Showing 42001 words to 45000 words out of 247770 words
ya barmu tare._
*_Page ~16~_*
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Komawar Bilal ɗinne ya sanya abubuwa suka ƙara yi mashi yawa, ginin shi da kuma kayayyakin su da suka iso, wannan ce ta sanya hankalin shi ɗauke wa daga kan su suhan ɗin, to dama dai taimako ne kawai tsakanin shi dasu acikin ranshi, ba kaman yanda yayi iƙirarin soyayyar ba gaban mahaifan nashi.
Ta ɓangaren mu kuwa, komai yayi tsanani, rashin abinci ai ba ƙaramar barazana bace ga ɗan adam.
Idan hankalina yaso ya tashi umman tawa ce ke taɓo ni, da nasiha da wa'azoji da dama, dole ne in daure in maida komai ba komai ba, gudun ɓacin ran nata.
Bamu da wani aiki a yanzu sai sallah, wanka da kuma bacci, mu kan share tsawon yini biyu bamu ci komai ba, saidai ruwa da kuma ɗan farau farau ɗin da muke kaɗawa mu sha, saboda rashin kuɗi a hannun mu, sai umma ta ce ta bani ƴan abunda suka rage a hannun ta na siyo mana fura cen cikin gari, muka dama muka ajiye in munji yunwa mu ɗiba mu tsiyaya ruwa mu kwankwaɗe, da haka har muka kwashe tsawon yini biyu
Idan ma fita muka yi tsakar gida haka zamu dinga fuskantar ƙananan maganganu da habaice habaice daga sauran ƴan uwan namu ma'aikata, hakan ce ta sanya umma ta hanani fita, idan ba aike ba to fa mun gwammace muyi zaman mu a ɗaki umma tayi ta ƙara man karatu in mun gaji mu kwanta
Ko wanki a banɗakin ɗakin namu nake yi mana, iyaka shanya ce zanyi a tsakar gida, sai sharar ɗakin namu da ƙofar ɗakin.
Mun zama bare na ƙarfi da yaji a cikin gidan, gashi shi wanda ke ɗan tausaya mana ɗin ma ya ɗauke ƙafar shi ɗaf daga gare mu, afnan kuma sun riga sun koma tini, saidai kafin tafiyar tata, tayi dabara zuwa sashen mu, duk da ba kuɗi ta kawo mana ba, abubuwa ne masu yawa nata ta tattara ta bani, irin su kaya da kayan kwalliya.
Ta ɓangaren su hajiya Kubra kuwa, komai ya mata yanda take so, magana ta mutu murus, su ɗin da ta tsana ko jin ɗuriyar su yanzu bata yi, lallai Hajiya Laila ƙawar tata hatsabibiya ce, gashi ko Alhajin ma ta dena jin zancen auren Al'Ameen ɗin a bakin shi, gashi ya sake mata sun koma kaman da cen yanda suke
To dama dai ita ɗin wannan ne kawai burin ta, tini Al'Ameen ɗin ya samo masu kuku har biyu suna masu aikin abinci,
Wannan ce ta sanya ta ci gaba da harkokinta cikin kwanciyar hankali, ta ci gaba da zuba mulki da isa da ikon ta kaman yanda take so
Likafa ta ci gaba, yanzu bata ko zama sosai a gidan, tanƙamemen shagon kayan ƙyale-ƙyale da make-up ta buɗe, irin na manyan mata da riƙaƙƙun yara masu tashe da watayawa a faɗin Nigeria.
Yara ta ɗiba kyawawa ta zuba suke aikin, wannan ce ta sanya wurin haɓaka, duk wata mace da ta amsa sunan ta a faɗin garin na Abuja shagon take zuwa ayi mata gyaran jiki, da kuma siyan kayan ƙyale-ƙyale da take yo order ɗinsu daga ƙasashe mabanbanta
To shima Alhajin baiyi yunƙurin hana ta ba, asali ma, shi ma ɗin ba mazauni bane, gara ma Al'Ameen ɗin, yafi zama a gida Nigeria, yana kula da sauran ma'aikatan nasu da suke ma'aikata da kamfanoni daban daban.
Duk da cewa ya fara jan Abie yana koya mashi abubuwan da suka danganci kasuwancin, shi kaɗai ba zai iya ba, ina zai kasu? Gashi yanzu amana tayi ƙaranci a wajen jama'a.
