Showing 63001 words to 66000 words out of 247770 words

Chapter 22 - BAN FI K'ARFINTA BA

10 Oct 2024

10461

shi da umma ta bata lafiya, da kuma a makaranta kwanaki kaɗan da suka wuce.

Ban aune ba na tsinkayo muryar shi daga cen gaba yana cewa " *kallon fa?*"

Ɗan duburcewa nayi, ina mai faɗa a zuciya ta cewa na shiga uku ni Hauwa'u, Ya ameen ya kama ni dumu dumu ina kallon shi, Sam bansan idanuna na kan madubi ba, ban
Kuma kawo ma raina cewa zai iya hango ni ba ta baya, da yake motar na da ɗan duhu haka.

Tsaf ya tsare ni da idanu ta cikin madubi yana ɗan cije bakin shi da haƙoran shi kaɗannkaɗan.

Hafsat ce da hankalin ta ya kai kanmu, kuma taji abinda ya tambaya, ɗan juyowa tayi kaɗan tana waywaye na, hakan ce ta sanya ni ɗauke kaina na maida idanuwa na kan glass ɗin da yake gefe na, gami da ƙure titi da idanu, ba tare da ko alamun bayar da amsa ba.

*indai kunya ce, tau nidai yau na riga na shata ni Suhan*


_Share_
_like_
_Comment_


~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/


🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺


*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._

*Page~23~*

*Page ɗinki ne maman sadeeq, kiyi yanda kike so dashi, asha karatu lfy*

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

Fuska ta a ɗaure, ko da muka haɗa idanu da hafsat, harara na sakar mata, ita kau juyawa tayi tana ƙunshe dariya a ciki, harda rufe baki, saboda ta fahimci Abunda duk ya faru.

Har yayi parking ƙofar katafaren supermarket ɗin ban ƙara yadda mun haɗa idanu dashi ba, ina ƙoƙarin sauka ne idanun A suka kai kanshi ta madubi, ya ƙureni da kallo ko motsi baya yi, hannun shi duka akan stiyarin motar ya jingina jikin shi da marfin motar ta ɓangaren shi, yayi kyau kaman saraki, saurin ficewa nayi har ina harɗewa da zumbulelen hijab ɗina Allah ma yaso ban kifa ba.

Lumshe idanu yayi, ya sake buɗewa lokacin da yaji duk sun fice hafsat na jero mashi godiya, da kallo ya raka su, a zahiri gaskiya ba ita yake kallo ba, tinanin abinda maree tayi mashi kawai yake yi, ita kau mutuniyar tawa sai ta ɗauka still ita yake kallo.

Jan motar yayi a matuƙar fusace ya bar wajen, dole ne ya ɗauki mataki, ba zai lamunci ƙaramin iskanci a cikin gidan nasu ba.

Mun sha soyayya, abinda ke bani mamaki yanda hafsat ta ragargazo mani siyayya sosai da sosai, kayan fitar biki ne masu tsada ta siya man, harda kayan Fulani da za'a sanya ranar tradutional day da za'a gudanar a lambun gidan nasu.

Kwanan mu biyar muna fita siyayya, har ɗinkunan mu duk mun amso, saboda kuɗin shap-Shap Hafsat ɗin ta biya aka yi mana.

Gyaran jiki Hafsat ɗin ta tursasani saida na biye mata aka yi tayi mana tare, wanda a zahirin gaskiya ma gyaran jikin yafi karɓa ta tinda na fita haske sosai.

Ban sake jin ɗuriyar Ya Ameen ba, haka suma mutanen cikin gida bama jin ɗuriyar su, hidimar biki ta sanya su gaba, ko ta kanmu ma basa bi.

Tini gida ya ɗauki harama, dukkan kayan dake cikin gidan nan saida aka fidda shi aka cenza wasu, hatta fentin gidan baki ɗaya saida aka cenza.

Kullum da kalar baƙin da za'ayi a cikin gidan, muma ta ɓangaren mu ba baya ba, muna shirya daidai ƙarfin mu.

