon, bai san lokacin da ya matsa kusa da hajiyar ba yana faɗin
" Haba Mom? Kinsan kuwa irin alƙawalin da na ɗaukar ma Al'ameen? Nace zan kula dasu zan basu dukkanin Abunda suke buƙata, ba zan iya faɗa mashi cewa sun tafi ba yanzu, ki taimaka in kinsan inda suke ki kira su kice masu su dawo"
"Au dama ashe ƙarya yake yi mani bai rabu da yarinyar ba, ashe dama yaudara ta kukayi, me kuke shiryawa ne? Bilal ka fita a cikin idanun a fa in kulle tin wuri, dama kai ke zuga shi kana ɗaure mashi gindin Abunda yake yi, gashi kai kayi auren ka hankalin ka kwance da yarinyar da kake so ƴar gidan manya sai shine zaka so haɗa shi da wannan ƴar matsiyatan"
Cikin sauri Alhajin ya dakatar da ita, yayin da shi kuma Bilal ganin ba zai iya jure kalaman Hajiyar a kansu ba ya sanya shi juyawa da niyyar fita, dakatar dashi Alhajin yayi yana faɗin "ka jira mugama magana Bilal, zata kira su ne yanzu su dawo"
"Ni babu wanda zan kira, domin bansan a wace ma duniyar suke ciki ba, na ji daɗin faruwa hakan don haka suje cen su mallake ƴaƴan wasu Amman dai ba na Kubra bB, kuma inaso ku sani babu wanda zan kirawo ai kuna da waya a hannuwan ku duka"
Tana gama faɗar haka ta juya cikin isa zuwa ga upstairs ɗin domin komawa ɗakin nata, su kuwa da kallo suka bita galala, shi Alhajin ma mamaki yake yi yaushe Kubran tashi ta koma haka? Yasan halin ta duka, Amman bai san na ta tsaya tana fuskantar shi take faɗa mashi magana ba haka a gaban yaro.
Girgiza kai kawai Bilal keyi, yana binta da kallo, daf da zata shiga ɗakin nata ne wayar ta dake hannun ta riƙe ta hau ƙara, ganin Abie ne ya sanya ta ɗauka tana mai ƙara ta a kunnen ta.
***********************
Ba yanda Abie ɗin baiyi dashi ba na akan ya tsaya ya kai shi airport ɗin, tinda ya matsa lallai lallai yau sai yaje ƙasar tashi, ganin Abie ɗin zai ɓata mashi lokaci ne ya sanya shi cewa yabarshi kawai zai tau taxi, idan ya shirya kawai ya wuce office kai tsaye, shima ba wani daɗewa zai yi ba zai juyo.
Ba yanda ya iya, shi ɗin mai biyayya ga yayan nashi ne, saboda yawan jiɓintar Al'amarin shi da yake yi a kulli yaum, hakan ce ta sanya shi haƙura ya shiga shiryawar shi a tsanake bayan ya raka yayan nashi ya hau taxi ɗin.
Saidai ko minti ashirin baiyi ba da tafiya, wayar Bilal ɗin ta soma ruri, bai ɗaga ba har ta tsinke aka kuma kira domin lokacin yana sanya kaya ne, tankawa yayi a hankali da niyyar duba wanda ke kiran shi, Telephone ɗin landline ɗin ta ɗauki burari itama.
Fasa ɗaga wayar tashi yayi kuma ya juya ya nufi falon domin ɗaga kiran, saboda duk a zaton shi daga hotel ɗin da ake kawo masu abinci ne, niyyar shi ma yace su bar shi kawai domin ya riga ya shirya zai yi break fast ɗin a office.
Kafin ya isa ta katse kuma, ɗan tsoki yayi yana mai juyawa, daidai lokacin door bel ɗin gidan ta ɗauki ruri itama.
Cikin Al'ajabi ya juya ya nufi ƙofar yana faɗin what co-insidence is that?
Daidai lokacin da ya buɗe ƙofar, ɗan sanda ya gani tsaye sanye cikin kakin shi kalar na ƙasar american, gaisawa sukayi cikin turancn da ya riga ya zauna a halshen su, id card ɗinshi ya nuna mashi yana mai cewa ya biyo shi suje domin ɗan uwanshi ya samu accudent a hanyar shi ta zuwa airport ɗin, yanzu haka ma bai san wanene ke a kanshi ba.
