Showing 159001 words to 162000 words out of 247770 words

Chapter 54 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10468

amman ko a yanayi da yanda fuskar ta ta nuna ita ɗin ba mai zafi bace.

Kowa dake falon ya gaida Umman tawa, banda Saudat da Nihal suma da suke bin mu da wani irin kallo na tsana.


Nikau da nake zaune cen ƙasa gefen Afnan ta kama hannuna ta matse taƙi saki, nima jikina da hijabi, fuskata tayi luhu luhu, Allah ya sanya lokacin da afnan ɗin ta shiga kirana Salla na gama ba kukanba, saida tayi ihun murnar ta mai isar ta, na jin daɗin gani na, sannan ta faɗa mani saƙon Dad ɗin nasu.


Kallon shi gabaki ɗaya da hankalin shi yana kanta, yana kula da yanayin ta, watau tasha kuka kenan bayan wanda yaga ta tanayi ɗazu.

Saida Bilal ya zungurobshi sannan ya iya janye idanun nashi a kanta, wanda har Hajiya Kubran ta lura da Kallon da yake yi ma a Suhan ɗin.



Gyaran Murya Dad ɗin yayi, yana mai muskutawa ya fara buɗe taro da addu'a

Sannan ya fara jawabi kamar haka.


"Na tara ku ne anan ba don komai ba, sai don in gabatar maku da abokiyar zaman mahaifiyar taku, daga yanzu wannan itace a matsayin abokiyar zaman Mahaifiyar taku, ina fatan zaku yi mani biyayya wajen bata girman ta, da kauce ma duk wani abu da zai kawo saɓani. Ku sani yanzu ba matsayin ta na mai aiki take ba, matsayin matar mahaifin ku take,kaman mahaifiya take a wurin ku, ku girmama ta kaman yanda zakuyi ma mahaifiyar ku nan da take zaune, sannan ki darajta ta, ga Suhan nan, ku ɗauke ta matsayin ƴar uwa, bana so inga wani banbanci a tsakanin ku, masalan ma ku Saudat Da Nihal, ina fatan zaku kiyaye.......


*"Alhaji dakata"*

Hajiya Kubran ta faɗa cikin kashin murya, tana mai zaburowa daga inda take zaune bisa Sofar.


*"Ni ba abokiyar zaman ta bace, kuma ita ba kaman mahaifiyar ya rana bace ba, ni a wuri na maci amana ce, kuma ina sonka sani daga yanzu har yaumuttanadi ba zan taɓa amsar ta ba a matsayin kishiya, san amshe ta ne a matsayin aiki wadda taje zaune a gudana cikin rigar alfarma ta, tana cin dukiya ta da nufin ta kare kanta daga Raɗaɗin talaucin da take fama dashi tin shekara da shekaru, muddin tana zaune a ƙarƙashin rufin gidan nan nawa, ba zata taɓa amsa sunan matar guda ba, saidai ƴar aikin gida, tinda wannan auren babu Abunda yake cikin shi sai cin amana da mugunta kawai*

Ba Alhaji Mustapha ba, hatta Afnan da Feena, Bilal da uwa uba Al'ameen da suke zaune a falon saida maganar tata ta Dakar masu zuciya.

Cikin tsananin furgici Al'ameen ɗin ya ɗago kai yana mai ƙure Mom ɗin tashi da idanun ta ya rufe ga kallon gaskiya yake yi.

Shi kau Bilal saidai sauke kanshi ƙasa yayi yana mai ɗan girgiza kai, yayin da Feenar take kallon Mom ɗin nata da wani irin kallo kaman ta nutse ƙasa.

Ni kau tare da Afnan a lokaci guda muka kai kallon namu a bisa fuskar Umman tawa, domin ganin yanda ta karɓi maganar Hajiya Kubran.

Ga ɗin bin mamakin mu, murmushi ne kwance bisa fuskar Umman tawa, har kana iya hango fararen haƙoran ta, a lokaci guda na janye idanuna na maida su kan su Saudat ɗin da farin ciki fal a zuciyar su kaman zasu taka kan jariri....


