Showing 171001 words to 174000 words out of 247770 words

Chapter 58 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10443

na shigo"

Sai gata kuwa yaran na shiga da tsaraba.

Mace mai yawan fara'a, ga kamala, kyakkyawa da ita, fara tas.

A hankali take saukowa tana faɗin wannan saukon fa haka malam?

Ɗan zamkwa yayi daga bisa kujerar da yake zaune, lokacin da take zama ne ya shiga gaida ta cikin girmamawa.

Amsawa tayi itama, tana mai rage fara'r dake saman fuskar ta.

Ina Ma'un?

"Bata tashi ba na baro ta Ammi"

"Amman dai Tasan ka dawo ko?"

"Ammi tana jina fa tayi banza dani ta ƙyale ni, ni kuma ban mara magana ba na fito, ki sanya a kawo man break fast nan, yunwa nake ji, ko jiya lipton kawai nasha"

Cikin wani irin kallo take faɗin

"Salim ka dena zama da yunwa, nasha faɗa maka" ta faɗa tana maibƙwala ma mai aikin ta kira.

Sai fata kuwa, cikin girmamawa ta gaida Salim ɗin.

"Ki kawo mashi breakfast, kada ki cika suger a tea ɗin"

"To Hajiya" mai aikin ta furta tana mai juyawa.

Ba'a daɗe ba kuwa sai gata ɗauke da tray, cike da kayan abinci.

Tashi yayi tsaye ya amsa, yana mai ajiyewa ƙasa, ya sauko bisa carpet ɗin, yana mai cire hula ya ajiye, sannan ya zare links ɗin, yana mai kalmashe hannun riga.

Miƙewa yayi yana mai wa ko hannu cikin sink da yake ajiye gefen falon tare da gogewa da towel, sannan ya dawo ya zauna.

Sai da yaci ya ƙoshi, sannan Ammin ta sake kiran mai aikin tazo ta kwashe, sannan ya sake miƙewa ya wanki hannu ya dawo ya zauna.

Tattara dukkan natsuwar shi yayi kan Ammin tashi, yana mai faɗin "Ammi gani, kince inzo kina son ganina"

Itama ganin ya bata dukkanin hankalin shi, ya sanya ta gyara zama, tana mai fuskantar shi, cike da tausaya ma yaron nata, akan abunda zata faɗa


"Salim, yarinyar nan kayi ta addu'a, idan rabon ka ce sai kafa Allah ya baka ita"

Gaban shi ne ya yanke ya faɗi, cikin tsananin firgita yake kallon Ammin tashi, idanun nashi har sun cenza kala.

"Ammmii bann.. Fahimta.. Ba, wani abu ne ya faru kuma?"

Ya tsinci kanshi cikin in'ina yana mai jefa ma Ammin tashi tambaya.

Tsam ta miƙe daga inda take, tana mai dawowa bisa kujerar da yake zaune, sai kuma ta kamo dukkanin hannuwan shi.

"Wato jiya Su mahaifin ka, da su Alhaji Basheer (Wan mahaifin shi) su je cen Abuja gidan Iyayen yarinyar nan, to Amman dai su abunda sukace, yarinya dai sunyi mata miji, Amman dai idan basu daidaita kansu ba, to zasu neme mu"

Cikin tsananin firgita ya miƙe yana mai sauke hular dake kanshi, salati ɗauke a bakin shi yake furta

"Ammi anya kuwa cen suka je? Suhan fa na ƙauna ta, kuma mahaifiyar ta da bakin ta tace maki ta bani, yanzu kuma ya zasu ce haka? Ko dai ba cen suka je ba Ammi?"

Kamo hannuwan shi tayi duka, tana mai cewa "Zauna Salim, zauna, ya zaka ce ba cen suka je ba Alhaji Mustapha Dambulan ɓoyayyu ne a ƙasar? Kana sane da mahaifin ka ma ya sanshi tin da daɗewa ko? To dai haka suka ce, sannan Baffan ka ma ya riga ya yanke hukunci, yake ka haƙura, su ba ƙananan mutane bane da zasuyi magana biyu ba, kuma ma banda abun ka, ai ba mace ke bada aure ba ko?"

