Showing 147001 words to 150000 words out of 247770 words
tashi cike fal da farin ciki.
Gaida Alhaji Mustaphan nayi, ya amsa cikin sakin fuska sosai, Abunda ke ƙara ma Alhajin Daraja kenan a idanun mu.
Sai kuma ya shiga takowa a hankali cikin salon tafiyar shi mai cike da natsuwa.
Yayi masifar kyau cikin hasken fitulun da suka haske ilahirin gidan tar kaman rana.
Daidai inda muke tsaye yaja ya tsaya, sai kuma ya shiga gaida ummata cikin girmamawa, sautin muryar shi na futa a hankali cikin wani irin amo da ya ƙara rikita ni da birkita mani tunani na.
Itama Umman tawa amsawa tayi, saidai wannan karon ba irin amsawar da nasan tana yi ma ya Ameen ba, Amsawa ce mai cike da dakiya irin ta ɗa da uwa.
A'ah
Me yake shirin faruwa ne wai?
Bai ko kalli inda nake tsaye duƙe da kai ba, ya sanya kai ya wuce zuwa sashen nashi.
Da idanu nake bin ilahirin gidan da ya wadatu da shukoki masu ban sha'awa.
Gine ginen ma kusan zamu ce an cenza su, ko ina tsit kake ji ba ƙarar komai sai na kukan tsuntsaye masu daɗin sauraro.
Alhajin ne ya kwala ma Mudi dreba kira, da gudun shi ya taso yana mai faɗin "ranka ya daɗe gani"
Kayan mu da driver ɗinda ya kawo mu mai suna Mahi ya fiddo mana ya shiga nuna mashi da hannu yana mai cewa su kwaso kayan su shigo mana dasu.
Maimakon inga mun nufi sashen masu aiki, sai naga mun nufi wani ɓangare mai kyau, wanda ada sashen Alhaji Mustaphan ne na sani a wurin.
Da makullin da yake hannun shi yayi amfani ya buɗe sashen.
"Masha Allah".
Itace kalmar da na fara furtawa lokacin da na saka ƙafar tawa cikin tanƙamemen falon da ya wadata da kaya masu masifar kyau kalar royal blue da maroon.
Umma ta na biye a bayana, itama ga dukkan alamu sashen nata ya matuƙar burge ta.
Sai a lokacin na fara dawowa hayyacina.
"wai ba dai ummata ce ta auri Alhaji Mustaphan ba" na faɗa a cikin zuciya ta ina mai kai zaune bisa wata luntsumememiyar kujera da ta wadatu da fuloli burjik kaman na gidan sarauta.
Gaba na ne ya shiga faɗuwa, Alhaji Mustaphan ne ya shiga gaba, umman tawa tana biye dashi har ɗan corridor ɗin da yake ɗauke da ɗakunan bacci guda uku.
Na farko ɗakine da yake ɗauke da kaya gwanin ban sha'awa, komai kala ɗaya ne dana falon, sai na biyu kuma shi gabaki ɗaya kalar maroon ɗinne da surkin Ash colour masu matuƙar kyau da ɗaukar hankali.
Na cen ƙurya shine yafi kowanne tsaruwa, kaya ne ƴan uban su, ba kalar na ƙasar tamu bane.
Komai na falon fari ne tas, hatta da kalar fentin upwhite ne. Kuma ko wanne ɗaki da toilet ɗinshi.
Gaskiya sashen yayi ba ƙarya, na biyun shine aka nuna a matsayin nawa, sai na farkon wai na ummata ne ɗana cen ƙurya ɗin.
Da matuƙar mamaki nake binsu da kallo, yau Ummata ita ce a matsayin amaryar Alhaji Mustapha Dambulan???
Falon muka dawo inda muka tadda ƙofofi guda biyu, ɗaya ta balcony ce, yayin da ɗayar take ta makeken kitchen ɗin da yasha carbinet mai masifaffen kyau, ba tarkace a cikin kitchen ɗin, saidai komai akwai.
