Showing 174001 words to 177000 words out of 247770 words

Chapter 59 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10460

ɗauki al'amarin.

"Maganar Auren Suhana dai ce, jiya maneman aure sun zo daga Adamawa, kaman yanda kika sani, to saidai ban samu sanar dake yanda mukayi dasu ba, saboda muna shawara wani al'amari ne da yaya Auwalun tin jiyn. Amman alal haƙiƙa bamu amsa masu ba, daga ni har Alhaji Auwalun, dalili kuwa shine, yaron ki Al'ameen tin farko tin kafin ma ta shiga makarantar da suka haɗu da shi wancen yaro, shi Muhammadun shine ya fara zo mana da buƙatar auren Suhanan, to Amman saboda wasu dalilai acen baya, ya sanya muka dakatar dashi, sannan muka hana shi bayyana maku, har sai lokaci yayi, to kafin lokacin ne duk Abunda ya faru, ya faru. Saboda haka, inaso ki bani damar ba Muhammadu izinin neman ita Suhan ɗin, idan Allah yasa sun daidaita kansu, tana sonshi to falillahil hamdu, kinga ai gida batanƙoshi ba ba'a kaiwa dawa. Har ga Allah ni dai na yarda, kuma na amince da tarbiyyar da kika bata, hakan ce ta sanya kuma bana tunanin har zaki iya bijire wa wannan buƙatar tawa, nasan zaki ce Hajiya Kubra ita mahaifiyar Muhammadun, to inaso ki sani, ke babu ruwanki a wannan maganar, ki bar komai a hannu na, yanzu dai amincewar ki muke buƙata"

Da tsananin kallo take bin Alhaji Mustapha ɗin, saidai kwarjini, girma haiba tashi, ba zasu iya barin ta bijire wa buƙatar tashi ba, kaman yanda ya furta.

Ƙasa ta sake yi da kanta, tana mai jinjina wannan al'amarin, anya kuwa hakan zata yuwu? Ko ba hajiya Kubra ba, ai duniya sai ta zage su, sai ace son abun duniyar nasu yayi yawa, gashi dama har yanzu ta kasa fita waje balle su haɗu da su Mama talatun.

"Ko in baki lokaci ne kiyi shawara?" Alhaji Mustaphan ya faɗa cikin son jin ba'asi.

Tabbas Al'ameen yaro ne nutsattse, duk wani abu da ake buƙata wajen ɗa namiji ya tattara su, kusan ma zamu iya cewa idan ana zartarwa to shi fa ya zarta, Amman Hajiya Kubra ba lafiya bace...


Miƙewa Alhaji Mustaphan yayi, har yanzu da sauran murmushi a kan fuskar tashi, Allah sarki, dattijon arziƙi kenan.

"To shikenan ni zan fita, muna da Meeting da shugaban ƙasa, kiyi shawara da zuciyar ki, Amman inaso ki sani *Ni Alhaji Mustapha Yusuf Dambulan, ina nema ma yaro na Muhammadu Al'ameen Mustapha Dambulan, auren yarinyar ki Suhan* da fatan za'a amshi ƙoƙon barar namu da hannu bibbiyu."

Yana gama faɗar haka ya sanya kai ya wuce, yana mai faɗar "Nagode da abinci, lallai yau kada ki sanya in ta bacci a office ɗin shugaban ƙasa"

Miƙewa tayi itama, tana mai sakin fara'a, raka shi tayi har bakin ƙofar fita daga sashen nata, daga nan ta tsaya tana mashi a dawo lafiya hannun ta ɗauke da briefcase ɗin tashi tana miƙa mashi.

Amsa yayi yana mai sanya mata albarka, har ya juya zuwa ga motar tashi, sai ga mota ta shigo cikin harabar gidan.

Ɗan dakatawa yayi da shiga motar da driver ɗin nashi ya buɗe mashi ƙofa, domin ganin ko su wanene.

Hajiya Zainab ce ta fito daga cikin motar, Sanye take da tsadadden lace, hannun ta ɗauke da jikkar ta, cikin mutun ta juna ta isa ga motar ƙanin mijin nata, yayin da shima ya fasa shiga motar ya nufe ta suka shiga gaisawa.