" Ammi ki roƙe su su koma, ina cikin wani hali please Umma, Suhan ita kaɗai ce zata iya gyara mani gida na, da tsaftar ta, da kawaicin ta, da biyayyr ta, da haƙurin ta, Ammi ki taimaka mani don Allah"

Ya faɗa cike da kaɗuwa, yana kuma ƙoƙarin sake miƙewa.

Amman Ammin tashi ta damƙe hannun nashi kam, ta yanda ba zai iya kuma miƙewa ba.

"Nima Salim naso ka da yarinyar nan, na maka sha'awar ta, tarbiyyar ta, da hankali da natsuwar ta ta burge ni, saidai har yanzu ban fidda ran bazaka same ta ba, ban kuma fidda maka ran ko ka rasa ta, ba zaka samu wadda ta fiye maka ita ba, ina maka addu'a Salim, kuma zan cigaba da yi maka Addu'a, Allah ya shirya maka matar ka, sannan ya baka wadda zata kawo kwanciyar hankali a cikin gidan naka. Wanna shi e fatana a gareka a kida yaushe."

Ta ƙarashe maganar tata itama cikin ƙunar zuciya.

Har ga Allah bata ji haushin Umman a Suhan ba, saboda ita uwa ce, har kida yaushe zataso ta Aurar da ɗiyar ta ga wanda take so, to saidai itama kanta ƙarƙashin wani take, dole ne tayi biyayya, komin yanda take son abun, addu'a ita kawai zasuci gaba da bin yaran nasu da ita.

Rabon ko da taga Salim ɗin yayi hawaye an daɗe, duk yanda yake shan wahala da azabe zama da Ma'un baya damun kanshi har haka, Salim mai barkwanci, Salim mai yawan fara'a, Salim bai fidda wasu daga damuwa da zaulayar shi, tau sai ga Salim na hawaye gaban Ammin shi.

Guiwoyin shi duka ya sauke ƙasa, har yanzu hannayen shi na cikin na Ammin nashi, Tunowa yakeyi da wayar su ta ƙarshe da ita, Tunowa yakeyi da kallon shi da ita na ƙarshe, Tunowa da Kunyar ta, da yawan son karatun ta, yanzu shikenan ta tashi ba'a mallakin shi ba? Anya kuwa zai iya haƙura kaman yanda iyayen nashi suka buƙata?

A sanyaye ya miƙe tsaye, yana mai faɗin "Ammi zanje gida in kwanta, kaina yana yi mani ciwo"

"Ba inda zaka Salim, shiga ɗaki na ka kwanta, zuwa anjima sai ka tafi."

Ba musu ya fara taka matattakalar upstairs ɗin, yana mai jin kanshi yana wani mugun sara mashi.

Wanene wannan? Wanene wannan mai sa'ar da har zai iya mallakar yarinyar daya ƙwalkafa rai a kanta? Yarinyar da ya tsara yanda zaman gidan nashi zai kasance da ita? Shin tana ma son shi kuwa? Zata yarda da auren itama kuwa? Saidai yasanta, yarinya ce mai kawaici da biyayya, ba zata taɓa bijire wa umurnin iyayen nata ba.

Koda ya isa ɗakin, ciki ya tadda yaran nashi, suna ta faman wasan su, hankalin su kwance, ga kayan ciye ciye daya kawo masu, sun baje bisa gadon kakar tasu Ammi, sai cin abun su suke suna wasa.

Haka suka sake hawa kanshi, kowa da abunda yake faɗa, kowa ƙoƙarin bashi biscuit yakeyi yaci, hakan na burge shi da yaran, Amman sai gashi yau yana ture su, yana faɗin suje ƙasa suyi wasa kanshi ke ciwo.....




Hhhhmmmmmmmm







~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._


*Page ~49~*


°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°


Tin dai da naga text ɗinshi da daddare, sai na kawo ma raina ba zai kirani ba sai zuwa safe.

Hakan ce ta sanya, banyi gigin kiran shi ba, har kusan ƙarfe goman safiya.

Ya kamata ace ya kirani, ko don inji yanda akayi da maneman auren suka je.

