Showing 114001 words to 117000 words out of 247770 words
yayi ya miƙe daga tagumin da yayi, baisan ya fara kai komo ba, yana mai cewa "Comon pick it Suhan please"
Itama ummin a zabure ta miƙe tana mai cewa "Ta shiga ne? Ta ɗaga ne?". Bai ko kula ta ba, ya cigaba da zagaye tanƙamemen falon, bata ɗauka ba, hakan ne ya sanya shi dunƙule hannu ya naushi iska dashi, gami da guntsar iska ya fesar, sake kira yayi Amman ta shiga ba'a ɗauka ba.
Da hanzari ya fice daga falon, mota ya nufa da niyyar barin gidan, zuwa zai yi ya kai number ɗin ayi mashi tracking ɗinta, koma ina Suhan ɗin take yau ce ranar da zata bayyana, baya jin idan zai iya yafe ma duk wanda yayi sanadiyyar barin su gidan gabaki ɗaya a rayuwa.
Ko ta kan ummi baibi ba, ya danna ma mai gadi horn, da gudu yazo ya buɗe mashi gate, ya ja motar a fusace yabar gidan, daidai ƙarasowar ummin da gudu tana ɗaga mashi hannu.
"Wash" tace tana mai kai hannuwan ta bisa guiwoyinta kaman zata yi ruku'u, saboda tayi gudu ta gaji, daga falon zuwa harabar gidan da ƴar tazara, hakan ce ta sanya ta gajiya, ga kuma laulayi da take fama dashi.
*Adai yi mani uziri, a kuma bini da Addu'a please*
~Oum-Deedat ce~
[10/1, 8:25 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
*YAN UWA MUNA KARA KIRA DA MABIYA LITTAFAN GOLDEN PEN WRITTERS ASSOCIATION DA SU KIYAYE DA WANNAN MAI CUTAR TASU DA SUNAN YANA SAIDA LITTAFAN KUNGIYARMU,TO KARYA YAKE MACUCI NE KAWAI LITTAFANMU IS FREE 1 NE KAWAI NA KUDI,KUMA DA YACE YANA BA KUNGIYARMU KUDIN REGISTER DIN DA KUKE BIYA DOMIN MU TURA MASHI SABBIN LITTAFAN MU,TO WALLAHI DUK KARYA YAKE MANA MU BAMU DA MASANIYA AKAN WANNAN B'ARNAR DA YAKE MANA SAI DAGA BAYA MUKA JI,SANNAN KUMA INA SON KUSAN NUMBER DIN SHI SABODA YANA NAN YANA SHIGA GROUPS NA MATA DA SUNAN MACE SABODA HAKA KU KIYAYE GA NUMBER DIN SHI NAN (08107707692)*
*Page ~35~*
*_Happy Indipendance Day To All Nigerias, Allah ya ƙara mana zaman lafiya kwanciyar hankali da wadata, yaba shuwagabanninmu ikon yi mana aiki da adalci bisa gaskiya. AMEEN_*
~Gaisuwa ga Lubabatu Funtua shima wannan Page ɗin naki ne, nagode da kulawa da ƙauna baki ɗaya~
*Aishatu Babayo Jos Mrs: Abubakar Yakubu (Ɗanjuma Master) ƴan golden pen suna yinki, ba zamu iya fasalta ƙaunar mu a kanki ba, saidai muce Allah ya bar mana ke, kiyi ta suburbuɗa mana comment Ameen*
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Munyi nisa a tafiyar tamu da mukeyi zuwa makarantar, saidai ba wanda ke ceman wani ƙala cikin ni dashi,tin bayan gaida shi da nayi, lokacin da na shiga motar. Jefi jefi ya kan ɗan juyo ya saci kallo na haka, ni kuma sai in kauda kaina, tunani na yayi zurfi sosai, abubuwa da yawa nake saƙawa cikin raina, lokaci guda tunanin in sanya waya ta cikin caji a motar ganin cazar da nayi ya faɗo a raina.
