Showing 237001 words to 240000 words out of 261814 words

Chapter 80 - AMEENATOU

Mamuhgee   

21 Nov 2024

9990

take ba Dan haka fitarta Aiki yafara qaranci wanda ya Saka Ashley shiga fargaba sbd hasken Data qara sosai hakama Bata Wani cin abinci sosai sedai kayan ruwa ko fruits kaman lokacin Cikin Arfat Dan haka take Ashley taji hankalinta na Neman tashi.

Ita Kanta Ameeenatou din rasa gane kanta din datai ya sakata damuwa sedai Babu tinanin dayaxo kanta irin ko yanayin sauyi. Weather ne yake tabata.

Ranar da Dad dinta suka dawo tareda uncle Ahmed farin Ciki sosai suke Ciki Dan haka da dare tare gaba daya aka zauna cin abinci sedai Babu abinda ta iya ci bayan samosas din da Ashley tayi wanda Shima Dan Taga tacisa sosai ranar datai Wani Dan haka tayisa me yawa dashi aka jera a dining din.

Mum Nur dataga yanda Ameeenatou din taci samosas din da yawa batareda taci komaiba kallanta tayi tana cewa

"Am bazaki ci komaiba sai samosas dinne da kikacisa da yawa haka??

Murmushin karfin hali tayi sbd qamshin abincin dasuka hau kanta gaba daya daurewa kawai takeyi.

Apple Ashley ta miqa mata sbd Danne abinda takeji sedai tana fara ci Wani amai me qarfin ya taso mata ta miqe da sauri tabar dining din tareda ficewa da gudu sedai tana fitowa palon daidai shigowansa tareda Siddeeq.

Ashley ce ta biyo bayanta bayan ta Kalli su babbah da Dad da kowa yayi tsit Cikin mamaki da tausayin menene ya samu am din tace musu zazzabin gajiyar Aiki Ameeenatou din ke fama dashi kwana biyu.

Fitowan Ashley tabi bayan Ameeenatou din sama ya Saka Jamaal binsu Kai tsaye Yana shigowa palon Ashley ta fasa shiga bedroom din Ameeenatou din ta barsa ya shige ita Kuma sai daga baya ta bisa.

Amai takeyi sosai jikinta yayi zafi take.

Rungumeta ta baya yayi ba sosaiba Yana shafa bayanta tareda gefen fuskanta harta samu ta gama aman Cikin Jin sassauci sosai sbd yanda yake shafa bayanta da gefen fuskanta.

Wanke fuskanta sukai a tare kafin ya zubawa fuskanta Idanuwansa Yana kallanta cikeda qwarewansa a amtsayinsa na likita.

Towel ya Saka Yana goge mata fuskanta Yana Jin kaman zai hadiyeta sbd so da kauna tareda abinda yake ji.

Baice komaiba ya kama hannunta suka fito yabarwa Ashley ita ta tayata gyarawa ta kwanta kawai.

Yana saukowa siddeeq dayake zaune a palon kadai ya tarar Yana yiwa Siyam da aka fito da ita palon zaune kan wheelchair Bata iya magana bare dogon motsi sbd kanta daya juye sama sama take sedai juyewan kanta bana hauka bane tuburan idanma batai magana kaji yarinta ko shirme aciki ba bazaka ce kanta ya juyeba.

Nurse dinta ce ta fiddota palon daga bedroom dinta Dan Tasha iska.

Jamaal na ganinta dakatawa yayi tareda qarasowa gurinta zuciyarsa cikeda tausayinta da kaunarta a matsayinta na yar uwarsa.

Itama zuba masa Idanuwanta tayi bat ko kyaftawa kaman zata tinasa Amma Kuma Bata gane komaiba sai kawai ta Maida kallanta kan siddeeq daya ambaci sunanta lokacinda aka fito da ita cikeda kulawa da tausayinta Shima.

Jin tayi zuciyarta yafi kaunar siddeeq din Dan haka ahankali ta Bude Baki tana kallansa tace

"My name is Siyam Seelah,
Did you know my Dad??
Please take me ta him.....

Hawaye tafara tana qanqame kujeran datake Kai tana Neman jiwa hannuwanta Ciwo da sauri Jamaal ya miqa hannu zai cire mata sedai Yana matsowa ta fasa Kuka da ihu me qarfi.

Dakatawa yayi siddeeq yayi saurin isa ya zare mata hannuwan sbd har farcenta data kafe a jikin karfen kujeran sun fara jini.

Ga mamakin kowa daya fito palon sbd ihunta Siddeeq suke kalla sbd Bata taba yadda da kowa ba ihu takewa kowa Ameeenatou kawai takeso sai Dadah sai Kuma siddeeq din wanda Shima tsayawa yayi kallanta.