Gida ya fara tara jama'a, wanda hatta mutanen kankiya sun iso, da family ɗin Alhaji awwalun, da aka buɗe ma babban sashe guda, dole hafsat ta tattara ta koma sashen da aka basu, inda aka mallaka mata babban ɗaki guda ɗaya da komai da komai a ciki.

Ba yanda bata yi ba don inzo muje tare nace aa, umma ta ma da ta tambaya cewa tayi a'a, indai tana buƙatar wani abu daga safiya zuwa dare tazo ina nan Amman banda kwana,dole ta haƙura ba don taso ba, muka cigaba dayin shirye shirye yanda ya kamata, daga safiya har dare kaman yanda umman tawa ta faɗa muna tare, domin nice na zame mata babbar ƙawa kaman yanda ta faɗa.

Su kau sauran amaren ma ba ganin su mukeyi ba, suna sashen da aka buɗe masu su da ƙawayen su kawai, Shiyasa in ficewa zasu yi har sun fita ta ƙaramar ƙofa ma babu wanda ya gansu.to dama dai mu bamu damu da al'amarin su ba, babu abinda zai haɗa sai tradutional day da Hafsat ɗin tace shi kaɗai zata yi.

Hajiya Kubra tare da manyan aminan ta da ƙawayenta sai shige da afice akeyi, bikin fa na manya ne, mata kake gani manya jugunannu daga kowanne ɓangare suna fitowa, zo Kaga ruwan ƙaryar gudunmuwa, har saida ta wakilta ƙawata Hajiya Laila ta dinga karɓa domin ita ta gaji da hayaniya.

Ana saura kwana bakwai biki su Aunty Feena da Afnan suka iso, karkaso kaga murna, ba ma kaman yanda suka tadda gidan ya cika da ta kowanne fanni ƴan uwa da abokan arziƙi, dangin Hajiya lailan ma sun iso suna babban sashen ta aka sauke su, yo ai su nata ne ko, su kuwa ƴan kankiya ɓangaren kusa da na Hajiya zainab maman Hafsat aka basu, to dama dai sun fi shiri da jituwa da ita, saboda tafi Kubra sauƙi da girmama dangin mazajen nasu.

Afnan ce ta rungume ni ta baya, tana "oyoyo Aunty na, wow kinga yanda kika yi kyau kika haska kuwa? Allah kaman ba ke ba, minene Sirrin?" ta faɗa tana kashe man ido ɗaya.

Murmushi nayi na sanya hannu na jawo ta gabana, "Afnan yaushe zaki bar ce an auntyn nan? So kike a jiki ki jaman?" na ƙara she alamar tambaya.

Murmushi tayi, sannan ta buɗe baki da niyyar magana, dakatar da ita nayi ina mai cewa "to yanzu dai ya hanya? Ya shirye shiryen biki?"

"Shirye shirye ai sai ku, ko aunty Hafsat?" ta maida tambayar tata akan hafsat, bata jira cewar hafsat ɗin a ta zauna tana mai cewa "tau yanzu dai minene shirin ku? Ya ban ganku a sashen amare ba ku?

Shiru muka yi mata ni da hafsat ɗin, ɗan nazarinmu tayi na tsawon second biyu, sannan ta ɗaga hannu alamar dakata-dakata

" Bama wannan ba, gara da kukayi zaman ku nan ɗakin umma ta, (Tana nufin umman suhan) ku ƙyale su cen da ƙawayensu ƴan fafa, mu cigaba da hidimarmu anan kawai mu share su".

Dukkanmu murmushi muka yi, umma ta dai tana gefe zaune, ƙala bata ce mana ba, da yake mun samu sauƙi tsangwama yanzu hidimar biki tasha kan kowa, sai ba'a damu da shigar afnan ɗin cikin mu ba mu kayi ta shirye shiryenmu daidai gwargwado.

Afnan ɗin fa ta shige cikin mu, kaman ma ba ƴar gidan ba, ko wajen yayyen nata bata zuwa, komai mun kammala, hatta da kayan da amarya zata sanya tsawon kwana biyar da za' a fara hidimar bikin zuwa bayan kai ta gidan mijin nata, muma haka ta taya mu muka shirya su mu duka muka adana abunmu.