*********
Duk wannan abubuwan dake faruwa, Al'Ameen ɗin bai san dasu ba, tsarin da aka ɓullo dashi a gidan na hana mu abinci,
Yana iyakar ƙoƙarin shi ganin cewa babu wani ma'aikaci acikin gidan dake fuskantar matsala,
Wannan ce ta sanya ya shafa'a Sam damu da al'amarin namu, gashi yanzu ko a hanya bama haɗuwa dashi, saboda babu inda nake zuwa, haka umman tawa, kullum tana ɗaki tana karatun ta, kuma tana iya bakin ƙoƙarin ta, wajen kauda tinanin komai, gudun sake tashin ciwon ta.
Tafe yake cikin takunshi mai ɗaukar hankali, sanye yake cikin fari ƙal ɗin wandon jeans da riga ƙirar polo mai ruwan makuba.
Cikin sauri ya kwala ma mudi driver kira, da ɗan gudun shi ya iso wurin, yana mai russunawa cikin girmamawa ga uban ɗakin nasu yake faɗin "Gani Alhaji"
"Mudi gashi" ya miƙa mashi ƴan makullayen motar, "yau bana jin daɗi sosai, so bazan iya driving ba, ina so ne ka kai ni office, aikin gaggawa ya taso mani, da bazan ma iya fita ba" mudin ne yayi saurin amsar makullin, yana mai ƙara russunawa yake faɗin "Angama ranka ya daɗe"
Buɗe mashi ƙofa yayi, ta mai zaman banza ya zauna sannan ya sake zagaya wa ya shiga yayi ma mota key, tare da danna horn ga mai gadi, cikin daƙiƙa da basu Gaza biyu ba ya wangale masu gate, yayin da mudi ya harba motar bisa titi, yana mai sake danne ma mai gadi horn alamar sai sun dawo, shi kuma ya shiga ɗaga masu hannu yana mai washe haƙora.
Mudi ne ya shiga kallon ubangidan nashi ta gefen ido, dafe yake da kanshi dake sara mashi, kaman zai faɗo, gyaran murya yayi sannan ya shiga faɗin "ranka ya daɗe ko dai asibiti zamu fara zuwa ne?"
Girgiza mashi kai Al'Ameen ɗin ya shiga yi cikin rashin son Magana irin tashi, sannan ya buɗe baki daƙyar yana faɗin "Naje jiya mudi, na sha magani ma ai" ɗan guntun murmushi mudin yayi kasancewar ya san ubangidan nashi yanda yake tsoron asibiti da Allura tin ba yanzu ba, idan akwai Abunda ya tsana baifi ace za'ayi mashi Allura ba
Sake nisawa yayi cikin san gulma, "ummmmm yallaɓai nace, dama...... Uhm" ya faɗa yana mai ɗan haɗiye miyau cikin in-ina, "Ina jinka" ya tsinkayi muryar Al'Ameen ɗin yana faɗa a hankali.
"Yallaɓai ka gafarce ni, na san in bani ba, babu mai zarafin gaya maka wannan maganar, dama ina ta son samun dama, ayyuka ne da naga sun yi maka yawa ne yasa ban tinkare ka ba"
Ya isa mudi, kawai ka gaya man meke faruwa ne? " ya faɗa har yanzu idanun shi na a lumshe, hannun shi har yanzu yana a bisa kanshi, ya to kare shi da murfin motar
" Maganar su Suhana ce Yallaɓai, yarinyar nan da suke zaune ita da mahaifiyar ta, da aka dakatar dasu daga aikin gidan..... "
Cikin hanzari ya buɗe idanun shi, da suka kaɗa sukayi ɗan ja, hakan ce ta sanya suka ƙara shanye wa.
Kallon muɗi ɗin yake yi cikin alama ta son jin meke faruwa dasu ne kuma?
Baice ƙala ba, hakan ce taba mudi tabbacin yana sauraren shi kenan
"Yanzu fa ba'a basu abinci a gidan nan, bama asan halin da suke ciki ba, gashi har yanzu lokacin albashi baiyi ba, nima a bakin saude mai dafa abincin naji, kasan su da ƙananan maganganu, kuma wai........
" Ya salam" ya furta cikin tsananin firgita, sauke hannun shi yayi bisa cinyoyin shi, hakan yayi daidai da ƙarasawar tasu bakin gate ɗin tanƙamemen company ɗin, mudi na shirin danna kan motar cikin gate ɗin da tini an riga an buɗe masu
"Mudi"
"Na'am Yallaɓai"
"Mu koma gida, muyi gaggawar komawa gida, me ya sanya baka faɗa man ba tini? Wanene ya bada wannan damar ta hana a basu abinci?"
