Showing 162001 words to 165000 words out of 247770 words
shi hakan ke bashi lasisin haɗa jiki dani a koda yaushe kenan?
Ban ankare da har yayi nisa ba, sai hango shi nayi cen nesa dani.
Yana ta ɗaukar abubuwan amfani cikin salon shi mai ban sha'awa
Haka na cigaba da bin shi, har yanzu bai ko juyo ya kalli inda nake ba.
Ba ra'ayi na ko zaɓi na yake bi ba, saidai na kula dukkan abubuwan da yake ɗauka masu matuƙar amfani ne.
Har ya gama ya cika keken taf, har wasu suna zubo wa.
Haka na sake bin shi har teburin accounter.
ATM card ɗinshi ya miƙa masu, zasu, zasu cura ta Pos
Sun matuƙar yi mashi discount, saboda Alfarmar dake gareshi a garin.
Sannan aka zuba mana su sit ɗin baya.
Har yanzu bai ko ceman ƙala ba, ya shiga motar.
An cika sit ɗin baya, ba damar jan magana. Hakan ce ta sanya ni buɗe sit ɗin gaban na zauna, nima ina mai basarwa tare da shassharewa.
Zama a kusa dashi ko a tare dashi, ba ƙaramin abu yake jaza man ba.
Kuma ni ba wai zan iya cewa ga abunda nake ji ba.
Haka muka shiga tafiya zuwa gidan babu mai kallon wani.
Saidai lokaci zuwa lokaci na kan muskuta in gyara zama, daga baya ma sai na jingina kaina jikin makarin kujera ina mai ɗan lumshe idanu.
Kaman ance in buɗe idanu na, idanun nashi na bisa fuskar tawa tar dasu, bai ji kunya ba, kaman yanda bai ɗaga idanun nashi ba.
Sai nice na janye fuska ta, ina mai maida ta bisa titi ganin yanda yake tafiya a hankali kaman wanda yaba so mu isa gidan da wuri.
Mai gadi yayi ma horn yaje ya buɗe mana, har muka sulala cikin gidan ba wanda ya tanka ma ɗan uwan shi.
Fitowa mukayi mu duka.
Ganin ya zagayo ta inda nake ne ya sanya nayi tunanin ko kayan zai fiddo mani ne.
Miƙo mani makullan motar naga yayi, sannan yace
"Idan kin gama kwashe kayan ki rufe mani motar, ki shirya da wuri da safe Dad yace in kaiki kamarantar da kaina. So kun katse mani ayyuka na, bana so kiyi keeping ɗina delay ok?"
Amsa nayi ina mai cewa "To yaya"
Sai kuma Kunyar abunda nayi mashi ta shiga kama ni.
Mutum ne mai ƙoƙarin kyautata ma duk wani wanda Allah ya haɗa shi zama dashi.
Da kallo na bishi, ganin ya juya ya nufi part ɗin Dad ɗin nashi, ya bar mani makullan motar a hannu na
Ya Ameen mutum ne mai matuƙar sauƙin hali.
Miskili ne, Amman yana jin haushn kiyi mashi miskilanci.
Da kallo na kuma raka shi.
Har gobe na rasa abunda zance yana burgeni tattare da Ya Ameen ɗin, saidai zan iya cewa shine mutumen guda da ko bacci nakeyi tunanin shi baya saki na.
Har ya shige part ɗin idanu na suna a kanshi, a hankali na saki ajiyar zuciya ina mai fara sauko da kayan zuwa ƙasa sannan na kulle motar.
Cikin part ɗin namu na nufa, sai kuma naja na tsaya ƙirjina yana dukan uku uku, ko a wanne hali zanje in tadda Umman tawa? Ko ya sukayi da Alhaji Mustapha da Hajiya Kubran?
A kasalance na ɗaga ƙafa na shiga takawa a hankali har zuwa cikin part ɗin namu......
_Kuyi manage, wannan ma squizing nayi na maku typing_
*Muna tare My Fans*
~Oum-Deedat ce~
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*
*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*
>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
*Page ~47~*
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
A falon na tadda Umman tawa zaune, kayan kallo a kunne suke, amman Sam hankalin ta baya kansu, har na ƙara sa inda take zaune na shiga ajiye kayan.