Sai bayan da suka gama gaisawar ne sannan ta nufi sashen Umma dake tsaye tana iya hangen su.

Ɗan runguma juna sukayi, alamun gaisawa sannan suka rankaya cikin falon gabaki ɗaya, yayin da motar alhaji Mustaphan ƙirar Range Rover 2019 fara ƙar ta sanya kai ta fice daga cikin tanƙamemen gidan.

Hajiya Kubra da take tsaye jikin window ɗinta ta ɗaki daga upstair ta saki labule tana mai komawa baya, cikin ƙutawa take faɗin "ayi dai mu gani maciya amana"

Bayan ƴan gaishe gaishe irin na mata, Umman tawa ta buƙaci ta kawo ma Hajiya Zainab ɗin kayan breakfast, Amman sai tace a'a wlh sauri takeyi zata wuce ne. Dama akwai Abunda ya kawo ta ma yanzu.

Cikin kulawa Umman tawa take kallon ta.

"Umman Suhan, akan maganar yaran nan ne, ina roƙon ki da girman Allah ki amince masu su auri junan su, shi Al'ameen ɗin yaje mani da maganar wai kin hana, saboda mahaifiyar shi, haba Maryama, mahaifiyar shi ce zata zauna da ita ko shine zai zauna da ita? Ba'a aure ita aka aure ta? Ina ce itama ita taga Alhaji Mustaphan ta nuna tana son shi? Don haka ni banga abun hanawa anan ba, yara dai suna son junan su, ba tin yanzu ba, tin lokacin da aka fara kawo maganar auren su Hafsatu shima yace Suhanan yake so, aka dakatar dashi, wanda tin lokacin ni banji daɗi ba, tinda yaro yace aure yake so, kuma ga wadda yake so ba sai a bashi ba? Ko yarinyar ce tace bata yi?"

Ta ƙarashe da jefa ma umma tambaya.

Ita dariya ma abun ya bata, gaskiya ba abunda zata iya cewa da waɗannan mutanen sai godiya, ƙauna dai sun nuna mata ita, ita da yarinyar ta, har wani lokaci ta kan ji babu abunda zasu iya nema a wurin ta, ta kasa basu.

"To Alhaji Auwalu ne ya turo ni, yace inzo da kaina, kuma saƙo ne, muna neman auren Suhanan, don Allah ki bamu asamu ayi a wuce wurin, duk abunda zai biyo baya a shirye muke da mu ɗauka, indai mun samu anba yaron namu"


Da murmushi Umman ke kallon ta, sai kuma ta shiga cewa "A hajiya Zainab ya da haka kuma? Ba komai Allah ya shige mana gaba, Allah kuma ya zaɓa Abunda yafi zama alkhairi, ai Muhammadu yaron kirki ne, kuma yaro ne nutsattse Sam ba don komai na hana ba, sai don gudun zagin mutane, da kuma siya ma ita Suhanan mutunci, bana so ta sake shiga wani halin ƙunci kuma anan gaba, Shiyasa ma na amsa ma Wancen yaron malamin su, Amman tinda anyi haka Allah muke roƙo da ya shige mana gaba."

Farinciki fal a ran Hajiya Zainab ɗin take cewa" Yo wace irin maganar mutane kuma? Mutanen yanzu da idan kika biye ma faɗar su babu abun ariziƙin da za'a ƙulla, ki ƙyale su duk wanda bai zaga ba, bai shirya bane" sai kuma ta miƙe tana faɗin" yauwa ko ke fa ƙanwata? Allah ya basu zaman lafiya, kar ki wani damu, insha Allahu auren nan alkhairi ne a tattare damu baki ɗaya, nabarki lafiya, bari in leƙa sashen Kubra ɗin sai in wuce"

Itama Umman miƙewa tayi tana faɗin "to ko in raka ki ne?"

"a'a wallahi yi zaman ki, bari inje ai sauri ma nakeyi, itama dai don kar ace nazo gidan ne ban shiga ba mun gaisa"

Duk da haka har saida ta raka ta ƙofar falo, sannan ta koma ciki, yayin da Hajiya Zainab ɗin ta wuce sashen Hajiya Kubra.