Babbah na Bude Baki sai cewa yayi shikenan an samu wanda zai fanshi Dadah a gurinta.

Maganarsa ta Saka Didi da Mum darawa sedai Kuma Jamaal sosai yanayinta ya tabasa sbd Ameeenatou dinsa ce ta fado masa arai alokacinda itama ta samu kanta a wannan yanayin.

Dad Omar ma koyaushe ya Kalli halinda Siyam din take Ciki zuciyarsa Ciwo takeyi sbd Siyam tamkar yarsace daya Haifa hakama Shima yarsa tayi wannan rayuwar a baya Dan haka yakejin radadin ganinta hakan.

Dadah ce ta qaraso ta kama hannuwan Siyam din cikeda kulawa tana share mata hawayenta tace

"Siyam Din dadah Yaya dai?
Bakyason yayanki yazo ya ganki ne?
JAMAAL ne fa,yayanki"

Qanqame Dadan tayi tana rufe Idanuwanta batason ganin kowa.

Janta dadah tayi tai Ciki da ita shi kuwa babbah akan tasa yar hankalinsa ya koma.

Jamaal da Dad Omar dinsa kuwa sbd kewan juna da sukai rungumesa Dad yayi kafin sukai sama Shima hankalinsa na rabuwa zuwa ga 'yarsa da batajin Dadi.



Ashley data Cikin mummunan fargaba kallan Ameeenatou tayi Cikin sanyin murya tace

"Am nidai Ina zargin Ciki a jikinki.....

Wani aman ne ya sake tasowa Ameeenatou din sbd dukan da maganar tai mata.

Toilet ta koma ta ringa Wani Aman jikinta na rawa.

Tana gamawa zazzafan zazzabi me qarfi Mai hade da mummunan tashin hankali suka rufeta.

Ashley ma tsinkewa tayi sbd tsoron ma babbah taji Yana shigarta da Kuma kunyar kowama duk da ba itace me cikinba Amma kusan lefin nasu ne su duka ga Jamaal gefe daya da Yana Jin Cikin idan akwai ko a jikinsa zai iya fitowa ya fada Kai tsaye.

Cikin tsoro da fargaba duka su biyun suka samu suka ga safiya ta waye Dan haka yau da wuri sukai Shirin Aiki su dukan duk da Ameeenatou har lokacin tanajin jikin Amma haka ta Danne ta daure tai Shirin Aiki suka fita a motar Ashley sbd bazata iya tuqi ba.

Fatmah data ga fitarsu take tayi zargin akwai abinda suke boyewa da alama sbd fitarsu a taren Kuma tinda sassafe Dan haka itama data fito zata fitan binsu tayi da motarta Dan saita ga ko menene sbd duk abinda zai Saka ta tona kowanne asirin Ameeenatou shi takeso sbd Jamaal ya rabu da auren Nan kowa ya huta itama zuciyarta ta huta.

Wata asibitin daban suka nufa ba tasu ba sbd tasu ansan waye Ameeenatou Kuma aga sunzo awon Ciki.

Dan haka Wani tsadaddiyar private asibiti suka nufa Suna zuwa Kai tsaye scanning ma suka buqata kowannensu zuciyarsa kaman zata fado.
#MAMUH*_Arewabooks@Mamuhgee_*
139
Ameenatou tafi Ashley shiga tashin hankali sbd harda Wani tsoro taji Yana kamata idan ta Tina babbah sbd batajin Dad dinta kaman yanda tajejin babbah sedai Kuma kunyar Dad dinta itace take sakata Jin kaman zata zare a asibitin.

Scanning ta kwanta aka fara yimata wanda tashin farko Kai tsaye likitar tana farawa tace musu Cikin kuwa gashinan lafiyayye ba matsalar komai.

Ashley kusan zarewa tayi itama sbd firgita da tsoron daya rufeta ga abin arziki da murna Amma Kuma tsoro da kunya na Neman rage musu son Cikin.

Ameenatou kasa riqe kukanta tayi ta fasa Kuka mara sauti tana qin karban takardan scanning din da ake Bata tayi gaba.

Ashley ce ta karba takardar tareda bin am din a baya sbd daman sungama biyan komai.

Ko data fito ameenatou ta isa mota tana rufe fuskanta sbd kada aga kukanta.

Bude mota tayi ta fada tareda rufewa ta fashe da lafiyayyan Kuka tana Saka kanta a qafafunta.

Ashley ma Neman shiga sabuwar damuwa takeyi Dan haka ta fara rarrashin am din Dan rage musu damuwa da fargaba gaba dayansu.