Ya jefa ma mudi tambaya cikin ɓacin rai, "Magana nake yi maka mudi"
Cikin sanyin jiki, da nadamar gaya mashi zancen da yayi muɗi ya duƙar da kanshi ƙasa yana faɗin "Allah ya huci zuciyar ka yallaɓai, Amman Hajiya Babba ce ta hana tin waccen tafiyar da kuka yi, mu kuma muna tsoron gaya maka a samu matsala, hajiya ta gane daga bakin mu maganar ta fito"
Ya faɗa a sanyaye yana mai juya akalar motar zuwa inda suka fito.
"Haƙiƙanin gaskiya raina ya ɓaci mudi, menene laifin yarinyar da mahaifiyar ta? Aikin ai basu ne suka ce basa yi ba, wannan ɗaukar alhakin yayi yawa mudi, ya kamata ka dinga sanar dani abubuwan dake faruwa a gidan, saboda na kula munafunci yayi yawa a tsakanin mata ma'aikatan gidan nan"
Mudi ne ya sauke ƙaramar ajiyar zuciya, yana faɗin "haka ne yallaɓai, Allah ya kyauta gaba, kayi haƙuri idan irin hakan ta ƙara faruwa, za'ayi gaggawar sanar da kai"
Shiru ne ya biyo baya cikin motar har zuwa lokacin da suka isa zuwa ga gidan, ko daidaita tsayuwar motar mudin baiyi ba, Al'Ameen ɗin ya ɓalle murfin motar, cikin sauri da azama ya isa zuwa ga sashen na masu aiki.
Cikin sallama yake ratsa sashen namu har zuwa bakin ƙofar ɗakin namu
Kwance nake nayi matashi da cinyar ummata da take zaune gefen katifa tana ƙara man karatun umdatul ahkam,
Nikam har ga Allah bana gane karatun Sam, yunwa ce kawai ke cina, ko motsin kirki na kasa yi, sauraren ta kawai nake ba tare da gane abunda take faɗi nake ba
Ita ɗin ma ƙarfin hali take, rabon da mu sanya abinci acikin cikin mu anfi sati, kullum saidai farau farau wanda tin jiya ma furar tamu ta ƙare
Sallamar shi ce ta dakatar damu daga karatun da mukeyi, banyi yunƙurin tashi ba, haka ma umman tawa bata matsa man ba, saboda ta san halin da nake ciki, ita ce ta yunƙura dakyal ta miƙe, bayan ta zame kaina daga saman tata cinyar.
Ɗakin da yake sakaye ta buɗe, da ɗan murmushi a kan fuskar ta, sannan ta shiga faɗin " a'ah Muhammad ne? Shigo mana, ka tsaya daga bakin ƙofa?"
Jiki a sanyaye ya sanya kai cikin ɗakin yayin da ummata ke shimfiɗa mashi yalwata ciyar dadduma a gefen ta katifar daga ƙasan tiles ɗin
Zama yayi yana mai gaida umman tawa, cikin natsuwa da girmamawa, haka itama umman tawa ta shiga amsawa da ɗan murmushi a kan fuskanta, kai daga gani ka san na yaƙe ne.
Nikau dakyal na ɗaga na zauna gami da ja na jingina jikin bangon ɗakin
"Ina kwana?" na faɗa a hankali, murya ta har bata fita sosai, kallona yayi cikin ido sosai yana mai amsawa, ya ɗauke kanshi zuwa ga umman tawa.
"umma nazo ne in baki haƙuri, a bisa Abunda yake faruwa acikin gidan nan" ya nisa sannan ya ɗora da faɗin
"Sam bansan me ke wakana ba, sai yanzu ne mudi driver ke faɗa mani, umma menene ya sanya in irin haka ta faru ba kwa sanar dani da gaggawa? Idan an dakatar daku aiki, ai ba hakan yana nufin ba kwa cikin gidan bane, kuna nan kaman yanda kuke a da"
Ya tsagaita yana kallon umman tawa da kanta yake ɗan duƙe tana murmushi, dame zata saka ma Al'Ameen ɗin? Lallai yaro ne ɗan albarka da bai biyo halin mahaifiyar tashi ba Sam, murmusawa tayi ta shiga faɗin
"kai haba babu komai ai Al'Ameen, Hajiya bata yi komai ba, ni ban ma so muɗi ya faɗa maka maganar ba, bana so hakan ya kawo saɓani tsakanin ka da mahaifiyar ka Muhammad, don Allah ina so ka bar zancen nan, Mungode da alkhairi ka gare mu, Allah yasa ka gama da iyayen ka Lafiya, ka cigaba da yi masu biyayya, insha Allah zaka ga haske a rayuwarka"
Cikin jin daɗin addu'ar da umman tawa tayi mashi ya murmusa yana faɗin "Ameen Umma, nagode kwarai da addu'ar ki, ina mai ƙara baku haƙuri insha Allah komai yazo ƙarshe, ina so komai ya tsaya iya mu ne dake nan, ku siyo abubuwan buƙata da Abunda zakuyi girki iyakar naku, ku dinga cin abinci, duk abinda kuke buƙata kuma insha Allah ku tuntuɓeni kai tsaye ina tare daku. Kuyi haƙuri da halin mahaifiya ta, ina mata Addu'a Allah yasa ta gane gaskiya"
Miƙewa yayi tsaye gami da ajiye mana kuɗi masu yawa sosai, gami da complement card ɗinshi da yake ɗauke d suna da number tashi ta waya, sai kuma matsayi shi na MD Dambulan And CEO Dambulan Estate and More, sai Address ɗin Office ɗin nashi.