Yau ne za'a kawo lefe, hakan ce ta sanya muka shirya zuwa wurin ƙunshi a yau, tau suma ɗin sauran amaren dai duk yau za'ayi masu, Amman su har gida za'a zo ayi masu, saboda a gobe ne za'a fara program ɗinsu tinda mu tradutional day ne kawai, saura kwana biyu biki ne za'ayi shi shi.

Afnan ce ta jamu zuwa wani shago inda aka ƙware da zanen lalle, ɓaki da ja, aka yi ma amarya, masha Allah, gaskiya yayi kyau sai ɗaukar idanu yake, duk da hafsat ɗin ba fara bace, Amman kunsan amarya yanda take, kuma ƙunshi yayi daidai da kalar fatar jikin ta, sai aka yi ma afnan, ita fara ce tas, su tace baƙi take so duka, haka aka yi mata, masha Allah kaman ka sace ƙafar da hannuwan nan.

Nice ƙarshe, hakan ce ta sanya nace ni ja nake so duka, ɗan kaɗan, cikin hannuwa da yatsu sai tafin ƙafa ya ɗan hau kaɗan, haka aka yi man shi, sunce yayi kyau sosai, nima na san yayi kyau ɗin, dama ba don wani nayi ba don kaina nayi.

Haka muka dawo da yamma lis, mun tadda an kawo lefe, a bakin umma ta muka ji, wanka muka yi muka sake kaya sai ɓangaren maman Hafsat, mun gaishe ta da duk wanda ke sashen, da yake sashen ba hayaniya, bikin da za'ayi ba a gidan ta ba, Shiyasa batayo gayya ba sosai, duk da itama ƴaƴa biyu zata auras da Hafsat ɗin da yayan ta.

Sashen su kaka zuwaira muka shiga, abun ka da wasu daga ƙauye suka zo, an fa yi ma sashen diƙi diƙi, abun ka da farin tiles da fenti sai dattin ya fito fili, tin kaka zuwa Iran na magana har ta haƙura ta gaji, shima saida Giggo Aisha, yayar su Alhaji mustaphan tayi mata magana, tace ta ƙyale su don Allah duka kwana nawa za'ayi kowa ya tattara ya koma?

Jawo Hafsat ɗin kaka zuwaira tayi, tana mai cewa "Zonan ja'ira, ina kika samo miji malaniya haka? (Wai millioneire take sabon cewa🤣), kin kau ga kayan da aka kawo maki? Akwati ashirin da huɗu? Ko su iyayen kankambar ba'a kawo masu haka ba, sunkuyar da kai hafsat ɗin tayi tana mai ɗan murmushi, Giggo Fatima ce ta ce "Haba Hajiya, ya isa hakanan ki ƙyale ta, kowa ba da goshin shi yake zuwa ba?"

Duk da haka saida ta danƙwashe kanta tana ƙara zaulayar ta, ita kuwa da taga haka sai ta sulale ta kwanta bisa cinyar tsohuwar tana mai cewa bari inyi hawan ƙarshe 🤭

Dukansu dariya suka sanya suna cewa ta ɗaga masu tsohuwa kar ta karya masu ita, da yake amarya farin jini gareta, sai kowa ya dawo nan aka yi ta fira da ita, to ko babu komai ai hakan yafi, dama su saran sarakan basu ko leƙa sashen ba tin bayan da suka je suka gaida su ranar da suka zo, saɓaninnhafsat ɗin da kullum sai taje, ko in raka ta ko ta tafi ita kaɗai.

Nayi nisa cikin gyaran sashen da ya kusa komawa kwalta tsabar datti, cen an zubda tea, cen abinci, cen an jiƙa bredi an zubda, gida ne ba wanda ƙuda ya saba zama ba, Amman zuwan ƴan kankiya saida sashen ya koma matattarar zaman ƙudan, duk da wasu na kiyaye wa, Amman wasu kau sai a hankali, yo an kwaso ƴaƴa an taho dasu cin duniya 🤣

Saida na gyara ko ina tsaf, harda falon da suke zaune saida suka ɗaga na gyara, sannan muka bar sashen zuwa namu domin magariba ta kawo jiki.