Sun jima a motar tana rarrashin am da tinanin yanda zasuyi sbd dole suna buqatan sanarwa Jamaal
kafin Ashley ta tada mota suka bar asibitin.

Suna ficewa Fatmah ta fito motarta ta nufi inda Taga sun fito.

Tana shiga Kai tsaye ta fahimci gynecology Dr suka Gani hakama scanning Akai musu wanda ganin komai dayake gurin ya sakata fahimtar hakan.

Shiru tayi tareda shock da tsoro da tinani kala kala sbd dole dole Babu abinda zai kawo macen da ba Ciki ne a jikinta ba wannan dakin.

Riqewa tinaninta yake neman Yi Dan yaka ta Kalli nurses da Dr din datai musu scanning tana Dan bayyanar musu da ko ita din jdens ce ta Bude Baki ta tambayesu abinda ya kawo wainda suka fita.

Da farko kallan rashin tinani sukai mata sbd Babu ta yanda zasu fada mata matsala ko sirrin patients dinsu Dan haka Kai tsaye Dr din tace Dan Allah ta fice kawai.

Nurses din kuwa dayake sunfi kowa iya wulaqantawa banza sukai mata batareda sun Dake ko kallanta ba.

Qaramin tsoki tayi sbd ganin batada lokacin batawa akansu Dan kallan Yan wahala ma take musu Dan haka handbag dinta kawai ta Bude ta Ciro kudin da suka sakasu kallanta dukansu lokacin da ta ajiyesu gabansu.

Batace komaiba bayan hannu data miqa musu tace results din abinda Akai mata kawai nakeso.

Kallanta sukai a tare kafin Dr din ta kalleta tace

"Bama bada copy gaskia na result sbd akwai hadarin hakan sosai ga aikinmu sedai zaki iya karanta komai gashinan a rubuce bamuyi clearing ba tukuna.

Juyo mata da fuskan screen din sukai tana karantawa batareda ta fahimci komai sosai ba tinda ba karatun asibiti tayiba ta Kalli Dr din tana Neman qarin bayani.

Cikin nutsuwa sukai mata bayanin Ciki ne na wata kusan biyu a jikinta.

Wani irin shock ne ya sake shigarta sbd Jin tabbas cikine kenan,
To waye da Cikin a cikinsu biyun sbd sunan da sukai amfani dashi na A J kawai wanda daga Ashley din har am din da A din suke farawa.

Koma menene zata gane hakan ya Dan ta nutsu sbd duk Tama rikice sbd Ciki a jikin daya daga cikinsu abin mamaki da firgici ne gaba daya.

Fitowa tayi tana Jin zufa na Dan jiqata sbd Tama rasa tinanin kamawa sbd bazai taba yiyuwa ace an samu Cikin mutum a jikinsu ba sbd a Cikinsu Babu ko me saurayi bare,
To kodai Ashley ce sbd itace tubabbiya Kila halin ba komai a haihuwan shege Yana jininta shikenan sunyi daya da Ameenatou kowaccensu nada 'dan da Babu aure aka haifesa.

Rikicewa tinaninta ya sake Yi Dan haka itama gida Kai tsaye ta nufo kaman yanda Suma Suna kamo hanyar gida Ameenatou ta dago jajayen Idanuwanta ta Kalli Ashley Cikin tsananin sanyin murya da Bata fita sosai tace

"Ash Dan Allah kada ki fadawa Jeey,
Kada yasan da Cikin Nan please
Wlh Yana sani ba ruwansa zai iya fadawa su Dad da bakinsa Kuma nidai wlh zan iya shiga kowanne hali idan su babbah sukasan da Ciki a jikina
Dan Allah kada ki fada masa....." Qarasa maganar tayi hawaye masu tsananin zafi Suna gangaro mata masu tsananin zafi.

"Nidai cire Cikin Nan zamuyi batareda kowa ya sani ba,
Gobe muje asibitin da babu wanda ya sani a cire kokuma muyi tafi kawai mubar qasar muje wata qasar a cire batareda sanin kowa ba idan mun cire mu dawo Amma wlh bazan iya barin kowa yasan da Cikin Nan ba har Jeey din." Kukan daya zo mata ne ya sakata rintse Idanuwanta tana goge fuskanta da tissue.