Bakin gado ta koma ta zauna, tana tunano halin karamci irin na Ammi, gashi bata da wayar ta balle ta kira ta ta bata haƙurin yanda al'amari ya juye lokaci ɗaya, su duka ta tausaya masu, masalan ma shi Salim ɗin da ta kula yana ƙaunar Suhanan da zuciya ɗaya.

Runtse idanun ta tayi, tana mai kwararo ma Suhanan addu'ar zaɓin Alkhairi a cikin Al'amarin.

Ta daɗe tana sallama a sahen, sai cen ne Afnan ɗin ta fito, ga alamu ma bacci takeyi, don kayan bacci ne a jikin nata.

Cikin fara'a ta ƙara so tana gaida Hajiya Zainab ɗin.

Sai kuma ga Aunt Feena ɗauke da nasreem, jaye da Ayan, itama gaishe ta ta shiga yi cikin girmamawa.

Cikin jin daɗi Afnan ɗin take ce ma hajiya Zainab ɗin, bari taje ta kirawo Mom ɗin tasu.

To tace mata, tana mai zama ta ɗauki Nasreem tana mata wasa, tana ce ma Ayan mijin da babu cefane kyaun shi bola

Cikin fara'a suka shiga ƴar fira da Aunt Feena ɗin, ita mace ce da abubuwan duniya basu cika shan kanta ba, bata cika kula da abubuwa ba, saidai wani lokaci halin Mom ɗin tata kan ɗanyi tasiri a kanta, shima ba wai yarda takeyi ba duka, saidai halin ɗa da mahaifi, wasu abubuwan idan Mom ɗin ta cika faɗa kan yi mata zafi, duk da itama wani lokaci bata mara wa Mom ɗin tata baya.

Afnan ce ta sauko tana mai faɗin "Tace tana zuwa"

Da to Hajiya Zainab ɗin ta bita, itama zama tayi suna ɗan fira, har ake zancen Hafsat, suna so ne zasu je gidan nata kafin su wuce.

Har kusan rabin awa, Hajiya Kubran bata sauko ba, har Hajiya Zainab ɗin ta miƙe cikin ƙunar zuciya, tana mai cewa su gaida Mom ɗin tasu idan ta sauko, sai kuma gata, cikin takun ta na isassu take saukowa daga bisa matattakalar.

Bisa wata kujera mai cin mutum ɗaya tayi ma kanta mazauni.

Hajiya Zainab ɗince ta fara gaida ta cikin sakewa.

Cikin shan ƙamshi take amsawa kaman wadda akayi ma dole.

Sai kuma ta maida kallon ta kan su Aunt Feena ɗin da suke zaune, alamun su bata wuri.

Cikin mutuwar jiki su duka suka miƙe suna mai ficewa harabar gidan, basa so Mom ɗin tasu ne ta yima Hajiya Zainab ɗin wani abu, ko ba komai dai gaba take da ita, kuma Hajiya Zainab ɗin ba mace bace mai yawan damuwa da al'amurran kowa ba, tana da matuƙar sauƙin kai, sannan ga girma da ya fara kama ta, duk da cewa wani lokaci hutu baya bari a gane.

Mom ɗin ce ta maida kallon ta kan Hajiya zainab ɗin da take ƙoƙarin miƙewa.

"Dakata Hajiya Zainab, bana son sake ganin ƙafar ki cikin gida na, haka duk wanda ya dangance ki, kun yi ma Alhaji aure cin amana kun ji daɗi? , saidai ina so ku sani, Abunda zai biyo baya ba zai taɓa maku daɗi ba, kunyi matuƙar kuskure, kun manta wacece Kubra ne, ba wanda ya isa yaja dani ko ya taka ni, don haka bana son munafunci ki kiyaye shigo mani gida... "


Murmushi Hajiya Zainab ɗin ta saki, tana mai gyara zaman gyalen ta bisa kanta, sai kuma ta shiga takawa a hankali har gaban Hajiya Kubran da take zaune bisa kujera.