Goggo Aisha ce ta kalli Goggo Fatima tana cewa "wai ni kau Fatima, wannan ba yarinya nan bace da Muhammadu na wajen Mustapha yace yana so ba?" "ita ce kuwa, nima da farko ban gane ta b, sai da uwar tata ta shigo gaidamu ne sannan na gane ta, ai kinsan ita ce ta rako ta" kaka zuwaira da take zaune gefen su bata sanya masu baki ba, sai yanzu ta tanka tana mai cewa "haba, ni kau da har zan tambaya ina Hafsatu ta samo wannan yarinya haka mai natsuwa da son aiki, yarinya tana da tarbiyya wallahi, ku duba duk lokacin da tazo sashen nan sai tayi mana aiki, ko gazawa batayi"

Goggo Aisha ce ta shiga jinjina kai alamar gaskiya ne zancen mahaifiya tasu sannan ta shiga cewa "aiko in haka ne, ni banga abun ƙi ba a tattare da yarinyar, yarinya kyakkyawa da ita masha Allah, ga hankali da natsuwa, ai irin ta ce kowa ke burin samu a matsayi suruka, in banda hauka irin na kubura" "kema kinnfaɗa Yaya, Allah shi kyauta yasa ya ta gane gaskiya"

Ameen kowa ya amsa. nan suka bar zancen suka kama wata tashar kuma, yayin da cikin zuciyar hajiya zuwaira ta yaba da natsuwar Suhan ɗin sannan ta ƙhdurce abubuwa da dama akan lamarin.

Washegari da wuri muka farka, domin yau ne ƙawayen Hafsat ɗin zasu fara zuwa, duk da ba wani event zata yi ba, Amman sunyi mata kara sosai sun zo da yawa kuwa. Bamu san wanene ya tsegunta zaman hafsat ɗin sashen su ba, ba cikin amaren ba, sai ga mama Talatu an aiko ta, cewa Hafsat ta koma sashen da aka ware ma amaren, ita da gayyar ta, ba don son ranta ba ta tattara ta koma cen, aka ware mata ɗaki ɗaya babba dazai isheta har zuwa ɗaurin auren nata.

Komawa sukayi ita da Afnan roƙon ummata akan ta barni in tafi tare dasu, da farko ta hana, sai kuma ta barni tare da shara ɗin duk Abunda za'ayi mani kar in kula, in yi haƙuri in share, da haka muka ɗunguma zuwa sashen amaren Amman a ɗakin u nake komawa inyi wanka in shirya.

Umma ta ta kan leƙa sashen Mama zainab ɗin, kama mata wasu ƴan ayyukan, da haka har suka saba, in ma bata ga tazo ba ta kan aika a kira ta.

Mun shiga cikin hidimar bikin dumu dumu Dukkanmu, albarkacin Hafsat da mahaifiyar ta, Abunda banyi zaton umman tawa zata lamunta ba, sai gashi ita dakanta ke ƙara gaya man irin halin kirki da karamci irin ma Hajiya zainab ɗin, da gani dai Hafsat ɗin ita ta biyo.

Abunda na kula dashi shine, duk lokacin da zan gifta ko zan wuce ta falon shine shewa da ƴar guɗa da ake Sanyawa haka ana zunɗe na sai kuma ayi tafi a kashe, manyan yara ne masu ji da kansu, ban ma yi tinanin zasu tsaya kula ko zunɗena ba, tinda Nidai bansan me suke mawa ba, bansan me na aikata masu ba da har suke yi man haka. Share su nake yi kaman yanda umman tawa ta umurceni.

"Hahaha, Wannan? Yo me haɗaɗɗen saurayi kaman wannan zai ci da wannan? Haba Nihla, kisan me kike faɗa mana, dubeta fa, kaman alhaja, har koɗa take yi, ni anya ma ba sadaukar yalla bace, irin waɗannan masu muna bara muna karuwanci bace? Ni wallahi na tsani yarinyar bansan dalilin da ya sanya Dad ya sanya suka dawo nan ba, kishin ta nake ji sosai har cikin raina, bansan dalilin shi na son auren ta ba, bayan gani."

