Showing 45001 words to 48000 words out of 261814 words

Chapter 16 - AMEENATOU

Mamuhgee   

21 Nov 2024

9964

Kuma wani lokacin Yana sane da batada gaskiyar Amma Baya yadda sedai idan sun dawo gida yayi mata fadan kafin ya lallasheta daga baya.

Duk da su bamasu hali bane Suna rufin asiri sbd su Hafiz na aikin karfi hakama babban duk da manyanci sosai Yana Dan babbuga sanaar dabbobin Daya Saba Babu wani samu sosai Amma sbd inganta rayuwan Ameenatou Babu Wanda yayi qasa a gwiwan Nema.

Ameenatou Bata rasa komai ba sbd Tako ina Babu abinda take nema ta rasa,
Tana cikin gata gaba da bayanta hakama har yanzu datake budurwanta batasan basu babbanta ne suka haifeta ba kaman yanda a garin kaf Babu Wanda yasan da Hakan,
Har mamakin akeyi yanda sukeda manyanci sosai Amma sunada qaramar 'ya sedai Babu Wanda ya taba kawo tinanin basune asalin iyayen nataba duba ma da yanda suke tsananin jinta fiyeda komai.

Ameenatou duk gatanta da sangartan da Akai mata tanada tarbiya sosai Dan kuwa sun Bata kyakkyawar rayuwa su Hafiz musamman Yaya Abdul Basu bari gatan ya lalatata gaba Daya.

Bangaren Bata ilimi kuwa sai inda karfinsu ya kare Dan kuwa makarantar primary ma ta kudi tayi Bata gwamnati ba duk da bawai kudi Basu yawa sosai ba Amma dai private school ce.

Secondary ma Bata gwamnatin takeyiba yanzu tana shekarar gamawa Dan haka daidai gwargwado tanada iliminta kaman su Hafiz din da Suma sunyi karatun bokon Dana Addini kowannensu nada diploma Amma dai Babu wani aikin bare Dora karatu me kyau da amfani sai suke Yan buge bugensu.

A cikin gidan kauna da shaquwa ce sosai a tsakaninsu da barkwanci tin daga kan babban har Dadah dasu Hafiz,
Sosai suke cikin Kwanciyar hankali da farin ciki,
Hafiz da Ameenatou akwai shakuwa da rigima sosai fiyeda Yaya Abdul duk da Shima akwai shaquwan da kauna sosai Amma shi Bata renasa ba kaman yanda ta Rena Hafiz.

Duk inda zata makarantar boko ko islamiya ko wani abin daban basa barinta fita ita kadai shiyasama duk irin shirmen soyayyar da kawayenta keyi ita Bata yi hakama Allah Bai Saka mata shaawan soyayyar da sukeyiba kwata kwata batama ganin kanta a wadda ta Isa fara soyayya.

Akwai masu Sonta da yawa sbd kyau da haskenta tareda gatanta da kyan jikinta Amma suna shakkar tinkararta da maganar soyayya sbd kullum tana tafe da babanta ko yannanta hakama gata kaman Me rariya a Baki koka zagaya kaje makaranta kace kana Sonta tana Isa gida take fadawa yayunta ko Babbah azo ana rantse rantse a gaban me gari ace kana bibiyanta shiyasa kowa ya kama kansa da ita duk da akwai Yan nacin da duk masifar Babbah suna Nan kan bakansu.

Tinda dadewa Yaya Hafiz ya daukota daga makarantar boko ya biya da ita site gurin Hafiz yace tinda lokacin tashinsu yayi ya wuce da ita gida shi gurin aikinsa ana nemansa.

A ranar idanuwanta suka ganar mata kyakkyawar halittar da Bata taba ganin me kyansaba tinda take.

Da farko kasa yadda tayi da mutum ne seda ya tinkaro inda suke sanye da baqaqen kayan dasuka fidda farinsa sosai ga Rana tana haskasa sai wani daukan ido yakeyi duk sai Taga su Yaya Hafiz da sauran ma'aikatan gurin sun koma mata kaman wasu halittun daban ba mutane ba.

Bakinta ta sake tana kallan fuskarsa dake sanye da black sunglasses me shegiyar kyau da fcap akansa Yana magana kaman ranar zata kashesa Dan kuwa alamunsa sun nuna Hakan.

Fitowa tayi daga inda take ta nufi inda yake Kai tsaye Dan kuwa idan ba gabansa ta tsaya tayi masa kallan kurulla ba bazata tantance abinda idanuwanta suka ganiba.

Hafiz ne yayi saurin riqeta daidai tana gap da Isa gabansa Yana cewa

"Ke Ina zakije?

Kwacewa tayi tana cewa

"Yaya Hafiz wannan baturen shine oganku?
Kullum ze Riqa zuwa ne??

Tunkuda keyarta yayi ya maidata inda yace ta jirasa tayi wani Dan qaramin ihun Jin zafi tana cewa

"Tambaya fa nayi Kuma baka ban amsaba ai"

Jin maganar mace a gurin ya Sanya JAMAAL juyowa ya Kalli gurin daidai Hafiz na rufeta da bayansa Yana fuskewa.