Ban dai kira ba, amman zuciya ta na ta saƙa man in kira shi inji halin da ake ciki.

Har yanzu gabana bai bar duka ba, sai kuma hankalina ya fara tashi, gashi munyi waya da Umma da safe itama bata ce man ga yanda ake ciki ba.

Hakan ce ta sanya ni kiran Hafsat, saidai muka gama gaisawar da ita Amman itama bata ce man komai ba.

Ban iya tambayar ta ba dai, kunya nake ji sosai, tun da dama nasan ita bata ra'ayin abun a cikin ranta, ɗan uwanta kawai take so.

Haka nayi shahadar kiran Sir Salim ɗin.

Kira na sau biyu amman ba'a ɗaga ba.

Kasaƙe nayi da waya riƙe a hannu, ga su khadee suna ta tambaya ta wai ko an sanya bikin ne?

Rasa abunda zance masu nayi, saidai na miƙe tsaye ina mai ficewa daga ɗakin, wayata riƙe a hannu.

Sake jaraba kiran nashi nayi, wannan karon ma ta shiga, saidai tana fara ringing aka katse.

A'ah me ke faruwa ne?

Sake kira nayi, amman sai ba'a katse ba, aka barta ta cigaba da ringing, har said ata gaji ta katse don kanta.

Gashi dai ina jin kunya, bana iya kiran Ammi, hakan ce ta sanya dole na koma ɗaki na kwanta, nan na tarar su Raihana sun tafi lecture.

************

Baya jin zai iya ɗaga kiran nata a daidai wannan lokacin, hakan zai iya ƙara karya mashi guiwa.

Muryar ta kaɗai yake da muradin ji, Amman idan ya tuna da hakan ba zai wani amfane shi ba, mallakn wani ce, sai ya runtse idon shi ya sake buɗewa, har yanzu dai wannan abun da ya tattaru ya dunƙule mashi a maƙoshi ya kasa wucewa.

Har Ammi ta gama tattara yaran nashi ta shirya masu zuwa makaranta, driver ya ɗauke su, yana nan kwance bisa gadon nata, shi ba bacci ba, shi ba ido biyu ba.

Babu sauran kuzari ko walwala tattare dashi, yana tuno farko haɗuwar shi da ita.

Sanyin ta, tarbiyyar ta, duk waɗannan abubuwan idan ya tuna wai ya rasa su, sai yaji kanshi ya ƙara yi mashi nauyi.

A haka Ammi ta shigo ɗakin ta same shi.

Bakin gado ta kai zaune cikin sanyin jiki itama, ƙura ma yaron nata ido tayi, har yanzu tana iya hango irin Abunda take gani a cikin idanun shi, aduk lokacin da ya nemi wani abu ya rasa, tin yana yaro, saidai da yake shi ɗin mai haƙuri ne, tasan zata iya shawo kanshi da izinin Allah.

"Salim" ta faɗa a hankali.

Ganin hakan da yayi ne ya sanya shi tashi zaune, yana ƙure Ammin tashi da kallo irin na ban tausayi.

A take tausayin yaron nata ya kuma tsira mata.

Duka hannuwan shi ta kamo.

"Salim Abban" sunan da take yawan kiran shi kenan duk lokacin da rashin irin wannan ya same shi.

Da gefen baki ya ɗan murmusa mata, irin yadda shima ya kan yi mata.

Hakan ne ya ƙara mata ƙwarin guiwar ci gaba da abunda take da niyyar faɗa.

"Nasan ba daɗi Salim, to saidai bamu da yanda zamuyi, dole ne kuyi biyayya ga iyayen ku, masalan ma ita da take mace, ba ita zata aurad da kanta ba, wannan yasa nake matuƙar so ka taimaka mata wajen yin biyayyr ga iyayen nata. Ba zan ji daɗi ace ka koma mata ba a yanzu, inaso ka sanar da ita dukkan abunda ke faruwa, sannan ka yanke duk wata alaƙa ta soyayya dake tsakanin ka da ita, ina maka addu'ar Allah ya baka wadda ta fita"

Da idanun shi da suka cenza kala yake daɗa bin Ammin tashi da kallo.