Jikkata na jawo gami da ɗauko wayar, a hankali na jona ta a cikin chajin,kaman jira take yi kuwa ta ɗauka, kunna ta nayi, lokacin da na kula ta kai kusan 5% na ajiye ta kusa dani.
Har yanzu dai bai ce man uffan ba, tuƙin shi kawai yake yi, ganin hakan da nayi ne ya sanya ni janyo hijab ɗita na rufe kusan rabin fuska ta,gami da jingina kaina jikin ƙofar motar ina mai lumshe idanu, sanyin Ac na ratsa ni, haɗi da ƙamshin freshner ɗin dake cikin motar sun haɗu sun cakuɗe da ƙamshin turaren mutumen da ya kira kanshi da suna *Salim Bawa*
Ban aune ba naji muryar shi kwatsam yana cewa "Maman ki ta burgeni matuƙa, haka nake son mace mai jajircewa akan ƴaƴanta, nima haka Ammi na take"
Ɗan ɗagowa nayi a hankali, ina mai kai idanuna bisa ƴar kyakkyawar fuskar shi, sannan nace "Nagode" a hankali.
Ɗan murmushi ya sake yi, sannan ya cigaba da cewa "ya kamata ki sake sanin ko ni wanene ko? Gudun kada in sace ki a rasa inda kike, gashi ba'a haɗo mu da kowa ba"
Dam gabana ya faɗi, sake kai dubana nayi gareshi, ɗan murmushi na hanga saman fuskar shi, ga alama ma bai wani damu da abunda ya faɗa ɗin ba.
Gyaɗa mashi kai kawai nayi ba tare da na samu zarafin ce mashi wani abu ba.
Ganin hakan da yayi shima ya sanya shi sake sakin murmushi mai sauti.
"Kaman yanda na faɗa maki gaskiya sunana *Salim Bawa Bala* mahaifi na shine Alhaji Bawa Bala idan zaki iya sanin sunan?"
Ya faɗa da alamar tambaya a kan fuskar shi.
Nan ma ɗan sake girgiza mashi kai nayi, duk da har yanzu ban ɗago ba, saidai na tattara dukkanin natsuwa ta akan shi.
Jinjina kai yayi yana mai sakin murmushi da na kula hakan Al'adar shi ce, sannan ya ɗora da faɗin.
"Ni ne ɗa ɗaya tilo a wurin Alhaji Bawa Bala, da Hajiya Khaltum Bawa Bala, duk kuwa da cewa mu biyu suka haifa ni da ƙanwata Asiya da taci sunan Kakata wadda ta haifi Babana Alhaji Bawa Bala, Shiyasa muke kiranta da Suna Imtihal ko kuma mu ce Imti. Ni haifaffen garin Adamawa ne a ƙaramar hukumar Yola, ni bafulatani ne Usul, duk kuwa da kasancewa ta baƙi. A gaskiya zan faɗa maki ina da aure harda yara biyu. Aisha Sholy da Usman muna ce mashi usi. Munyi auren soyayya da matata kaman me, iyaye na kowa na ƙaunar ta, saidai kasancewar faruwar wasu abubuwa ya sanya yanzu nake searching ina so in ƙara, saboda haka ina barar ko da acikin ƙawayen ki ne masu hali da natsuwa irin taki, a taimaka mani"
Duk wannan maganar da yake yi, idanuna ƙur a bisa titi, dukkanin garuruwn da muke wucewa hankali na yana a kansu, saidai kuma kaf ina sauraren shi da kunnuwan basira.
Ƴar ƙaramar ajiyar zuciya na sauke, ina mai cewa "Allah sarki, nikam bani da ƙawaye, ka gaida man da yaran idan kaje gida da maman su"
"Zasuji"
Ya faɗa a gajarce cikin wani murmushin
Ya buɗe baki kenan da niyyar sake cewa wani abu, sai kuma wayata ta ɗauki ƙara alamun kira ne ya shigo. Nima ƴar firgita nayi, ina mai sake waro idanu waje, lokaci ɗaya na yunƙura gami da wawuro wayar.
Sunan *Yaya Bilal* na gani ɓaro ɓaro a bisa fuskar wayar yana yawo.