Murmushi umman tawa tayi tana mai Cewa "a'a Muhammad ba zamu karɓa ba gaskiya, abun yayi yawa, ai ana hidima damu, kwarai da gaske, Allah ya ƙara buɗi"
Ameen ya amsa yana daga tsaye, yake faɗin "Umma ki amsa Alkhairin da nayi maku, ba kowa ya sanya ni ba, ni na sanya kaina, ba roƙona kuma kuka yi ba, ni ne naga dacewar hakan, indai kin ɗauke ni ɗanɗan ki da kika haifa, ki amsa ki sanya man Albarka umma" yana gama faɗar haka ya juya ya fice cikin azama, har yanzu kan nashi na sara mashi matuƙa gaya
Da kallo nabi bayan shi har ya idasa ficewa gaba ɗaya daga ɗakin namu, ajiyar zuciya na sauke a hankali ina mai zamewa na kwanta lamo abubuwa da dama na man kai kawo cikin ƙwaƙwalwa game da wannan cukurkuɗaɗɗiyar rayuwa da muke yi.
Watau ni na ma rasa gane kan wannan mutum wallahi, Ya Ameen daban yake cikin mutane, kallona na maida kan uban damin kuɗin da ya ajiye, in ba gizo idanuna keyi man ba, raper ce ta ƴan dubu ɗaya har guda biyu, sai katinshi da ke bisa kuɗin ajiye,
Ba ɓala lokaci na mirgina ina mai wawurar kuɗin, na sanya hannu na zaro masu ɗan yawa ina Miƙewa kaman zan faɗi
Mun daɗe bamu da ko sisi a daƙin, me zamu tsaya jira tinda ga dama tazo ta iske mu har inda muke? Ban bi ta kan ummata ba, na zari hijab ɗina ina mai ɗaura wa bisa kayan dake jikina na atamfa ɗinkin doguwa riga bubu dake jikina
"Umma me zan fara siyo mana muci kafin mu nemi mafita?" na furta daga tsaye ga dukkan alamu ma ba sauraren cewa da take yi "ke suhan menene haka?" nake yi ba
Ɗan murmushi tayi cikin tausaya war mahaifiya ga yaron ta ta shiga faɗin "Ko me kika nemo mana suhan zanci"
"To umma"
Na faɗa ina mai ficewa a daƙin, da zallan kallon tausayi ta bini dashi hawaye na biyo kuncin ta suna silalowa, "Allah yayi maki Albarka Hauwa'u ya ƙara shirya man ke, ya baki miji nagari, mai tausaya ma maraici ki, Allah ya ƙwato maki haƙƙin ki, ya kuma saka ma zalumcin da aka yi maki Ameen.
Ta daɗe zaune tana kuka tana share wa, gami da jera ma gudar tilon ɗiyar tata adduo'i na alkhairi da take fatan su bita ko bayan babu Rayuwar ta, sannan ta miƙe gami da kauda sauran ragowar kuɗin da kantin kada ƴan bani na iya su leƙo su gani, ɓalli ya tashi,
Abundant bata sani ba, tin bayan shigar Al'Ameen ɗin sashen ma'aikatan, mama uwani, da mama Talatu sun gashi, suna laɓe bayan ƙofar ɗakin su suna hangensu, saidai basa iya jiyo me yake faɗa ko kuma me yake wakana acikin ɗakin, fitowarshi, da kuma fitowar suhan ɗin ba jimawa da fitar Al'Ameen ɗin duk sun gani,
Cikin sauri