" Kubra kenan, ba zance ma Hajiyar ba, kin manta ne, kin manta nan gidan ƙanen miji na ne, kin manta nan ba gidan ki bane, kaman yanda nake da masani yar babu ko sisin ki acikin ginin gidan nan, ke baki isa ki hanani shigowa gidan nan ba, saidai idan kika ce kada in shigo sashen ki, wannan bana da ja akai, saboda mallaki ki ne, kuma ki sani dama cen ba don ke nake zuwa gidan nan ba, saboda mijin ki, Ayanzu kuma zan shigo ne saboda mutum biyu *Mijinki da kuma Kishiyarki* a domin haka, ki sani shigowa yanzu ma na fara, kiyi Abunda kike ganin zaki iya yi, kin manta bana neman komai a wajen ki ne, kin manta duk Abunda kike taƙama dashi baki kai mai gidan naki ba, Amman shi haka kika ga yanayi? Saboda me yasa baya yin haka? Saboda shi ya san kima da darajar ƴan adam, kuma ya san ba shine yaba kanshi ba, kuma kema yanzu baki wuce ya ƙwace ya ba ma wanda kike ganin bai kai ba, ko bai isa ba. Kince mun ma Alhaji Mustapha aure, eh lallai aure fa anyi, kuma nan gani nan bari, ba abunda kuka isa kiyi, da ana tausaya maki, ashe ke ɗin ba abar tausayi bace, mu ba mune muka ce kada ki tsaya ki kula da mijin naki ba, kina nan zaune, Maryama zata ƙwace Alhaji da duk wanda yake tare da Alhaji ki rubuta ki ajiye. Amman shigowa gida yanzu ne ma muka fara, tinda yanzu ne zamu san munje gida ba kango ba"

Kuttttt


Hajiya Zainab yau ita ce ta zage tana zuba ruwan bala'i haka? Lallai mai haƙuri bai iya zuciya ba.

Da mamaki ita kanta Hajiya Kubran take kallon ta, ita dai a iya zaman ta da ita, ba zata taɓa cewa ga ranar da taga tayi faɗa ba.

Tana gama faɗar haka kuma ta juya tana mai saɓar jikkar ta, ta nufi ƙofa da niyyar ficewa.

"Ke kika ɗauke ta a matsayin kishiya, bata isa ta mallaki mijina ba, na auren saurayi da budurwa ba ta zauna lafiya, wallahi zaku san dani kuke yi dukanku"

Ta faɗa daidai lokacin da Hajiya Zainab ɗin zata fice daga sashen nata.

Itama bata ce komai ba, ta idasa ficewa tana sakin dariya.

Afnan dake shilla Ayan a shillo, yayin da Aunt Feena take zaune ɗauke da Nasreem da har tayi bacci a jikin ta, bisa wani ɗan dandamali da akayi da zallar kankare, hankalin ta yana a kan sashen Mom ɗin tasu, don tasan komai zai iya faruwa, har yanzu Mom ɗin tasu bata huce ba, tinda gashi tin ranar ta kankara masu worning akan zuwa sashen Umman, duk yanda Afnan ɗin taso akan taje, tin kafin ma Suhan ta koma makarantar, Amman dole ta haƙura, koda suka sanar da Dad ɗin ma cewa yayi, su dakata har sai komai ya koma normal sun dinga shiga.

Hango Hajiya Zainab ɗinne, yayi sanadin tasowar Aunt Feena ɗin, ta nufo ta tana mai mata magana.

Bata share ta ba itama, haka suka jera har zuwa bakin motar Hajiya Zainab ɗin, har ta shiga motar ta tabar gidan cike da tausaya ma ƴaƴan Hajiya Kubran, masalan ma Al'ameen, Feena Afnan da Abie da yake cen american ɗin.

*********


Hankali na fa ya tashi matuƙa, gashi tun ina kiran shi tana shiga, har ta koma ma tabar shiga, a'a wai meke faruwa ne?

Haka su Khadeen suka dawo suka tada ni jiki a mace, tambaya ta suka shiga yi, banda zaɓi illa shaida masu, ko ba komai ina buƙatar wanda zamu tattauna dashi.

Suma hankalin su ya tashi, Amman sai suka shiga kwantar mani da hankali.