Duka ɗakunan suna da Ac da manyan tagogi, sai falon shima haka, Amman shi ac ɗinshi Central Ac ce tana daga cen saƙo kusa da inda dining table da water dispenser take ajiye.
Amman sanyin ta ya wadaci falon gabaki ɗaya, harma kusan mu ce yayi yawa.
Sallama Alhajin Yayi mana ya fita yana mai cewa yana zuwa.
Da kallo nake bin Ummata ina ta raya abubuwa da dama acikin zuciyar tawa.
Ita ko ko sau ɗaya bata kalle ni ba, wata irin ƙarfin guiwa ne nake hangowa tattare da umman tawa, ta yanda naga ta shiga ƴan aikace aikacen ta hankali kwance.
Toh fa, ikon Allah saidai kallo.
Ceman tayi in tashi in shiga ɗakina inyi wanka in kwanta in huta kafin a kawo mana abinci.
A sanyaye na tashi ina mai nufar ɗakin da akace wai mallaki na ne, da ban gama yadda ba, har yanzu gani nakeyi mafarki nakeyi, nice yau a gidan Su ya Ameen ɗin da irin wannan matsayin na mallakar ɗaki sukutum.
"To amma shi ya sani kuwa?"
Tambayar da nake ta nanata ma kaina kenan, gashi naga sai wani ɗaɗɗaure mani yake yi kaman na kashe mashi uwa.
*******
Kai tsaye ɗakin Ya Ameen Alhajin ya nufa, ba zan iya cewa ga tsayin lokacin da ya ɗauka bai taka sashen yaron nashi ba.
Ba kowa falon sai Ac da take ta faman yi a hankali a hankali.
Bedroom ɗin ya tura, hango shi yayi zaune tsakiyar gado, har ya cenza kaya zuwa na bacci, laptop ɗinshi ce gaban shi yana ta faman latsawa.
Tura ƙofar da akayi ne ya sanya shi maida hankalin shi wurin.
"Dad" ya faɗa da mamaki, yana mai saukowa cikin hanzari, yana fatan dai ace lafiya, saboda tin bayan shigowar tashi ɗakin zuciyar shi ke kai kawo akan dawowar su Suhan ɗin a cikin gidan, ba zai ce baiyi murna ba, to saidai fa shi yaso ne ace sun dawo a matsayin masu matsayi a cikin gidan ba ƴan aiki ba, saboda yanzu baya jin idan zai iya lamuntr irin wancen wulaƙancin da akayi masu a Wancen zaman nasu.
"Lafiya ƙlau kake kuwa son? Naga ina ta magana kana cen kana tunani"
Dad ɗin ya faɗa yana mai jawo stool ya zauna bisa, yana mai ɗora hannun shi kan madubi da yake ajiye gefe irin na maza.
"komawa yayi ya zauna bakin gadon, yana mai faɗin" Lafiya lau dad" ai na ɗauka ka kwanta ne"
"A'a ban kwanta ba, baƙi nake so ka nemo ma abinda zasu ci"
"Baƙi kuma Dad? Su wanene baƙi?"
"Umman ka" Alhajin ya faɗa kai tsaye ba tare da wani shayi ba.
Bai kawo komai ba, yana mai faɗin "To Dad, yanzu kuwa insha Allah"
Ya faɗa yana mai miƙewa tsaye haɗi da zaro jallabiyar shi ya sanya yana mai nufar ƙofa da niyyar ficewa.
"am Al'ameen, idan ka kawo ka miƙa mata sashen ta"
Ɗan dakata wa yayi daga barin tafiyar da yaje yi, sai kuma ya ɗan waiwayi yana kallon Dad ɗin nashi
"Dad ina ne sashen nata?" ya faɗa cike da mamaki
"Zo nan" Dad ɗin ya faɗa yana mai kiran shi da hannu
Dawowa yayi da baya ya samu gefen gado ya zauna, yana mai tattara dukkan natsuwa shi ya ɗora ta kan Dad ɗin nashi.
Ɗan gyaran murya kaɗan Dad ɗin yayi yana mai gyara zaman shi.