"Ammi ina son Suhan matuƙa, nayi rashi Ammi, ya zanyi? Naso ta shigo gidana, ko da hakan zai zama silar samuwar haske a cikin gidan nawa, nima in zama mai gida kaman yanda sauran maza keyi, Ammi ita kaɗai ce zata iya..."

Girgiza mashi kai ta shiga yi.

"Salim kada ka sare, da izinin Allah zaka samu wadda ko bata fita ba, itama ba abunda zaka nema a wajen ta ka rasa, insha Allah"

Sauke ƙwayar idanun shi yayi ƙasa, ji yake kaman ya saki kuka, ko ya samu maƙoƙon da ya tokare mashi ya wuce.

A hankali yake haɗiye wasu irin miyau masu zafin gaske.

"shikenan Ammi, ki cigaba da taya ni addu'a, nagode ƙwarai, ina alfahari da samun uwa ta gari, nagartatta kaman ki, ki faɗama su Abba cewa *Na janye kaman yanda suka buƙata* Allah ya zaɓa mana Abunda yafi zama alkhairi, ya sanya hakan shine alkhairi gare mu baki ɗaya"

Cikin tausayawa take bin shi da kallo, ita kanta tasan tayi rashin suruka ta gari.

"Ba komai Son, Insha Allahu zan cigaba da yi maka addu'a, ita kuma Ma'u Allah ya shirya mana ita, ya sanya ta gane gaskiya, kuma ya bata ikon yin aiki da ita, ko yanzu ka kawo wadda kake so, a shirye nake da na mara maka baya ka same ta Salim, sannan inaso idan kaje makarantar ka haɗa ni da Suhan ɗin zamuyi magana"

Jinjina mata kai ya shiga yi, ko ba komai ya ɗan samu relief, wani sashe na zuciyar shi yayi sanyi, Ammin tashi mace ce wadda ba kowa Allah yaba irin ta ba, a matsayin Uwa, samun ta kaɗai a rayuwa ya gamsar dashi. Shiyasa a kullum yake daɗa alfahari da ita a rayuwar shi.

Zuro ƙafafu shi yayi daga bisa gadon a hankali yana mai miƙewa, sannan ya maida kallon shi kan Ammin tashi, da ta riga da ta saki hannun nashi.

"Ammi Abban fa? Bamu gaisa ba, gashi ina so in wuce, ban ɗauki excuse ba"

"Ayya, Gashi kuma tin safe ya wuce majalisa (Senate) saidai ko ka kira shi, yace ne suna da muhimmin Meeting ta yanda za'a shawo kan matsalar wannan ƙarin harajin da gwamnati tayi, sannan da rufe boder"

Ɗaga mata kai yayi alamun gamsuwa, sannan ya fara takawa zuwa sauka down stair.

A baya ta biyo shi har suka sauko tana mai ƙara yi mashi nasiha akan yadda da ƙaddara.

A bakin ƙofa ya tsaya, yana mai kamo Ammin ya manna mata peck a goshi, sannan ya fice tana mashi fatan Allah ya kiyaye hanya.

Ba Abunda zai koma gidan yayi, hakan ce ta sanya shi ɗaukar hanyar zariyar kai tsaye ba tare da ya kuma bi ta kan Ma'un ba.


********

Sanye yake cikin dakakkiyar shadda, ruwan bula, sai hula daya aza bisa kan nashi itama bula ce.

A hankali yake takawa zuwa sashen amaryar tashi.

Ƴan aiki sai kallon shi suke yi, suna kuma gaida shi, haɗi da jinjina irin jajircewar Alhajin ta fannin tsaya ma gidan nashi, gashi dai kowa yayi tunanin wata fitinr zata ɓullo ta fannin Hajiya Kubra, Amman ga mamakin su, duk sai suka ji shiru kuma, kaman ma babu abunda ya faru a cikin gidan.

Ba kowa a falon, sai kayan kallo da suke ta aikin yi, da kallo yabi sashen, ko ina tsaf-tsaf, ga ƙamshin girki da yake tashi, wanda ya haɗe da na room freshner da ta fesa a ɗakin ta Naseem.