Jinsu dai kawai nakeyi, Amman bana cikin natsuwa

Waya ta ce dake saman cinya ta ta ɗauki tsuwwa, alamun saƙo ya shigo, da sauri na wawura in gani ko shine.

Saƙon MTN ne, hakan ya sanya nayi wurgi da wayar bisa gado, aikin banza ma kenan, su MTN ɗinnan basa gajiya da shirme, sai a lokacin da kake tunanin ganin alert ko wani muhimmin saƙo ne zasu ke damun ka da ture turen banzan su.

Miƙewa nayi ina mai ficewa daga ɗakin, komai ya dagule mani, gabaki ɗaya duniyar ta mani ƙut, ya kamata ace ko ba komai Salim ɗin ya ɗauki waya ta.

Magriba ta riga tayi, dole na shiga ɗakin na ɗaura alwala, yau fuska ta ko mai bata gani ba, tin dai bayan da nayi wanka na zura kaya na shikenan, ban tashi daga bisa sallayar ba, har aka yi isha'i.

Saida na gabatar da duka salloli na, sannan na miƙe ina mai naɗe sallayar, wanka na shiga, watsa ruwa nayi, koda zanji sauƙi.

Su khadee an duƙufa da karatu, sai gashi cikin sa'a akwai wutar nepa kuma.

Suma basu kuma ceman komai ba, sai karatun su da suke yi, ganin bana cikin Mood ne ya sanya suka ƙyalenin, har in warware sana.

Kwanciya nayi ina mai jawo littafi na, saidai babu abunda yake shiga kwalwa ta, hakan ne ya sanya ni ajiyewa na shiga jan bargo na lulluɓe jikina duka.

Wayata na jawo da niyyar kashewa, sai na hango ɗan akwati maƙale saman wayar, alamun ina da saƙo, kaman in share, sai zuciya ta ta gaza daurewa "Idan Sir Salim ne fa?" zuciya ta ta raya mani.

Buɗewa na shiga yi a hankali.

Yana yin tsarin Rubutun, da kyawun shi ne suka ɗauki hankalina, na gaza wucewa ban karanta ba.

Rubutun turanci ne a tsare, cikin grammer mai kyau, ga words ɗin sun tsaru iya matuƙa.

Ga Abunda ya rubuta.

_"Zuciya ta bata laƙanta man son abu, muddin tasan ba zata samu ba, ina mai yi maki albishir da cewa Alhaji, Umma da kowa da kowa sun yarda sun amince da auren namu. Ki shirya ma karɓar soyayya ta a koda yaushe, salon ta daban ne, kaman yanda ke ɗin kike daban a cikin zuciya ta. Ina alfahari da samun ki a matsayin uwar ƴaƴana. Kiyi bacci cikin natsuwa, ina fatan zakiyi mafarki na"_

Wuuuuuuuuu

Ai bansan lokacin da na duro daga bisa gadon ba, Sir Salim ne, Sir Salim ya turo mani saƙo, Su Dad sun yarda.

Abunda nake faɗa kenan, ina tsaye tsakiyar ɗaki kaman wadda akayi ma allurar tsayuwa.

Dukansu litattafan nasu suka ajiye, suna mai tasowa domin duba saƙon, sannan suka rungume ni suna mai faɗin


"wow Suhan, waɗannan zafafan kalamai haka? Wallahi sun tafi da imanin mu, dama haka Malam ya iya kalamai?"

Komawa nayi bisa gadon, ina mai zama, cikin tsabar farinciki, gashi gabana dai bai bar faɗuwa ba, amman murnar da nake ciki ta hana ni kula ko ankara.

Ba da numb shi ba kenan yayo mani saƙon.

Abunda zuciya ta ta raya mani kenan, ƙoƙarin kiran layin nakeyi, Amman ana faɗa man ba zai iya shiga ba. Layin shi na ainahi na kira, ya shiga Amman ba'a ɗaga ba, ban damu ba, sai ma sake sakin murmushi da nayi ina mai cewa "Ƙila wani abu yake yi."

A haka muka zauna muna ta fira mai daɗi da su Khadeen da suka kula ina cikin farinciki.....



~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login