"Umman taka yanzu ai ba ƴar aiki baceba, *Matata ce* Daga yanzu kafin ta zama taka surukar ta zama uwa a wurin ku gabaki ɗaya"
Cikin sakin baki da ƴar gigita wadda Al'ameen ɗin be bari ta bayyana a kan fuskar shi ba, yake kallon Dad ɗin nashi.
Bakin shi yayi matuƙar nauyi harma ya gaza iya magana.
Jin Al'ameen ɗin bai ce komai bane ya sanya shi ɗorawa da faɗin
"Wannan shine tsani, shine matakin samun auren yarinyar a wurin ka, domin ko da muka je ma mahaifiyar da maganar ta auren naku ƙiyawa tayi, tace akwai maganar wani a kanta, to sai muka yanke shawarar hakan da Babanka Auwalu akan cewa bari in auri ita maryamar kaga alabasshi ko yaya ne ina da ɗan iko akan Al'amarin yarinyar. Amman ku fahinceni, masalan ma kai da duk dan kai ne nayi wannan abun, da kuma tausayawar da muke yi ma matar"
Tabbas ya gamsu iyaka da zancen Dad ɗin nashi, to saidai ba'a nan matsalar take ba, Mom, Mom ita ce babbar matsala, tabbas yanzu ne za'a fara tashin hankali, duk da cen ba'a yi komai ba.
Tuni zullumi da fargaba suka shiga Al'ameen ɗin, to saidai bai ce komai ba, ya shiga ɗaga ma Dad ɗin nashi kai alamar gamsuwa.
Miƙewa yayi yana mai faɗin "to Dad Allah ya sanya Alkhairi, don Allah kayi ta haƙuri da Mom saboda gaskiya za' a fuskanci wani irin yanayi a cikin gidan"
Da kallo Dad ɗin yake bin Ya Ameen ɗin da har ya fice daga cikin ɗakin.
********
Sai dai koda ya shiga motar kwalwar shi Sam ta cunkushe, rasa inda zai nufa siyen abincin yayi ba kuma wai don babu wurin siyarwa bane, tsabar tunani ne kawai da zullumi. Karkata kan motar tashi yayi ya nufi gidan Aminin nashi.
Har sun kwanta ya sanya mai gadi ya buɗe mashi ya shiga.
Parking yayi, yana mai zaro wayar tashi daga aljihu ya danna kiran Bilal ɗin.
Cikin ɗan bacci da ya fara fizgar shi, yaji wayar tashi na ruri, sunan Friend da yagani ne jiki ya sanya shi tashi zaune, sannan ya ɗaga.
Sanar mashi yayi da gashi harabar gidan shi, cikin ɗan ruɗewa ya sauko daga gadon a hankali kada ya tada Ummin da ta samu bacci ya kwashe ta ga ciki da yayi matuƙar girma a jikin ta.
Fitowa yayi daga shi sai singlet da boxer. Ilai kuwa motar Al'ameen ɗin ce fake gefe.
Ba wata wata ya shiga motar yana mai faɗin "Friend Lafiya A Daidai Wannan Lokacin?"
Ɗan shiru Al'ameen ɗin yayi idanun shi a kulle, sai kuma ya buɗe su yana mai wara su akan abokin nashi.
"Friend akwai matsala, Dad ɗina ya ƙara aure, bama wannan ce matsalar ba, Mom, Mom ita ce matsalar, idan har taji maganar ƙarin aure kuma da wadda ya aura"
Da mamaki Bilal ɗin ke kallon Al'ameen, saidai shima ya gaza cewa komai, saida aka kusan ɗaukar Second ashirin sannan ya iya cewa
"Friend gaya mani wacece ya aura? Kuma yaushe? Ya akayi kowa bai sani ba? Ko dama kai ka sani faɗa man ne baka yi ba?"