Ba zan iya cewa ga halin da na tsinci kaina ciki ba, saidai a zahirin gaskiya na shiga matuƙar halin damuwa da firgita, ina cikin wannan halin ne har ta katse, wani kiran ya sake shigowa a lokaci ɗaya.
Nan ma ban iya amsawa ba, har ta kuma katsewa, ai kafin wani kiran ya shigo nayi saurin kashe wayar gabaki ɗaya ma, gami da zare chajin na warware wayar gami da zaro sim ɗin sannan na maida batirin gami da sake jona ta cikin caji.
Sim ɗin yana riƙe a hannu na, shawarar in jefar dashi nakeyi, ko kuma na adana, saboda kaman yanda ummata ta nuna mani a zahirin gaskiya bata so su san inda nake, ko kuma wata alaƙa ta kuma shiga tsakani na dasu.
Shiru ne ya biyo baya cikin motar, babu abinda kake ji sai ƴar ƙarar Ac da kuma saukar numfashin mu. Duk da yana lura da abunda ya faru amman baiyi yunƙurin tambaya ba, domin yana ganin ba hurumin shi bane, ko kuma lokaci bai yi ba tukunna da zai kutsa kai a al'amarin yarinyar daga haɗuwa da ita.
Daidai bakin gate ɗin makarantar yayi parking gami da ficewa ba tare da ya kashe motar ba, ba daɗewa ya dawo cikin motar hannun shi riƙe da layin Sim na Glo, miƙo mani yayi ba tare da ya kuma cewa komai ba.
A sanyaye na amsa gami da yi mashi godiya a hankali, lokaci guda na kuma zare chajin da har ya riga ya cika, sanya sim ɗin nayi da na kula yana da rigister already.
Har cikin makarantar da department ɗin namu muka isa, shi ya shige mani gaba wajen cuku cukun komai, sai naga ashe ma HOD ɗin namu abokin sh ne sosai da sosai, ina zaune gefe ba wahalar komai aka kammala komai.
Umurtata yayi da na bishi ya nuna mani hall ɗin da zamu rinƙa amsar lectures. Ko bayan dana fito daga office ɗin sai da ya tsaya suka sake wata magana da bazan iya cewa ga abunda suka tattauna na ba, sannan ya fito na bishi a baya har zuwa lecture hall ɗin namu da muka tarad da wani malami a ciki yana ba sauran ɗalibai lecturers, duk da na kula ɗalibai basu da yawa sosai, haka nayi sallama na shiga na zauna a kujerar da take gefe babu kowa a bisa ita. Shi kuma a daidai lokacin ya juya ya koma haɗi da yiman inkiyar yana jira na.
Da idanu na bishi, lallai mutumen ta taka muhimmiyar rawa a rayuwar karatun nawa, mutum ne shi mai zafin nama da yawan barkwanci a yadda na kula, sannan ɗalibai da dama sun sanshi duba da yadda naga ana ta gaishe shi bisa hanya sannan ana bina da kallo ganin ina binshi zarai-zarai a baya duk inda yayi.
Hankali na na maida bisa kan lecturer ɗin namu dana lura sosai cewa ya iya koyarwa sosai, cikin salon turancin shi da yake fita sala-sala.
Wata ajiyar zuciya na sauke, cikin son kauda tinanin komai a raina, zuciya ta fal da zumuɗi da farin ciki yau ni Suhan ce zaune a ɗakin ɗaukar karatu ina gaban malami yana koyar dani.
*Ya Allah ka bani ikon cinye wannan jarabawar ta rayuwa, ka sanya hakan ya zamo mafi alkhairi a rayuwa ta, Ya Allah ka dubeni da idon rahma ka bani abinda nazo nema, ka bani ikon jure dukkan wani ƙalubale na rayuwa daka iya kutso kai a cikin rayuwar karatun nawa anan gaba*
A haka muka cigaba da ɗaukar lectures kusan yinin ranar, ban kuma neman Sir, Salim ba kaman yanda Naji student na kiran shi.