Cikin tsanann firgita ya dafe kanshi, yana mai rugawa ɗaki ya ɗauko wayar tashi, ko kulle gidan ma bai tsaya yi ba, ya fito gami da bin bayan ɗan sandan yana ta salati.
Motar ƴan sandan suka shiga kai tsaye zuwa wajen, daidai isar su tayi daidai da isowar Ambulance ɗin, da gudu suka ɗauke shi gami da aza shi bisa ɗan gadon ɗaukar marasa lafiyar gami da tura shi zuwa cikin motar, Abie ɗin baiyi wata wata ba ya shige shima inda aka ajiye gadon yana riƙe da Hannuwan Al'ameen ɗin da yake kwance samɓal ko numfashi ba yayi, ya sake yin haske fayau idanun shi a kulle.
Jini ne yake ta zuba daga hancin shi da kunnuwan shi, hakan ce ta sake gigita Abie ɗin ya shiga rusa kuka rurus, bai ma san Abunda zai iya yi ba kuma, faɗi yakeyi
"Yaya ka tashi don Allah, kada ka tafi ka barni ni ɗaya Yaya, su wanene sukayi maka haka? Me kayi masu? Ina shi dreban yake yaya? Me ka aikata masu haka da suke neman Rayuwar ka?"
Baisan ma har sun isa ba asibitn, saida yaga an buɗe ana kiciniyar ɗaukar gadon, hakan ce ta sanya shi dirowa, shima ya shiga binsu da gudu yana riƙk hannuwan ɗan uwan nashi.
Tin a waje suka maƙala mashi robar shaƙar iska, ko ta kan Abie basu yi ba suma suna ta dalla gudu da keken har zuwa ɗaki da aka rubuta Emergency a jiki.
Daga bakin ƙofar ne suka dakatar da Abie ɗin suka shige suna mai rufo ƙofar, saidai da yake ƙofar ta glass ce yana hango yanda suke ƙoƙarin samo numfashin shi, jikin Abie ɗin kuwa ya ɓaki da jini sosai, saboda yada ya rinƙa rungumo Al'ameen ɗin a jikin shi lokacin da suna mota.
Zubewa yayi a wurin yana sakin gunjin kuka, da yake ƙasar ta turawa ce, babu ma mai kula dashi sai ɗaiɗaiku, ganin kukan ba zai fisshe shi bane ya sanya shi kiran Alhajin nasu, sai akaci sa'a shi kuma ya manto wayar tashi ɗaki da zai fito, sai kuma ya fito ya tadda Wancen tashin hankalin, hakan ce ta sanya Abie ɗin cenza akalar kiran zuwa ga Mom ɗin tasu.
********************
"Wat Abie, me kace? Yanzu ina Son ɗin yake? Kadai kace man ya mutu?" ta faɗa cikin matuƙar tashin hankali, a sukwane ta juyo zuwa ƙasan inda tabar su Alhaji Mustaphan da ɗinbin mamakin ta yanda ta rinƙa zuba masu ruwan rashin mutumci.
"Alhaji kaji Al'ameen yayi haɗari, yanzu ma yana asibiti Baisan inda kanshi yake ba" ta faɗa cikin tashin hankali, ruwan hawaye har sun fara ɗigowa a daman fuskar tata.
Zaburowa Bilal ɗin yayi yana faɗin
" WHAT? Me ke faruwa damu ne yau? Ina Friend ɗin yake yanzu?"
Girgiza mashi kai ta shiga yi bata ma san tana yi ba, hankalin ta a matuƙar tashe, miƙa ma Bilal ɗin wayar tayi, ya amsa yana mai tambayar Abie ɗin Abunda ke faruwa, shima ta cen ɓangaren cikin kuka ya zayyane ma Bilal ɗin Abunda ya faru, jin hakan da kuma kukan da Abie ɗin keyi yasan abun yayi worst cikin salati ya miƙa ma Alhaji wayar da yake tsaye baka ma gane Abunda ke kai kawo a ƙwaƙwalwar tashi.
Hannu ya sanya gami da amsar wayar, yayin da Bilal ɗin ya juya a sukwane ya bar sashen. A inda ya bar su nan ya tadda su, cewa yayi kowa ya koma bakin aikin shi har zuwa anjima idan komai ya lafa, jiki a matuƙar sanyaye suka juya zuwa bakin aikin nasu, bama kaman mama talatun da zata iya kintatar dalilin da yasa su Suhan ɗin barin gidan.