_Ku godewa Allah fa, nima na fara koyon ƙyuyar typing, tinda kuma kun iya ƙyuyar comment. Sai kuma sati na sama_





~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._


*Page ~46~*

*Aslm Alkm.Fans da fatan duk kuna cikin ƙoshin lafiya. Sabili da yawan ƙorafe-ƙorafe da nake samu daga gareku, da yawan roƙo na, da masu kirana a waya, da masu mani Dm da masu bina Pc akan in taimaka inyi typing, na yanke shawarar baku koda kaɗan ne ba yawa, ba don na kammala uziri na ba, ba don ayyuka na sun koma normal ba, sai don in faranta maku rai, haƙiƙa har kullum masoyi yafi maƙiyi, Rubutun nan dan ku nakeyi, domin jin daɗin ku ne, domin idan babu ku, tabbas fa babu mu, Amman sai wasu daga cikin readers su kasa gane haka, su sun ɗauka idan kace zaka yi rubutu baka da aikin yi ne (Jobless). To inaso ku sani ba haka abun yake ba, kawai dai sa kai ne wanda yafi bauta ciwo. Masu yawan damuna akan nayi typing wannan Page ɗin naku ne har abada, kuyi yanda kuke so dashi. Daga ƙarshe ina mai roƙa ma sister ta lafiya a wurin Allah, ina so kuma ku taya ni da addu'a, duk da nai nasan kuna yi, inaso ku ƙara sosai my fans. Allah ya barmu tare Abadan da'iman. Ina sonku tsakani da Allah. Ngd*



°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°



Babu wanda ya katse ta har ta kai aya, haka babu wanda ya tanka har kawo yanzu da falon ya ɗauki shiru.

"Kubra ke ba zaki cenza ba ko? A gaban yara kike faɗar irin waɗannan kalaman? Maryam dai matata ce, itama auren ta nayi kaman yanda na aure ki, kuma ba ƴar aiki bace ma a yanzu kaman yanda kika faɗa, Amman wannan ba irin maganar da zamuyi bace a gaban yara, ki kiyaye hakan ko don gaba"

Muka tsinkayi muryar Alhj Mustaphan yana mai maida ma Hajiya Kubra maganar tata.


Ƙara duƙar da kan namu mukayi ƙasa, yayin da su Saudat jin haushi ji suke kaman su rufe Dad ɗin nasu da duka, zunɓura baki suka hau yi sun murguɗe murguɗen baki.

Umma ta dai har ila hazar yanzu bata ce komai ba, sai dai ɗan murmushi da take ta faman yi, babu ko alamun damuwa akan fuskar ta.

Ita kanta tasan abunda tayi ba daidai bane, ta sani abunda tayi don Hajiya Kubra ta kira shi cin amana ba laifi bane, kowa ma zai iya kiran shi hakan, muddin yaji yanda abun yake. To saidai bata jin wannan dalilin ya isa daƙile nata dalilin da take dashi cikin zuciyar ta.

Alhj Mustaphan yayi maganganu masu daɗi da fa'ida, ya kuma ja hankalin Haj kubran da yaran nata akan su haɗa kansu, baya so su kawo mashi wani tashin hankali a cikin gida, duk wanda ya samu da hakan, zai mugun saɓa mashi.

Sannan ya umurce mu da mu tashi kowa ya koma part ɗin shi, yayin da ya buƙaci Hajiya Kubra da Umman akan su su zauna yana da magana dasu.

Sannan yace Ya Ameen ɗin kada yayi bacci yana son ya ganshi idan ya kammala da iyayen nashi.

Haka muka tashi da niyyar ficewa.

"Suhan yaushe ne zaki koma makaranta?"

Muryar Alhaji Mustaphan ce ta doki dodon kunne na daidai lokacin da nake ta faman sauri domin barin falon, da nake ji na kaman a ɗaɗɗaure, yawan aika mani da harara da Hajiya Kubran takeyi.

"Gobe idan Allah ya kaimu"

Na faɗa kaina a ƙasa, bayan na dakata daga tafiyar da nakeyi,ina mai ɗan waiwayawa na kalle shi.