Daga Hostel ɗinmu zuwa lectures Hall da ɗan tazara ba sosai ba, hakan ce ta sanya na saki niƙab a hankali nake taka wa zuwa Hostel ɗin bayan mun gama dukkan darussan ranar.
Waya ta ce ta ɗauki ƙara, da mamaki nake kallon fuskar wayar, ganin baƙuwar number, gashi dai na san yau na sanya layin babu wanda ya sanni da number ɗin.
Ɗagawa nayi cikin siririyar sallama a bakina, daga cen ɓangaren Naji ance "Assalamu Alaikum. Idan kin gama kada ki wuce gani ta nan bayanki ina jiran ki" ɗaga wayar nayi a kunne na, gami da juyawa, ko ba'a faɗa ba na gane mai magana Sir Salim ne, shi komai nashi cikin zaulaya yake yin shi.
Ɗan juyawa nayi a hankali, cen bisa bayan boot ɗin motar shi na hango shi zaune, kallon second biyar nayi mashi, har na ɗaga ƙafa da niyyar komawa ta inda yake, sai kuma naja na tsaya. Shima ganin hakan ne ya sanya yayi ɗan murmushi gami da dirkowa ya tako cikin tafiyar shi mai sauri ya iso inda nake tsaye kaman an kafe ni.
Da murmushi ya ƙara so yana faɗin "Ya da haka kuma? Shikenan da ban ganki ba sai kuma gobe?"
Ɗan girgiza kai nayi, sannan nace "A'a dama zan kira ka ne in na shiga ɗaki" daga haka ban sake cewa komai ba.
"To ai shikenan, zan iya yin rakiya cen bakin hanya?" ya sake jefo mani tambaya cikin wani salon zaulayar
Ɗan murmushi na saki ina mai jinjina mashi kai, sannan na juya muka fara tafiya, duk da akwai ƴar tazara tsakanin mu, kuma ba mai cema kowa ƙala, illa dai ɗan kallo na da yake yi akai akai, wannan ce ta sanya duk na takura, tinda hasali ni ba sabawa nayi da hakan ba.
Har hanyar da zata sada ni da ɗakin mu ya raka ni, sannan yayi mani sallama ya juya yana faɗin zai kirani anjima idan na huta.
Naji daɗi, ko ba komai dai na samu mai shige mani gaba, na samu mai tsaya mani da kula da dukkanin motsi na, wanda in nayi ba daidai ba zai iya cewa in bari.
Da haka har na ƙara sa ɗakin da yake mallakin mu mu uku, ga dukkan alamu ma dai za'a iya ƙaro wata nan gaba mu zama mu huɗu. Waɗanda na tadda cikin ɗakin da gani dai basa da hayaniya, shiru shiru suke dan duk kansu karatu na tadda sunayi da litattafai a hannu, sallama nayi masu haɗo da yi masu sannu, sannan na hau shirya kaya na a ɓangare na, na gyara komai na kimlace. Sannan na shige banɗaki domin yin Alwala.
************************
Da matuƙar hanzarin shi ya isa ga tracking office ɗin, Allah Allah yake yi a kammala komai ya samu ya samo yarinyar nan tin kafin abokin nashi ya kuma tuburewa.
Saidai babban tashin hankalin da ya same shi, lokacin da aka sanar dashi an fidda layin a kan wayar, kusan faɗuwa yayi, saida ya dafe bangon dake kusa dashi.
A hankali ya jingina bayan shi da bangon, Ya Salam! Wannan wace irin rayuwa ce? Me hakan ke nufi? Menene dalilin su na aikata hakan? Da gangan sukayi kenan? Laifin ne suka aikata masu? Ina ita Umman take? Da hankalin ta zata ja yarinya su shiga uwa duniya inda basu da kowa?. "Huh" ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi jiki ba ƙwari yaja ƙafar shi ya bar wurin.
Koda ya shiga mota yafi minti sha biyar ya gaza tada motar, hankalin shi bai sake tashi ba, saida kiran Al'ameen ɗin ya shigo wayar tashi, kaman ba zai ɗaga ba, sai kuma yayi tunanin kada Al'ameen ɗin ya zargi wani abu kuma, tinda ya san halin shi, shegiyar ƙwalwa Allah ya bashi.