Girgiza kai Al'ameen ya shiga yi, yana mai faɗin "Umman Suhana ya aura, kuma yau ta tare, ya kake gani idan Mom ta dawo gobe ƙasar ta tadda wannan al'amari? Kadai san wacece Mom ɗita ba sai na baka labari ba, kasan halin ta kasan ne zata iya aikatawa, beside ma ina tausayin yarinyar, hakan na iya zama tarnaƙi tsakani na da ita, duk da shi Dad a ganin shi wannan ce hanya mafi sauƙi ta samun Suhan ɗin a wuri na, shi ko tunanin Mom ɗin ma baya yi, da Abunda zai iya zuwa ya dawo"
Al'ameen ɗin ya faɗa cike da ƴar damuwa a saman fuskar shi.
Ajiyar zuciya Bilal ɗin yayi, tabbas ya san Mahaifiyar abokin nashi, Sam mutumci ko karamci bai cika taba, da akan yaronta takeyi, gani takeyi kaman zasu mallake nata yaro, sai gashi abun ya juye ya koma kan mijin nata, kafin yazo ga kan ɗan nata.
Lallai akwai cakwakiya zalla a gidan nan, saidai fatan Allah ya kare kawai.
Muskutawa yayi yana mai faɗin. "Friend ka kwantar da hankalin ka, kada wani abu yazo ya same ka kawai, kayi ta addu'a, kuma kabar lamarin a hannun Abba, a shawarce kada ka sanya kanka ciki, in da hali ma, kada ka zauna a gidan gobe..."
" Bazan iya ba Friend, ko ina zanje hankali na yana a kanta, gani zan kaman wani abu zai same ta, a yanda na gani a saman fuskan ta, kaman itama bata san komai ba, Friend mafita nake nema please"
Ya ƙarashe ya mai bin kwayar idanun abokin nashi da kallo.
"To kuwa dole kayi kaman baka san me ke faruwa ba, dole ka bar zancen yarinyar for now, kada ka sake ka nuna ma Mom ɗin buƙatar taka akan Suhan, in ba haka ba kuwa abun zaiyi zafi sosai, ko da komai zai faru a gaban ka, kada ka nuna kana da intrest akan yarinyar, ka daure ma ranka, ka daure ma zuciyar ka please, komai zai zo da sauƙi, yanzu bari in zuro jallabiya muje mu nemo masu abincin"
"a'a ka bar shi kawai, zamu haɗu zuwa da safe, kana bacci na tada ka, ka koma ni zanje in nemo masu"
Al'ameen ɗin ya faɗa yana mai tada motar, fita Bilal ɗin yayi yana mai rufo mashi ƙofar ya matsa baya, har Al'ameen ɗin ya fice sannan ya koma cikin gidan.
*******
Abinci mai rai da lafiya ya siya masu, harda ruwan sha na gora masu yawa da kayan tea, sannan ya nufo gidan.
Tura ƙofar falon yayi cikin sallama ya shiga, zaune nake bisa kujera na takure saboda ɗan sanyin da yake ratsa ni, ummata kuwa tana cikin ɗaki bansan Abunda takeyi ba.
Bai ko kalli inda nake ba ya wuce kai tsaye bisa dining table ya ajiye manyan ledojin hannun shi.
Juyawa yayi da niyyar zai fice na taso a hankali ina mai kiran sunan shi cen ƙasan maƙoshi
"Yaya"
Ɗan tsayawa yayi, sannan ya juyo yana mai fuskanta ta, "Lafiya?"
Ya faɗa cikin amon murya dake nuna kaman na takura mashi.
"Yaya ina jin tsoro, bansan Abunda zai iya faruwa ba, please kaba Dad shawara a warware auren nan don Allah"
Na faɗa murya cen ƙasan maƙoshi.
Wani irin tausayin tane ya tsirga mashi, lallai ya ƙara tabbatar wa ba tare da sanina komai ya faru ba.
Takowa ya shiga yi har inda nake tsaye, duk da kaina yana a ƙasa, wasu irin siraran hawaye ne masu ɗumi ke sauka akan fuskar tawa, har ina iya juyo saukar numfashin shi a hankali.
A hankali ya sanya hannun shi duka ya ɗago fuskar tawa, wara idanu ya shiga yi saman tawa fuskar yana son gano dalilin da ya sanya ni kuka haka lokaci ɗaya.