Bance mata komai ba, saida na juya na gama shigo da kayan, sannan na zauna kusa da ita ina mai kamo hannuwan ta nace
"Umma lafiya kuwa?"
Sai a lokacin ne ta ɗan firgita ta dawo hayyacin ta. "Lafiya ƙlau mamana, kun dawo?". Ta faɗa cikin son kauda wani zargin daga zuciya ta.
Ɗaga mata kai nayi, ina mai cewa "eh Umma, ga kayan da Ya Ameen ya siyo mani nan"
Ɗan kallon kayan tayi kaɗan, sai kuma tace "baki dai takura mashi ba ko?"
"a'a Umma, shine ma ya zaɓo da kanshi, wai waɗanda na zaɓa sunyi kaɗan"
To Mamana aikuwa an gode, je ki kaisu ɗaki kizo zamuyi magana dake.
Sai da gabana ya faɗi jin Abunda ta faɗa, hakanan na daure na miƙe, gami da kwasar kayan na nufi ɗaki.
Sai da na kwashe su duka, sannan na koma inda taje na zauna ƙasa ina mai cewa "gani Ummana"
"Taso ki hau kujera, banson kina zama ƙasa mamana, nan sashen Umman ki ne"
Haka ta faɗa cikin wani yanayi da na Gaza fahimta.
Sai da na miƙe na hau kujerar, sannan ta sake kallon a sosai tace "Mamana inaso ki bani aron hankalin ki sosai, akwai maganar da nakeso muyi dake, kinga dai dukkan abunda ya faru, ba sai na faɗa maki komai ba, zama a cikin gidan nan abu ne mai wahalar gaske, masalan ma gareki, da za'a dinga maki kallon agola, kiyi haƙuri da Abunda na faɗa, amman zaman ba zai iya cigaba a haka ba, Shiyasa nake so da ki faɗa ma Saleem yayi gaugawar turo da manyan shi, akan azo a tsaida lokacin biki, shima ba wani lokaci mai yawa za'a sanya ba, saidai kafin hakan dole ki toshe kunnen ki, zaki iya fuskantar matsaloli ta ko ina, maganar Muhammadu ki ajiye ta gefe, ban hana ki auren shi da wata manufa ba, na tabbata babu mahaifiyar da zata samu suruki kaman Muhammadu ta ƙi shi, to saidai abubuwan da zasu iya biyowa baya, da kuma irin matsaltsalun da zaki shiga bayan auren, wannan ne dalili na naƙin amincewa, mahaifiyar Saleem mutuniyar kirki ce, tasan darajar ɗan adam, zaki samu sauƙi zama da ita, shima kanshi Saleem mai ƙaunar ki ne, don haka kiyi biyayya, kibi umurni na, insha Allah zaki ci nasara a rayuwar ki. Ki tabbatar kin gama haɗa komai da wuri don Alhaji yace shi Muhammadn ne zai maida ki, amman ina so ki kula, babu komai tsakanin ku, in banda yana matsayin yayanki a yanzu. Kuma don Allah ina so dukkan Abunda zakuga anyi mana acikin gidan nan ki toshe kunne, ki kauda kai, insha Allahu komai mai wucewa ne"
Da idanu kawai nake binta, sai dai na rasa irin fassarr da zan yi ma maganganun nata, ban dai san me ke faruwa ba, illa iyaka dai na tsinci kaina da gangarowar hawaye a saman fuskan tawa.
Me kalaman Umma suke nufi, tabbas nasan Saleem shi nake so, shi ne muka shirya Rayuwar aure dashi, to saidai duk lokacin da ta furta ko ambata mani rabuwa da Ya Ameen na kan ji wani irin dafi ya soke ni a ƙahon zuciya ta, bansan dalilin hawayen ba, amman na ta'allaƙa abun da maganar aure, da rabuwa da ita ne data sako mani a yanzun.