Kai tsaye ticket yaje ya yankar masu, ya kuwa ci sa'a ƙarfe 11 jirgi zai tashi, don haka uku ya yanka harda Alhajin da Hajiya Kubran sannan ya juyo zuwa gidan shi, domin faɗa ma ummin Abunda yake wakana.
"Hajiya kiyi mani shiru hakanan da kukan nan naki fisabilillahi, da wanne kike so inji ne? Da ciwon yaron ko da ɓatar wannan matar. Iye"
Alhaji mustaphan dake zaune dage da kai ya ɗago yana mai kallon matar tashi da take ta safa da marwa tana fama rusa kuka.
"Ya za'ayi kace inyi shiru? In yarona ya mutu fa? Ko don kai baka son shi ne yasa baka san zafin shi ba?"
"Eh bana son shi ɗin, ke ai son da kike mashi ne ya sanya gashi nan nagani kina son sa bauta mashi rayuwa, duk Abunda yake so ke bakya son shi, su waɗancen da kikayi sanadin barin su gidan su ba mutane baneba ko. Wallahi Kubra kiji tsoron Allah, gabaki ɗaya yanzu kina neman canza hali, kina neman ki nuna baki jin magana ta ko? Na san irin matakin da zan ɗauka akanki wallahi, kuma abun ba zai yi maki da daɗi ba"
Suna cikin haka ne Bilal ɗin ya kira wayar ta hajiyar yake shaida mata su shirya an samu jirgin sha ɗaya, zasu tafi su dubo jikin na Al'ameen, tana jin haka kuwa ta juya gami da hayewa sama tana faɗin
"Duk fa Abunda zaka yi Alhaji wallahi ko a jikina, yaro na kawai nake so a bar mani kayana, muddin ina raye bashi ba waccen kilakin mai mallaka ma maza jikin ta"
Da fatan shiriya ya biya yana mai miƙewa ya fice daga sashen nata, zuciyar shi a cunkushe shi ya ma kasa gane daga inda zai fara neman waɗannan bayin Allah.
************************
Bansan sunan garin da muka dosa ba, kawai dai naga har ƙarfe shida na yamma muna ta faman tafiya a mota, tin ina ƙorafin kuka na har na gaji na dena.
Gashi umman tawa ta ƙi koda kula ni ne ma, saidai ta siya mana abinci munci a wani gari da muka tsaya da bazan iya cewa ga sunan garin ba, duk da dai cewa babban gari ne.
Duhu yayi lokacin da naga mun doshi wani ɗan ƙauye marar girma haka, na kula ma kaman bukkoki ne a cikin shi.
Jikin wani ruɓaɓɓen guda naga munja mun tsaya, hamdala Naji umman tawa nayi, hakan ce ta sanya na gane mun iso kenan, fitowa mukayi mu duk kanmu, dreban na sakin wata uwar miƙa gami da hamma.
Sauke mana kayanmu ya shiga yi, da yake ba wani yawa ne dasu ba, duk ƙulluka ma sunfi yawa a kayan.
Ummata ce Naji tana cewa ya kamata dai ya tsaya ya kwana dare ya fara rufawa, ce mata yayi a'a ta sallameshi kawai ya wuce.
Kuɗi da bazan iya faɗar yawan su ba ta ƙirga gami da bashi yanƙilga yaga sun cika cif cif yanda sukayi da ita, juyawa yayi gami da shiga motar bayan yayi mata godiya yaja motar shi yayi gaba.
Nimau saboda tsabar gajiya takalmi na na cire gami da zama bisan su, yayin da umman tawa take tsaye riƙe da ƙugunta da na fahimci ga dukkan alamu ya ƙage mata ne.
Juyawa tayi gami da shiga cikin gidan a hankali ba tare daya ce mani komai ba, ganin hakan ne ya sanya ban ko yi yunƙurin binta ba, na dai san duk wuya ba zata barmu mu kwana anan ba.
Gashi waya ta ta ɗauke tin muna mota, da na kuka ma babu service a hanyar bare inyi yunƙurin kira wani.
Sallama ta shiga kwaɗawa, gada cen cikin ɗaki na bukka aka amsa mata, wata dattijuwa ce ta fito riƙe da Aci balbal tana ta fama karewa da hannu kada iskan sanyin da akeyi ya kashe wutar.