Ganin Babu kowa yasashi juyawa Yana ci gaba da sauransu bayanin da ake masa ita kuma ta fito tana cewa

"Bazanyi magana ba kallansa kawai zan riqa yi" ta Dora hannunta Daya a bakinta tana zubawa Jamaal din idanuwanta masu haske da kyau tareda yin shiru.

Sautin muryansa me tsananin nutsuwa da kamewa acikine Taji Yana magana Rabi duk turanci Wanda ita bama irinsa malamansu keyiba dasu kansu Dan Wanda suka iya.

Tinda tafara kallansa tana Jin muryansa Yana magana Bata qara motsi ba har Saida ya gama ya juya yabar gurin Bata motsaba sai murmushi takeyi.

Hafiz Daya gama aka sallamesu sbd maigidan nasu Daya wuce kama hannunta yayi yaja suka bar gurin Saida sukai Nisa ta kwace hannunta tana matsowa kusa dashi sosai tace

"Yaya Hafiz Yaya sunansa?
Bature ne ko balarabe?

Suna Isa gida ta bawa babba da dadah labarin Taga irin Wanda zasu Nemo mata a matsayin miji idan zasu mata aure.


Tin daga wannan ranar Ameenatou Babu ranar da Bata maganar baturen ogansu Yaya Hafiz,
Kaf gidan saida suka gaji da Jin kalan kyansa datake fadan kaman Rana zata konasa yanata kyalli.

Haka zalika tin daga lokacin Yaya Abdul ko Babbah suna daukota daga makaranta gurin Hafiz suke ajiyeta shikuma daga Nan yaje da ita gida duk Dan sbd tagansa Amma kuma abin mamaki tin daga ranar Bai sake zuwa ba bare ma ta gansa daga qarshema sai gashi anrufe site din gaba Daya tareda aikin dole suka koma Neman wasu ayyukan kafin idan Allah yasa zaa dawo da aikin sai gashi kuwa kwatsam ance su shirya su koma bakin aikinsu Kuma me gidanma yananan tafe da kansa.
#MAMUH#
#AMEENATOU
#THE SEELAHS


*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
30
Washe gari Tin 7 na safe Yaya Abdul ya shirya fita aiki ya tsaya jiran Budurwar babban Amma dai lokacin ma dadah ke tadata bacci cikin lallabawa da tausayinta akan tashin safen Wanda yake kular da Hafiz Dake tsakar gidan Yana wankin kayansa Dana Ameenatou din.

Brush tafara kafin Tayo wanka ta fito ta nufi daki Dadah haryanxu data girma tayata shiri takeyi.

Sai kusan takwas saura ta gama shiryawa ta fito tsakar gidan ta zauna gefen Babbah dake zaune kan tabarma.

Farin Koko me kyau da aka zuba mata zuma aciki ta dauka a cup da fanke manya manya da zafinsu sun soyu tafara Sha tana fadawa Babbah gobe bazata je makaranta ba duk idanuwanta rage girma sukeyi Bata samun bacci gashi da Rana ma Bata samu.

Cikin kulawa da yadda da abinda ta fada din Babbah ya gyada Kai Yana cewa

"Na lura da Hakan sarai 'yar budurwata magana ce kawai banba sbd Yan Saka idon gidan Nan Amma gobe Babu inda Zaki ai ana son Rai da hutawa"

Juyowa Hafiz yayi sbd ya Dena mamakin lamarin babbah da budurwan tasa Amma takaici Baya barinsa yin shiru Dan haka Baki sake yace

"Wlh duk ranar da kika sake tsallaken zuwa makaranta bazaki sake zuwa site ba ko oga yafara zuwa aiki kuwa,
Sai naga karshen rashin bacci."

Kallan babbah ta dago tayi da idanuwanta da suka narke tana masa alaman yayi magana.

Inda yake babbah ya juya ya kalla Yana jifansa da wani mugun kallo yace

"Nine nace bazata goben ba sai naga abinda zakayi"

Yaya Abdul da hakurinsa ya fara karewa sbd yayi masifan lattin Danma Babu ranar da Baya latti sbd ita cikin kulewa yace

"Zan tafiyata idan Baki nutsu kin gama abinda yake gabanki ba Kokuma ki tashi mu tafi hakanan Baki gama cin abincin ba."

Dadah Daketa Kaida kawon hada mata jakarta da ruwanta a sabuwar roban ruwa me tsafta sosai da Yaya Abdul ya sake siyo mata miqawa Abdul din dayake tsaye Yana harare harare tayi tana cewa

"Dan taimaka riqe mata kafin ku Isa"

Baida lokacin batawa na musu Dan haka ya karba kawai zai sake magana Dadah ta rigasa da cewa

"Yi hkr saura kadan fa ta gama karta qware duk Kuna Neman rikitata"


Hafiz ajiye wankinsa yayi Yana nufota Babbah ya jefesa da wani kallan daya sakashi tsayawa Yana cewa

"Babbah wai meyasa kakemun hakane duk lokacinda naso gyarawa wannan yarinyar zama duk ta renani ko abokaina fa sunsan ta renani a gabansu Babu kalan sakarcin da batamin gudun nakeyi wataran na harzika na babbalata jinin mutane yayita Hawa"

"Karka wani Sakaya fito fili kace jinina Dana uwarku ya hau,
Zaka koma aikin gabanka kokuwa saina ce Abdul din ya tafiyarsa ka aje wankin ka Kaita"

Ball yayi da takarmanta Dake gabansa Yana juyawa ya koma aikinsa Dan ba qaramin aikinsu Babbah dinne ba ace ya aje wankinsa ko wanka beyiba ya Rakata makarantar.