Ashley da itama hankalinta da tinaninta suka Dena Aiki Jin tayi zuciyarta na aminta da hakan sbd tsakani da Allah sai yanzu take gane kuskuren da suka tafka babba sbd fitar Cikin Allah kadai yasan bacin ran da zaayi hakama idan an boyewa Mam Arfat Ciki Kam a jikin Ameenatou indai anan zata rainesa to tabbas bazai taba boyuwa ba,

Hakama Jamaal tabbas Yana sanin da Cikin maganar boyewa Bata tasoba Dan Kai tsaye zai fadawa duniya cikinsa ne ba ruwansa da ciwon zuciya da hawan jinin da Wasu zasu iya shiga Dan haka itama ta zabi boye masa din a ynzun kafin su samo mafita.

Suna parking harabar gidan sake goge fuskanta am tayi tana kokarin daidaita kanta itama Ashley daidaita kanta tayi.

Sun Bude kofar motan suna fitowa motar Fatmah na shigowa harabar gidan Dan haka Idanuwanta akansu suke qur har tayi parking.

AM dataqi barin Fatmah Taga fuskanta sosai ta zubawa Ido tana karantarta sosai sbd duk yanda taso boyewa take Fatmah Taga yanda Idanuwanta sukai Wani irin kumbura sbd Kuka.

Kasa gasgatawa tayi tana sake tinano aman datai jiyan Suna dining tabar gurin da sauri wanda kowa yake tinanin cin dataiwa samosa ne da yawa.

Ciki sukai dukkaninsu Ameenatou
Sama ta haye batareda kowa yaga fuskanta ba tana isa bedroom dinta toilet ta nufa ta wanke fuskanta sedai Kuma Wani kukan ne ya sake zuwan mata ta zauna Nan Cikin toilet Tasha kukanta kafin ta wanke fuskanta ta sake Wani wanka sbd liquid din scanning da aka shafa mata.

Tana fitowa kaya marasa nauyi kawai ta Saka tareda kashe wayarta tayi kwanciyarta daki tareda rufewa tanajin ma zazzabi na Neman rufeta.

Ba Bata lokaci kuwa zazzabin ya rufeta me Dan qarfi wanda ya hada da baccin wuya da Shima yazo ya rufeta Dan haka Ashley na shigowa dubata Taga tayi bacci sai kawai ta kashe haske tareda rage mata AC tukuna ta fice itama jiki duk zazzabin na Neman kamata sbd sanyin jiki.



*******Dad Omar kuwa Dama bawa Ahmed akan a saki Mam wanda ko 'dansa baisan cewan rufesa Akai ba sbd duk inda zancen zai fita Basu bari ba Dan ko inda aka rufesa babu wanda zai gansa bare zanfen ya fita.

Ko da aka fiddosa gabaki daya ya sauya daga Mam ya koma Mamman dinsa Dan Wani irin warin zufa daya fitarwa da tsananin baqin Cikin dayake cin zuciyarsa datake Neman bugawa ya Saka ko abinci tinda aka rufesa Baici ba Dan hakan Nema ko karfi sosai baida a jikinsa sai zuciyarsa da kawai take ci da wata irin wutar da baisan iya illan da zaiwa kowa ba a yanzuba.

Motar jami'an tsaron har kofar mansion dinsa suka ajiyesa wanda Babu masu Aiki ko daya duka siddeeq ya sallamesu Dan haka shine ya a budewa kansa kofar gate din datake Bude ya shiga.

Kai tsaye kofar shiga dayake Gani Bude cikeda mamaki ya dosa sbd koina a Bude.

Yana Sako Kai palon ya tsaya cak tareda dago Idanuwansa da sukai Wani irin jajir Yana kallan koina sbd kusan Babu komai barayi da suka samu gidan Bude sunata shigowa Suna sacewa.

Babu abinda yake palon bayan kujerun palon masu tsananin tsadar gaske Amma hatta curtains din miliyoyin kudin Dake palon an sace bare sauran luxuries din Dake Palon.

Qafafunsa da sukai masa Wani irin nauyi ya daga Yana nufar dakunan mansion din daya bayan daya Yana Jin zuciyarsa na sake shiga Wani irin radadi da Ciwo,

Ayau ace shi Mam seelah ne qananun barayi masu Satan kaya suke shigowa gidansa Suna yiwa kayansa dauki daddaya.

Bedroom dinsa ya Bude anan ya tararda Wani mummunan shock din sbd suturar sakawa ko daya baa bar masa da zai Saka komai an kwashe hattada takardunsa da komai da komai na rayuwarsa masu Mahimmanci da marasa Mahimmancin ma an dauke duka.

Bangon dayake gefensa ya dafa Yana Jin Wani zafi da radadin gaske na ratsa zuciyarsa.

Wayarsa ma da zaiyi waya Babu sbd ranar daya bar gidan Bai fita da itaba anan yabarta Dan Bata Cikin motarsa da aka kamasa da ita tinda da ita aka dawo dashi Kuma Babu aciki.