Ɗaya daga cikin ƙawayen su Saudat ɗince ke cewa haka, ban ko kalli inda suke ba nayi saurin wucewa, fatana dai ace ba dani suke ba, yo me ma zai sa inyi tinanin dani suke? Bayan banji sun kama suna ba, kuma ni na san babu wanda yace zai aure ni balle har wata tayi kishina a banza.

Share zancen nayi, ina mai shige wa ɗakin amaren da suke ta shirye shiryen zuwa bridal shiwer ɗin da aka shirya za'a gabatar a yau, duk da ita amaryar tasu tana kwance, tace ba da ita ba, bai hana su cewa wallahi sai sun je ba sun kashe ƙwarƙwatar idanun su.

Harda Afnan aka shirya sunyi shiga ta jar riga da straigh skirt Black, sai hula itama baƙa an ɗaura wani abu mai kyalkyali a hannu shima ja, sunyi kyau ba laifi, Amman a haka wai ƴaƴan musulmai zasu fita, Allah shi kyauta.

Motoci aka kawo aka shiga ɗaukar amaren, dama even ne na mata, wani ƙerarren gida dake ta bayan Layin su aka shirya ma abun, shima ya sha decoration Red and Black, sai amaren da sukayi complet White, ba ƙaramin daɗi suka ji ba da hafsat tace bata yin even ɗin, dama wai suna gudun a cika masu wuri da ƴan ƙauye, Shiyasa suka bata getpass guda biyar kacal.

To ita cewa ma tayi bata zuwa, sai ƙawayenta ne su huɗu suka shirya aka tafi tare dasu, suka saje cikin ƙawayen amaren, saura getpass guda kuwa ajiye shi aka yi baya da wani amfani, gidan fa yayi tsit, duk masu rawar kan an da ƴan ƙaryar na sun kwashe sun tafi, sai Naji dama gidan ya cigaba da zama a haka

Ohh🤔🤔 su suhan da ƙarfin hali ake.


Washegari sukayi arebian night, hall aka kama mai kyau da tsada, acen aka gabatar da shirin, wannan haɗe yake maza da mata, sunyi yadda suke so, da yake ba ya ameen babu mai kwatsa masu, abie ƙanen su ne y bai isa yace gyadda za'ayi ba duk da Aunt Feena na wajen, to itama bata ce ga yadda za'ayi ba, tinda Rayuwar turawa ta shiga kansu da yawa.

Mothers eve, aka shirya washegari, zo Kaga yadda aka ƙawata gidan da yake a haraba gidan za'ayi, anyi ɓarin kuɗi kaman da gayya, makaɗa da mawaƙa sun sha daloli, dole ne asan da bikin ƴaƴan Hajiya kubra Dambulan akeyi, rawa dai da juyi sunyi shi, manyan mata ko kunya basa ji haka suke juyi suna watsi da kuɗi, babu Abunda kake hangowa illa, gwala-gwalai, da ɗanyun lesussuka malam, masu video coverage nayi, masu hotuna nayi.

Duk abun nan da akeyi Ya ameen ɗin na tsaye ta window ɗin falon nashi yana hango su, hannuwan shi duka soke cikin aljihu wandon bugaggiyar shadda tashi, fuskar nan tashi murtuk, bai san me ke damun mahaifiyar tashi ba, bidi'a da alfahari kawai ne acikin ranta, in banda haka duk wannan watsi da kuɗin da akeyi duk na menene? Wa za'a burge? Wa ke bai san suna da kuɗin ba? To indai haka ne shi a ganin shi wannan almubazzaranci ne.

Makullan motar shi ya zara gami da ficewa ta ƙofar baya, jin kiɗan dake tashi a cikin gidan zai fasa mashi dodon kunne duk kuwa da girma da faɗin gidan.


Zaune nake kunnuwa na toshe da headphone, ƙira'ar Sheik abdurrahman sudais ce nake saurare. Ina jin daɗin muryar bawan Allahn, a hankali nake bi shi cikin suratul baƙara, nayi nisa cikin bin shi karatun, ɓangaren ɗaya kuma tinani ne barkatai cikin ƙwaƙwalwar ta, a hankali Naji wani abu na bimanta cikin ƙafa, saurara wa nayi, lallai wani abu ne ki bi man jiki dagudu, a zabure na tashi ina kwalla ƙara gami da fara dire

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login