Runtse idanuna nayi, wasu hawayen na ƙara malalowa. Da hannayen shi yayi amfani wajen ɗauke mani hawayen. "Is ok Suhan, babu Abunda zai faru sai Alkhairi kinji" ya faɗa cike da tausayawa, wata irin soyayya na fizgar shi, ji yake yi kaman ya rungume ta ko ya samu sassaucin Abunda yake ji a cikin zuciyar shi.
Ɗan girgiza kaina na shiga yi, ina mai janye kaina daga ruƙon da yayi mashi.
Sai na juya da baya da niyyar tafiya ɗakin nawa.
"suhhaaaaan" ya faɗa cikin murya siririya tana cracking
Tsayawa nayi ban juyo ba.
Ƙafa ya ɗaga taku biyu ta kawo shi ta inda nake tsaye.
Da hannuwan shi yayi amfani wajen kamo nawa.
"Nasan Mom ɗita kike tsoro, kibar jin tsoro, yanzu zaman Dad kuke yi a cikin gida nan, kuma Dad shine mai iko a gidan nan ba Mom ba, kiman alƙawarin ba zaki kuma yin kuka ba saboda haka, nasan yanda kike ji a zuciyar ki, Amman kada ki manta ina nan, Dad ma yana nan"
Ya faɗa da ɗan murmushi cikin son kwantar mani da hankali.
Ban iya zame hannuwan nawa ba, na shiga ɗaga mashi kai alamar gamsuwa.
"A'a Muhammadu kai ne?" muka tsinkayi muryar umma daga bayan mu tana tahowa.
Da sauri ya zame hannuwan shi cikin nawa, yana mai ja baya yake faɗin "Eh Umma nine, ga kayan amfani cen ku fara kafin zuwa safe muga dame dame za'a buƙata, kuna iya yo list ma"
Ya faɗa kanshi a ƙasa cike da kunya, wai yau umman ce yake magana da ita a matsayin matar mahaifin shi, Un bleavable.
Ɗan murmushi ta saki tana mai cewa "To an gode kwarai Allah ya saka da alkhairi ya ƙara buɗi"
Da "Ameen" ya amsa yana mai juyawa ya fice ko ta kaina baibi ba, itama umma juyawa tayi ta nufi inda ya ajiye kayan ba tare data ce mani komai ba.
To nima ɗin da kallo na shiga bin umman tawa, yanda take komai kai tsaye, cikin ɗan ƙanƙanin lokaci umma tawa ta cenza kaman ba ita bace wadda na sani ada ba, me hakan ke nufi? Lallai akwai wani babban al'amari da yake a cikin zuciyar Umman tawa, babu shakka ko ɗar a cikin zuciyar ta?
Allah yasa koma me zai je ya dawo yazo mana da alkhairi Ameen.......
_Kuyi haƙuri da wannan a matuƙar gajiye nake wlh._
~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
*Page ~44~*
*Kyautar Page gareki One lurhv, ina jinjina maki a bisa soyayyar da kike mani Allah ubangiji ya bar ƙauna, ya tsole idanun maƙiya a kai, ya bamu ikon zama cike da so da amanar juna. AMEEN*
@Salamatu, Lubabatu, and Daura tnz for your personal Support, hearted u All guiz, ia ina yinku over and ove_
~_@Shalele (Raggon Miji Return) ki fita a idona in kulle fa tam, ni da One lurhv nan gani nan bari takalmin kaza, a tom_~
*Jinjina ga ƴan golden pen haƙiƙa haɗin kai da ƙaunar junan mu abu ne mai matuƙar ƙayatarwa, we are the best among the rest insha Allah, Allah ya bar mu tare*
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Sama sama muka yabiɗi abincin daga ni har umman tawa.
Ƙala bata ce mani ba, ina kula da ita sai bina da kallo takeyi.
Jikina har yanzu a matuƙar sanyaye yake, amman ita umma na kula ba ƙaramin ƙoƙari tayi ba wajen ƙarfafa tata zuciyar.
Kasa kwanciya nayi a ɗakina ni ɗaya ban saba ba. A hankali na tashi daga bisa makeken