Jan jikinsa yayi kaman me ciwon laka ya nufi bathroom din dakinsa ya shiga abin baqin Ciki hadda Kashi anyi an cika toilet seat din dashi.

Wanke toilet din yayi da hannuwansa da basusan aikin komaiba bayan Hutu da kisan ruwan sanyi.

Yana gama wankewa wanka yayi ya fito kayansa daya cire su ya kalla ya kakkabe ya sake mayarwa ya fito.


Motarsa ya shiga Kai tsaye Bank ya nufa Dan cire kudi sedai Kai tsaye aka sanar dashi Babu abinda yake bankinsa bayan 100k.

Yanke jiki yayi ya Fadi Cikin bankin Yana Neman kamuwa da ciwon zuciya.

Taimaka masa Akai aka kaisa har office din manager tinda ansansa babba ne sune wainda suke da manyan kudin da babu me irinsu a bankin Dan haka Ciki kulawa da girmamawa manager yayi masa bayanin da wayarsa Akai amfani aka cire kudin bankin gabaki daya zuwa bankin 'dansa Jamaal Seelah manyan Kuma da basa fita shine da kansa yazo ya cire sbd shine magajinsa dayake rubuce wanda kadai zai iya cire kudinsa bayanshi wanda tin farko shi Mam din ya saka Jamaal dinne a matsayin wanda kadai zai iya cire kudin dayake accounts dinsa na Nigeria Dana waje sbd yasan har abada Jamaal Babu abinda zaiyi da ko qwandala a Cikin kudinsa sbd tsanar da yayiwa dukiyarsu da Kuma tasa dayake da ita baya buqatan qarin.

Cikin mutuntawa aka Ciro masa sauran kudinsa aka basa Wanda yana fitowa motarsa ya shiga baya Gani sosai ya nufa Wani boutique ya Siya ready made masu yar kudi sbd ya Saba Saka masu tsadar.

Kaftan ne na 80k ya Siya ya sauya kayan jikinsa kafin ya wuce Kai tsaye gidan drivernsa da shine yasan dukiyarsa ta boye.

Yana isa ya tararda labarin shida matarsa sun bar qasar gaba daya zuwa south Africa.

Daga Nan Kai tsaye gidan Jamaal ya nufa zuciyarsa na gap da bugawa Amma bazai taba yadda yayi qasa ba sbd haryanzu Yana power da zai iya illata Omar da ita tinda 'yarsa itace abinda yafi so to tabbas zai dandana masa radadi da ciwon rasa abinda kakeso sbd Jamaal bazai taba masa hakan ba batareda Saka bakin Omar.

Hakama Aleena zata zama matarsa ne kadai a lahira idan sun hadu acan Amma badai idan shi Mam Yana Raye ba.
#MAMUH*_Arewabooks@Mamuhgee_*
140
Dr Aleena zaune take ita kadai a palon Jamaal dayake Sama tana magana da Siddeeq wanda ta Kira zasuyi magana tinda a palonta ko palon qasan maman fadeela zata iya ji ko Ayesha Kuma batason ko kadan su San asalin waye Mam bare Jin abinda zasu fada gashi Jamaal baya Nan ya fita tin safe Yana tareda Dad Omar gurin Wani Mahimmin meeting.


Jamaal baisan Dad dinsa ya dawo ba a ranar
Shikuwa Dad Omar Bai dauka an Riga an saki Mam dinba sbd ya dauka sai bayan sun dawo Ahmed zai isar da sakon Dan haka Babu wani special tsaro a gidan ranar sai iya securities na gidan Dan haka Mam na isowa Babu musun komai suka Bude masa gate kaman yanda suka Saba ya shigo fa motarsa.


Mum Aleena kuwa tana sama da Siddeeq ta kallesa tace

"Siddeeq Omar ya fadamun zaa Sako Mam yau Kuma a yanzu idan ya fito kowama Yana Cikin hadari musamman Ameenatou da Arfat sbd Mam bazai taba iya rayuwa Babu dukiyarsa da Bai hada da komai da kowaba,
So tinda Omar haryanzu Bai fada mana ARFAT 'dan JAMAAL bane Nima bazan masa maganar mun sani dinba Dan haka ba Damar ce masa a kula fiyeda tinani akan Arfat sbd Mam a yanzu kaman a haukace zai fito inason ne kawai kayiwa Ashley magana koina Kar asake fita da Arfat yanzu sai komai ya lafa"

Numfashi siddeeq ya sauke Yana kallan Mum yace

"Mum karki damu babban tsaron da Arfat yake Ciki ayanzu shine rashin saninsa

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login