"To Allah ya kaimu"

Ya faɗa yana mai nuna alamun da in tafi. Cikin matuƙar sakewa kaman kaman yanda yake yi ma yaran nashi.

Da hannu ya yafuto ya Ameen da bai kai ga miƙewa ba shi.

Inda yake ya isa, gami da ɗan russunawa domin sauraren Dad ɗin nashi.


"Kuje ka kai ta tayo shopping ɗin komawa makaranta, zuwa gobe ka maida ta makarantar da kanka, bana so a haɗa ta da driver"

Ya faɗa ta yanda ba wanda zai iya jin me ya faɗa, gudun wata fitinar ta daban.

A hankali ya miƙe yana mai faɗin "to Dad."

Da hannu yayi ma Bilal alamun da suje.

Shima a hankali ya miƙe yana mai yima su Dad ɗin sai da safe.

"Bilal zamu je mu kai yarinyar cen shopping inji Dad"

Ya Ameen ɗin ya faɗa daidai lokacin da suke barin sashn mom ɗin tashi.

"Kai bros, kuje kawai wallahi bacci nake ji, ina so in ƙara sa gida ne, Kaga Ummi ba lafiyar kirki"

Ya faɗa cikin son kauce ma rakiyar, yayi hakan ne saboda kada ya shiga haƙƙin masoyan.

"Muje sai mu sauke ka"

"To ai shikenan, ina jiran ku a mota", ya faɗa yana mai amsar key ɗin motar a hannun Ya Ameen ɗin.

Yayin da Ya Ameen ɗin ya juya kai tsaye ya nufi sashen su Suhan ɗin.

A falo ya tadda ni, tsaye nake na juya baya, hijab ɗita na a hannu na da na riga na fidda tin shiga ta sashen.

Zuciya ta cunkushe, bana so Haj Kubran ta ƙara ci ma Ummata zarafi a kalaman ta, in da son samu na ne, ƙafata ƙafar Umman muyi dawowar mu a tare, domin nasan dukkan Abunda Alhaji Mustaphan zai faɗa ma Hajiya Kubra ba wai ganewa zata yi ba.

Ya ɗan jima tsaye daga baya na yana ƙare mani kallo. Hannayn shi duka soke cikin aljihun wandon nashi.

A hankali ya shiga takawa yana nufar inda nake tsaye.

Jin takun tafiya daga bayana, ba ƙaramin tashin hankali da tsoro na shiga ba.

A firgice na juyo da niyar kwarara ihu, domin Nidai nasan babu kowa a sashen namu, gashi naji takun tafiya, kuma yanzu na baro ummata Sashen Hajiya Kubra.

Cikin azama ya sanya hannu gami da toshe mani baki na duka, yana mai ɗan tallafo ni zuwa jikin sa kaɗan, ganin kaman nayi baya zan faɗi.

"Matsoraci ya"

Abunda ya faɗa kenan, yana mai bin duka fuska ta, da idanuna da wani irin kallo, da na gaza fassara ko na menene.

Ajiyar zuciya na sauke, ina mai ɗan matsawa baya kaɗan daga jikin nashi.

Sai kuma na koma bisa kujera na zauna, ina mai dafe kaina da har ya fara sa rawa, tsabar tsorata.

Da kallo yake bina har yanzu, ganin bance komai ba, sai kuma ya fara takawa zuwa fita daga falon

"Ki shirya ki same ni mota yanzu, zan kaiki kiyi siyayyar makaranta"

Bai jira cewa ta ba, ya idasa ficewa daga falon.

Nima da kallo na bishi, oooh Ya Ameen, mai hali baya barin halin shi, komai nashi da yake aiwatar wa, cikin miskilanci yake yi kaman ma baya son yi, a hankali na miƙe ina mai zura hijab ɗita zuwa cikin ɗakin domin na duba fuska ta.

A mota ya samu Bilal ɗin yana ta faman jiran shi.