Duka ɗakunan ya leƙa bata ciki, hakan ce ta sanya shi nufar kitchen.

Ta gama soya dankalin ta lafiyayye, ta haɗa coleslow da ƴar stew ta anta da kwai, sai tea data haɗa wanda ya sha lemon grass da kayan ƙamshi.

Ta juye kenan zata fito sukayi kiciɓis.

Da murmushi a saman fuskar ta, sai kuma ƴar Kunyar shi da har yanzu bata gama sakin ta ba.

A hankali taja baya tana mai gaida shi.

Cikin murmushi ya sanya hannu ya amshi plate ɗin, ita kuma sai ta koma ta ɗauko Mug ɗin tea ɗin da wani fork.

Gaba ya shiga tana bin shi a baya, har bisa dining table ɗin.

Kujara yaja ya zauna, itama tana mai zama, ƙara gaida shi ta yi, ya amsa cikin sakin fuska da walwala irin ta dattawn arziƙi.

"Alhaji bismilla mana, ka karya don nasan dai da wuya idan kaci wani abu, don naga ka fito da wuri yau"

Ta faɗa a kunyace irin tasu ta manya.

Da kallo yake binta, tayi kyau, duk ta cenza abun ta, kaman wadda ta shekaru a cikin hutu.

Atamfa ce jikin ta, an mata ɗinkin zamani mai kyau, sai yake ganin kaman ma bata taɓa haihuwa ba, balle ace ta ajiye kaman Suhan.

"Kin bani ne? To wa zai bani idan ba ke ba?"

Ya faɗa cikin zaulaya.

Itama dariya tayi a hankali, tana mai tura mashi Mug ɗin tea ɗin gaban shi.

"Afuwa Alhaji, to gashi, ai bansan yanda tsarin yake ba, naga duk tare kuke cin abinci ne cikin gidan, Shiyasa nayi tunanin ko ka karya"

Bai ce ƙala ba, in banda murmushi da yake yi, yaja cup ɗin gaban shi, yana mai ɗaukar cokalin ya fara cin abincin.

Ba sabon abu bane a wurin shi, cin abincin nata, to saidai yau yake jin kaman abincin nata ya ƙara daɗi, gashi dai ba wani tarkace a ciki, Amman ɗanɗanon yayi mashi daɗi a baki.

"Magana nazo muyi dake Umman Suhan, to Amman dai kafin nan kije ki haɗo naki tea ɗin, tinda na ƙwace maki wannan"

Itama murmushi ta sake saki, tana mai tura kujerar baya, sannan ta miƙe ta nufi kitchen ɗin.

Da kallon jin daɗi ya bita, yana ayyanawa a ran shi, yanzu ne aure ya tabbata a gareshi, ko bayan hakan ya samu natsuwa da kulawr da yake da muradin samu a wurin Umman, wanda tun tuni yake fatan ya samu, masalan idan yaga yanda matan abokan shi ke ba mazajen nasu kulawa, kai ko Alhaji Auwalu da ya fishi manyanta, kuma itama Hajiya Zainab ɗin tafi hajiya Kubran Manyanta, Amman kulawar da suke samu Sam bama a haɗawa.

Bata daɗe ba sai gata ta fito, hannun ta ɗauke da madaidaici Mug ɗin itama.

Zama tayi, tana mai sake sakin murmushi, sannan ta sauke kanta ƙasa, suka ci gaba da karyawar, duk da dai a matuƙar takure take.

Ta riga Alhajin ajiye cokalin ta, sai bayan da ya gama ne shima ya tattara dukkanin hankalin shi a kanta.

"Maryam Magana nake so muyi dake ta fahimta, ina fatan kuma zaki bani dukkanin goyon bayan ki, a matsayi na na wanda yanzu na tashi daga mutumen da kuke ma aiki, na koma mijinki mai gidan ki, ina fatan kin fahimta?"

Gyaɗa mashi kai ta shiga yi, cikin girmamawa da mutuntawa.

Hakan ne ya sanya shi jin daɗi, gyara zaman nashi yayi bisa kujerar yana mai fuskantar ta, da yanda zata so maganar ko kuma yanda zata fahimce shi, har ta

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login