"Wacece?" ta faɗa daga bakin ƙofar ɗakin d ataja ta toge.
Ba tare da umman tawa tace mata komai ba, ta shiga matsawa kusa da inda take tsaye sannan ta buɗe baki a hankali ta shiga faɗin
"Nice Hajjo"
Jin matar ta kira suna ta, gashi kuma bata ɗauki murya ba ya sanya ta matso wa, ko ba komai dai tinda taji an ambaci sunan ta, to ta san ba mai cutar da ita bace.
Salati ta saka lokacin da tayi arba da fuskar umman tawa, ai tini ta yarda acibalbal ɗin gami da artawa a na kare zuwa cikin ɗakin tana ƙwala kiran
"Malam fito Kaga fatalwar Maryam"
Cikin hanzari ya miƙe yana faɗin "Ke Hajjo bana son shirme da shiririta, ina kika baro fitilar ne kin barmu a duhu?" ya faɗa yana laluben inda yaji hajjon na zunduma ihu gami da faɗa wa cikin shirgi.
"Wallahi malam itace, ita ce malam kuma je ka gani, wayyo Allah na Maryama me nayi maki haka ne?"
Malam ɗin baibi ta kanta ba ya nufi inda suke ajiye ashana cikin laluba ya ɗauka gami da dosar ƙofar fita yana faɗin
"Yau Naji sakar ci, wace Maryamar kuma banda wadda muka binne da hannuwan mu, shekaru da dama?"
A bakin ƙofar ɗakin ta inda yake jiyo warin kalanzir ɗin ya zuƙunna gami da lalubo ƴar fitilar sannan ya koma cikin ɗakin nasu ya sake kunna wa, yana miyar ta sakar masu fitila wajen sakar ci duk ƙasa ta ɓata lagwanin da ya murza ba jimawa.
Duk abun nan fa da akeyi, umman tana tsaye tana kallon shi, hawaye tuni ya jiƙe mata fuska, nima dai da nake tsaye ta jikin ƙofar gidan ina iya hango Abunda akeyi cikin gidan, kaina ne ya sake ƙullewa, hango umman tawa nayi ta sake matsawa jikin ɗakin nasu tana mai sake yin sallama lokaci guda tana faɗin
"Nice Malam, da gaske Hajjo keyi, nice Maryamar Muhammadu"
Jin kalaman dake fitowa daga waje ne, ya sanya shima jinin shi ya tsinke ya fara gudu, lokaci guda ƴan cikin shi suka fara yamutsawa, kaman zawo ma yake ji, saidai yayi ta maza yana cewa
"Kiyi ma Allah Maryama ki tafi abunki, i ma fansa kika zo ɗauka wallahi ba nan ya kamata kizo ba, bamu da hannu ko alhakin ki a kanmu ko ɗaya"
Ya faɗi hakan ne, sanin da yayi cewa da hannuwan shi suka birne Maryamar da ɗiyar ta, yanzu kuma ta yaya za'a kuma zuwa ace mashi Maryama ce?
Ganin ba zasu yarda da ita bane, ya sanya ta ɗaga labulen kai tsaye ta shige cikin ɗakin, a sukwane nima na biye bayan ta, domin ganin yanda zata kaya a cikin ɗakin
To me kalaman su ke nufi ne? Me suke nufi da kiran umman tawa fatawa?
Basu yi aune ba saidai suka ganta tsulum cikin ɗakin,
"Malam ka kalle ni da kyau, nice Maryama, bamu mutu ba ni da yarinya ta Hauwau gata cen waje ma"
Cikin salati ya buɗe idanun shi yana mai sake ƙullewa, addu'a yake yi ace mafarki yake yi, domin shi fa bazai taɓa lamunta da wannan al'amari ba.
Ita ɗin daice tsaye a gaban shi, gashi dama shi cen baiyi imani da akwai fatawa ba a zahiri, matsowa ya shiga yi kusa da ita, duk da jikin shi har yanzu karkarwa yake yi, hannuwan shi riƙe da fitila yana mai haske ma umman tawa fuska.
Lokaci guda ya saki wani ƙaton salati yana faɗin
" *ikon Allah sai kallo, shin Maryama kece da gaske?, ina ita Hauwa'un?*"
_A yiman uziri, wallahi wasu ayyuka ne suka taso man masu yawa, ina barar addu'ar ku_
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°