"Friend ya dai? Hankalin ka yayi gida wajen ummi ko?" ya faɗa cikin ƴar zaulaya da ya kan yi idan ya so, yana mai zama cikin motar, ƙafar shi ɗaya a waje bai kullo ƙofar ba.

"wallahi friend tana jin jiki ne, ni ina ma tunani ko gida zan maida ta, domin a kula da ita sosai, nauyi take ji sosai yanzu na jikin ta"

"Gaskiya kam Friend, idan kana ganin ba matsala, You can allow her to go, Kaga kai ba isasshen time ɗin zama gidan ke gareka ba"

"ehhh kuma....."

Ƙarar buɗe motar ne ya sanya su juyawa gabaki ɗaya.

Ƙamshin turarn ta ne ya fara yi masu sallama, kafin kyakkyawr ƴar madaidaiciyar zagayayyar fuskar ta ta bayyana cikin motar.

A tare Bilal da Ya Ameen suka kalli juna, sai kuma ya Ameen ya janye tashi yana mai gyara zaman shi, gami da maida ƙafar shi cikin motar ya rufo ƙofar motar.

Nima rufowa nayi ina mai gaida ya Bilal ɗin, saboda lokacin da muka haɗu sashn Hajiya Kubra bamu samu damar gaisawa ba..

Amsawa yayi cikin sakin fuska, yana mai ɗan zaulaya ta da cewa na ɓoye.

Ɗan murmushi kawai nayi mashi, ina mai wasa da yatsun hannuwa na.

Sai kuma motar ta ɗauki shiru, na tsawon wani lokaci har muka ƙara sa bakin gate ɗin gidan na Bilal.

Ya Ameen na ƙoƙarin danna horn, mai gadi yazo ya buɗe ne Bilal ɗin ya dakatar dashi ta hanyar cewa "Kaga malam ajiye ni nan, ya isa, kada kuyi dare fa"

Dakatawa yayi ba tare da yace komai ba, saida Bilal ɗin ya fita ya zagaya ta ɓangaren shi, sannan sukayi musabaha tare da yin sallama.

Nidai kallon su kawai nakeyi, Amman ƙaunar junan sun na matuƙar burgeni, duk duniya banga wanda Ya Ameen ke sake wa da sakin jiji dashi ba kaman Ya Bilal ɗin.

Haɗuwar jini, ƙauna, abota daga Allah.

Har ya shige gidan muna iya hango shi, rufo ƙofar gidan ce tayi daidai da sauke ajiyar zuciyar Ya Ameen ɗin. Sai kuma Naji yace


"Dawo gaba"

Da ɗan mamaki nake kallon shi, sai kuma nace "I am comfortable here"

"Am not asking you dear, i am jst commanding you, ko kin manta ni ba driver bane?"

Ɗan murmushi na sauke, yau ya Ameen ne da yin faɗa har haka? Ji yanda yaje magana kaman ana karanta mashi...


Sauke kaina ƙasa nayi, bana da niyyar ma ko motsawa.

Ji nayi ya kawai kashe motar. Sai kuma ya jawo wayar shi haɗo da kunna data, yana mai ɗan kwantar da kujerar sit ɗinshi ya cigaba da latse latsen shi.

A hankali na ƙure shi da idanuna ta bayan motar, hasken wayar tashi ba mai yawa bane, amman duk d a haka zan iya hango farar fatar fuskar tashi, da take cike da siririn sajen da ya kwata luf akan fuskar, gashin idanun shi Zara Zara, sunyi ma kyawawan idanun shi, masu kama da yana jin bacci kyau, girar nan tashi kaman an zizara mata kwalli, ta tsaru iya tsaruwa.

A hankali na janye idanuna, ina mai sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya, ganin ya kashe hasken wayar yana mai lumshe idanun nashi tare da ɗora Zara zaran yatsun hannun shi bisa fuskar shi.

Mu biyu haka acikin mota mai duhu? Ga Ƙamshin turaren shi, da ya haɗe da Ƙamshin humra ta da sanyin cikin motar ya saukar mani da wata irin kasala.