A haka ya ɗaga wayar, sukayi gaisuwa irin wadda suka saba da taɓa firar yanda abubuwa ke tafiya, har yake shaida mashi yaso zuwa Abba ya hana shi, shi ya rasa gane wannan dalilin hana shi ɗin. Kwantar mashi da hankali Bilal ɗin ya kuma yi tare da cewa yayi haƙuri har ya sake samun sauƙi.
Yau ma dai saida ya tambayi yanayin karatun Suhan ɗin da ummr, ce mashi yayi suna nan ƙlau kaman koda yaushe, umma kuma tana cikin ƙoshin lafiya.
Jin hakan da yayi ne, ya san aminin nashi ba zai yi wasa da amanar da ya bar mashi ba, ya sanya shi amincewa nan suka saki firar suka kama wata, sun kai kusan rabin awa suna magana mai muhimmanci sannan suka kashe wayar suna masu ƙaunar juna a ransu.
Bai ma jin zai iya zuwa office ɗin, don haka gida kawai ya wuce kai tsaye, koda ummin ta ganshi ba irin tambayar da bata yi mashi ba, amman yayi mata banza dole ta haƙura ta ƙyale shi.
Kwanciya yayi abun duniya duk ya ishe shi, yanzu haka rabon da ya ko leƙa gidan nasu Al'ameen tin bayan dawowar su ƙasar, to me zai je yayo? Alhaji Mustapha baya ƙasar, ba kowa sai masu aiki a cikin gidan, ko ita Hajiya Kubran ba zama take yi ba, kullum tana cen wajen harkokin ta arziƙi sai daɗa bunƙasa yake yi.
Su mama Talatu an samu Abunda akeso, ana saka ta a wala, tashin hankalin su ɗaya ita da maree da har yanzu Al'ameen ɗin yaƙi ya dawo ƙasar balle su san yanda zasuyi su shawo kan matsalar tasu na yadda zasuyi su karkato da hankalin shi, koda kuwa da ƙarfin asiri ne, wannan daular basa jin zasu iya barin ta ta tafi a ɓagas.
Tinda Hajiya Sa'a da Hajiya Laila suka tabbatas ma da Hajiya Kubran cewar, su umman fa sun tafi tafiya ta har abada ba waiwaye, sai hankalin ta ya sake kwanciya, kuɗi masu yawa ta narka masu wai tukuici, yanzu tana jin ta bata da matsala sai guda ɗaya, yayi yazo ya fidda matar daya dace ya aura kawai, ƴar manyan guda ƴar wani ƙusa a gwamnati ko ɗan kasuwa, ta yadda za'a dinga labari a ƙawaye cewa ita surukar wance ce a ƙasar ta nigeria.
Saudat basa ƙasar ita da mijin ta, Nihal ce kaɗai, itama kullum tana gida, ganin mijin ba zama yake yi ba, data dawo daga wurin aiki gida take wucewa ko gidajen ƙawayen ta, sai ta muka tasha iska sannan ta koma gidan. Hakan ce ta fara sanyawa ƴan ƙananan maganganu tashi a family ɗin mijin nata har maganar ta koma kunnen shi, duk da suke sangartattu ƴaƴan masu dashi, hakan baya mashi daɗi, ai auren ta yake yi, yana da haƙƙin duk inda zata je ta sanar mashi koda kuwa ba zai barta ba.
Sun fara samun saɓani akan hakan, inda ta nuna mashi Sam hakan fa ba mai yiwuwa bane, tana da ƴan cin da zata iya aiwatar da komai batare da ya sani ba, tinda auren ta yayi ba siyen ta ba.
A haka ya ƙyale ta yana mai ƙudurce ɗaukar mataki domin kuwa shi fa Sam ba zai iya lamunta ba, ko ba komai ai yana kallon matayen abokan shi ba haka suke yi ba, kullum suna gida ko wurin aiki