Girgiza kai na fara yi, ina mai cewa "To Umma insha Allahu, zaki same ni mai biyayya gareki, kuma in Allah ya yarda ba zan baki kunya ba kaman yanda kika buƙata"
Ɗan murmushi tayi tana mai shago kaina kaman ƙaramar yarinya, ni kuma ganin hakan sai wani irin kuka yaso ya ƙwace mani. Zamewa nayi ina mai kwantar da kaina bisa cinya ta, share kwalla nake ta faman yi, Amman bana so ta gane, saidai na riga na makaro, tini ta fahimci hakan, saidai bata so wannan hawayen nawa ne ya ɗore har ƙarshen rayuwa ta.
Mun kusan kai ƙarfe sha biyu anan zaune, ƴan labaruka take bani masu daɗi, rabon da in samu sake wa da Umman tawa kaman haka, har na manta, ina so in tambayeta yanda sukayi da Hajiya Kubra, wata zuciyar na garbaɗi na, ai ba hurumi na bane, saboda haka naja bakina nayi gum abu ba, kada ƴar fara'r da na samu takeyi mani in kauda ta da kaina.
Sai lokacin ne ta miƙe tana mai cewa "Mamana je ki haɗa kayan ki, kinga da wuri zaku tafi, kada ku tafi kuma kina jin bacci.
Da haka muka miƙe ina yi mata sai da safe, kowa ya shige ɗakin shi, bayan ta kullo ƙofar shiga falon.
****************
" Wai ni kuwa kunsan Abunda ke faruwa ne a cikin gidan nan kuwa?"
Mama saude ta furta cikin tsabar mamaki.
Suna zaune su duka ma'aikatan a ɗakin mama talatun da bata lafiya duk sun shiga gaida ta, sai kuma aka buɗe sabon babin gulma.
Da mamaki suma sauran suka kalle ta
" Me ke faruwa ne?" Cewar Uwani da take zaune gefen katifar mama talatun
"Maryama mana, wallahi ina jin fa ita ce tayi auren cin amana, ita ce amaryar da Alhaji fa ya aura, wadda kuka ga anyi walima jiya"
Cikin tsanann mamaki, firgita da kaɗuwa su duka suke kallon ta.
Mama Talatu kuwa bata san lokacin da ta tashi zaune ba, tana mai wara idanu kan mama Sauden
"Ke Saude kice Allah kin tuba, wannan ma Hajiya babba ta jiki ai wallahi sai kin bar gidan nan, ba fa ita bace, matar da ba'a san inda take ba ma a halin da ake ciki? Na fa ganta, ita waccen wata mata ce mai kyau, jiya saida na sai jiki naje ganin kwam wallahi, gaskiya ba ita bace... "
Cewa Uwanin da har yanzu mamaki ne fal a fuskar tata.
" Ke Uwani wallahl azim ita ce, ai na ganta, kwalliya kawai akayi mata, kuma dama kinsan Maryama da kyaun ta, kawai wahala da babu ne yasa kika ga ta koma wata tsohuwa guda, yo Alla na tuba Suhan a ce fa kawai ɗiyar ta, ita kanta Suhanan dududu nawa take? Wallahi dai to ita ce, nima na daɗe ina mamakin yanda wannan al'amari ya juye haka"
"Ke Saude kin tabbata da Abunda kike faɗa?"
Cewar Mama Talatun da kamar ta sanya kuka take ji saboda tsabar baƙin ciki
"Wallahi kuwa shugaba, ai nima nayi mamaki, Amman muna nan daku zakuga Abunda zai biyo baya, ai Hajiya Babba ba kanwar lasa bace ba, hakan ma da dauke zaune wace Alla cika balle yanzu dataci amanar ta? Kuɗi zasuyi mata aiki yanzu don wallahi kunsan ba ƙyale ta zata yi ba sai ta hukunta ta"
Mama Talaun bata samu zarafin cewa komai ba, sai a komawa da tayi ta kwanta, jikin ta duk yayi sanyi, ashe hassada ga mai rabo taki ce? To ita yanzu da wane irin ido zata kalli Maryama a matsayin matar Alhaji? Bayan duk irin abubuwan da sukayi mata a baya?
Lallai sunyi wauta, sunyi kuskure, baka raina ɗan adam duk min yanda yake, sai gashi su Alhajin bai kalle su yace yana so ba, su da suke cikin gidan, sai ita da ta sanya ƙafa tabar gidan shine yaje ya nemo ta ya aura, lallai akwai dabi, zasu sanya idanu suga yanda Al'amurra zasu kaya, Amman ita kanta tabbas tasha Alwashin ba zata taɓa ajiye makaman yaƙin ta ba, sauƙin ta ma ɗaya da maree bata nan taje ƙauye ai da yanzu ta ɗaga mata hankali.