A hankali na ɓalle murfin motar, ina mai ficewa daga cikin motar naja na tsaya, ina mai jingina baya na da ƙofar motar.

Duk motsin ta yana kula dashi, ganin ta fice ne ya sanya shi tashi zaune, yana mai sakin ɗan murmushi na gefen baki.

Wato ita taurin kai zata nuna mashi, ko kuma jan aji ne irin na mata? Tinda ya furta mata yana sonta, ya kula da wani shasshare shi da takeyi da ba zai iya cewa ga ko na menene ba.

Shima ɓalle murfin motar yayi ya fito.

Cikin takun shi mai ƙara kada mani gaba ya iso ta inda nake tsaye.

Sai kuma ya ja ya tsaya, hannayen shi zube cikin aljihun wandon nashi, idanun shi dukan su bisa fuskar tawa da hasken farin wata ya haske.

Sai kuma ya zaro hannun yana mai duba agogon dake ɗaure bisa wutsiyar hannun nashi.

Baice mani komai ba, sai naga ya sanya hannu ya buɗe sit ɗin gaban, yana mai nuna mani da in shiga.

Sake ɗauke kai nayi, nima bansan menene haka ya shiga kaina ba yau, Amman jina nakeyi a sama, kaman wata sarauniya mai mulki.

Ban aune ba naji ya kamo ni duka na, yana mai saka ni cikin motar gabaki ɗaya na, sai kuma ya rufe yana mai danna key.

Zagayawa yayi shima ya shiga motar, ba tare da ya ko kula ni ba, ya fizgi motar kaman zai tashi sama, har yanzu fuskar shi bazaka taɓa cewa ya taɓa dariya ba.

Har muka ƙarasa daidai super market ɗin ba wanda yace da kowa komai.

Ɓalle murfin motar yayi yana mai ficewa kai tsaye, nima ban da wani option illa na fitowr.

Gaba yayi ina biye dashi a baya.

Na ɓata mashi rai na sani, Amman hakan ba shi ke nuna nice mai laifin ba.

Tsabar girma da jin kai nashi, shine abu na farko dake ɗawainiya da Ya Ameen ɗin.

Wato shi yana da kuɗi, yana da kyau, yana jin cewa dole abi umurnin shi ko? Ga miskilanci yana fama dashi.

A haka har muka ƙarasa ciki.

Nuni yayi mani da ɗan ƙeƙen da ake zuba kaya. Alamun in ɗauka in ɗebo kayan.

Kenan dai ba zaiyi mani magana ba yake nufi?

Ɗan murmushi nayi ina mai wucewa kai tsaye ga zaɓen kayan.

Yayin da cikin girmamawa aka sanya aka ajiye mashi kujera ya zauna daga gefen accounter ɗin.

To nima dai ba komai na ɗina ba, kasancewr abincin ma ba damuna yayi ba, kuma ni ban iya almubazzaranci ba, nasan idan ummata taga siyayya da yawa ma, faɗa zata yi.

Haka na turo keken wani gulu gulu, har zuwa wajen accounter ɗin.

Da kallo ya shiga bina, ganin na taho ina turo keke duk da kayan basa da yawa, amman kaman zan kife.

Miƙewa yayi yana mai bina da kallon tuhuma.

Sai kuma ya ƙara gimtse fuska tamau.


"Wuce mu koma"

Ya faɗa cikin wata irin murya, da gani har yanzu yana cike dani sosai.

Ba musu na sake juyawa, ina mai wucewa.

Hannuwan shi naji kwatsam a bisa nawa, yana mai kama handle ɗin keken.

A hankali na zare nawa ina mai ɗan ja da baya.

Me ke damun shi ne wai? Ɗabi'ar turawa na neman yin tasiri a Al'ada da addinin nashi.

Gashi dai mutum mai addini, ga yawan ibada, Amman bai ɗauki haɗa jiki dani ba a matsayin komai.

Ji na da yake yi kaman Afnan, ai ni ba Afnan ɗin baceba. Kenan ma yana ganin don Mahaifiyata ta auri mahaifin

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login