*********
Washe gari kuwa tinda na tashi sallar asuba, ban kuma komawa ba, saida na shirya komai nawa sannan nayo wanka, mai kawai na shafa ma fuska ta, sai kuma na koma na kwanta.
Misalin ƙarfe takwas na sake tashi, a gaggauce na wanko baki na, gami da zura kaya na, hijab na sanya har kusan ƙasa, babu kwalliyar komai a fuskar tawa.
Ina daga ɗaki na jiyo shigowar shi, suna gaisawa da Umma ta da take falo
Saida gabana ya yanke ya faɗi, jiyo muryar shi da nayi, sai Naji duk jikina yayi sanyi, bansan ko menene dalili ba.
A haka na jawo akwatn kayan nawa na fito.
Yana ɗan zaune bisa kujera, hango fitowa ta daga ɗakin ne ya sanya shi miƙewa yana mai nufi ni da niyyar amsar akwatin daga hannu na.
Ja nayi na tsaya, ya masifar yiman kyau, fuskar nan tashi tar kaman wata ɗan daren sha huɗu, da mayatattun idanun shi, masu kama da yana jin bacci yake kallo na, ɗan bakin nan gum dashi kaman an ɗisa mashi, sai dogon hancin da ya ƙara ƙawata fuskar.
Ƙananan kaya ne jikin shi, baƙar riga sosai mai rubutun C-Blue a jiki an rubuta *Be my love* sai kuma blue ɗin wandn jeans mai kyau sosai, ƙafar shi soke cikin tomps masu masifar kyau suma C-Blue ne. Kai masha Allah 🤝 Ya Ameen mutum ne mai kwarjini da haiba, ga cika idanu.
Hakan ce ta sanya ni sauke kaina ƙasa, kama ni da yayi dumu dumu na shagalta da kallon shi.
"Ina kwana?" na faɗa daidai lokacin da ya ƙara so ya amshi akwatin.
Ban jira amsawar shi ba, na juya na shige ɗakin da niyyar kwaso wasu.
Ɗan bin baya na yayi da kallo, sai kuma ya juya yana mai fita zuwa motar tashi, bayan yayi ma Umma ta sallama.
Cikin sakin fuska matuƙa ta amsa mashi, ita kanta tana yi ma yarinyar tata sha'awar Muhammadun, yaro ne nutsattse, ga kamala da girmama na gaba dashi, Sam baya ɗaukar kanshi a wani ko wanda Allah ya mallakawa dukiya har haka.
Kwaso kayan na shiga yi ina mai kaiwa bakin motar inda naga ya ajiye akwatin, saidai fa baya wurin bansan ina ya nufa ba.
Umma ta ce ke cewa in tsaya ko tea in kurɓa saboda yunwr safe.
Girgiza mata kai nayi, Umma ba zan iya cin komai ba, kinga doguwar tafiya zamuyi insha Allah da mun isa zan nemi wani abu inci.
Da to ta bini, sabida Tasan dama bana iya karyawa tin da safe, sai ma inyi amai, har bakin motar ta rako ni, daidai lokacin da na hango Alhaji da Ya Ameen ɗin sun fito daga sashen Alhaji Mustaphan
Ƙarasowa sukayi inda muke tsaye da Umman, cikin Wasa da ƴar zaulaya Alhajin yake tambaya ta har na shirya?
Sauke kaina nayi ƙasa ina mai gaida shi, haɗi da yi mashi godiyar ɗawainiya.
Kuɗi masu yawa ya miƙo mani wai in riƙe a hannu na, kasa amsa nayi, har yanzu kaina a ƙasa yake, ina matuƙar jin Kunyar Alhajin tin da cen ma, balle yanzu da ya zama miji ga mahaifiyar tawa.
Ɓata rai yayi yana mai miƙa ma Ya Ameen, "Tunda ni ba zata amsa a hannu na ba, gashi kai ka bata idan kun isa cen, ku kula Al'ameen, banda gudu sosai,