Miqewa tsaye tayi bayan ta gama tana goge bakinta da tsaftacciyar kyallen sabuwar atampa da Dadah ta miqo mata ta Saka takarmanta masu kyau Wanda suka Hafiz dinne ya siyo mata Dan komai nata Hafiz da Yaya Abdul ne ke Siya
Babba kuwa a siya mata kayan ciye ciye da kwalama Yan canjinsa suke karewa sai fura da asalin Madaran fulani me kyau dayake siyo mata duk dare Wanda yawanci ita take Sha Bata cika cin abinci ba sai idan Yaya Abdul ya siyo mata kwai zuwa makaranta take ci da dare.

Suna fita tana gefensa tana masa surutu suka kama hanyar makarantar Yana amsata sama sama sbd hankalinsa na kan gurin aikinsa dayayi latti gashi Basu yadda da kowaba akanta da tini mashin zai ringa Bata kudi tana Hawa Amma kwata kwata Basu yadda da kowaba akanta shiyasa duk tsananin latti da rashin jinta basa iya barinta taje ita kadai makaranta kuma itama kanta sbd sabo da Hakan Bata iya tafiya koina batareda dayansu ya Kaita ba tsoro ma takeji na bin hanya ita kadai.

Suna Isa gate din makarantar ya miqa mata kayan ciye ciyen Daya Siya mata na break Dan basa Bata kudi kwata kwata.

Karba tayi tana masa Godia da fuska a cakude sbd lattin datai tasan Kuma Yaya Abdul din Babu rokon dazaije yayi mata Dan haka ta juya ta shige tana ciko idanuwa da hawaye Dan a tausaya mata.

Cikin babbar sa'arta malamin data tarar Yana Taron lattin Baya ko kallan inda take kwata kwata sbd tashin hankalin Daya taba Sha shida Babbah da Hafiz akan dukanta Daya taba yi
Babbah yazo makarantar ya rufe ido ya zuba musu tsiya rigima har gaban shugaban makarantar kawu yayi mirsisi ya nuna Yar budewarsa Bata da laifi shine Babu lafiya shiyasa batazo da wuri ba.

Dayake sunsan ba yadda zeyiba daga Nan har hukuma Dan haka suka basa hakuri aka rufe maganar,

Tin daga lokacin da yawa malamai basa taba Ameenatoun sbd Babu me buqatan rigima kowa na fama da kansa.

Simi Simi kaman munafuka ta wuce ciki tana Jin dadi a zuciyarta Dan idan akwai abinda ta tsana a duniya shine a taba lafiyar jikinta,
Bata kaunar abinda ya taba jikinta shiyasa Sam batason duka ko faduwa bare Jin ciwo.

Idan kuwa taji ciwo a gidan jinya zata kwanta a ringa fama,kafin ta warke zuciyar Hafiz saita kumbura ta huce yafi so a kirga sbd yanafin kowa Shan wuya da takaici Dan a kansa sakarcin yake karewa.


Farin jini datake dashine ya Saka yakeda kawaye masu tsananin son binta koina Amma da Aminiyarta Daya Khadija.

Karfe biyu saura Yaya Abdul yazo ya dauketa Kai tsaye gida suka nufa ko shiga beyiba ya juya ya koma gurin aikinsa ita Kuma ta shige a gajiye duk da Yaya Abdul din ya Siya mata yoghurt me sanyi sosai yazo mata dashi Amma dai batasha ba tana shigowa ta miqawa Dadah hadda Jakarta da komai ta tube a tsakar gidan ta daura zani ta nufi bandaki Tayo wanka tana fitowa abinci kawai taci Tayi sallah ta share dakinta dana Dadah duk da fes suke Dan Dadah akwai tsafta.

Tana gamawa bacci kawai ta kwanta abinta.
Sai kusan hudu ta tashi tayi Shirin makaranta dayake Hafiz yasan lokacin gama shirinta tana gamawa Yana dawowa yace ta fito su tafi yakaita sauri yakeyi akwai inda zashi.

Tin a cikin gidan suka fara rigima har suka Isa ta shige ya juya ya wuce inda zashi.

Da yamma kuwa babbah ne ya biya mata suka dawo gida tare Yana Bata labarin inda yaje da abinda ya Gani tanata Jin dadi.

Da daddare yau kusan kowa Yana gida lokaci Daya sukaci abinci su a tsakar gidan tanata zuba shagwabarta yanda takeso a cikin iyayenta da yannanta.


*****
Zaune yake a gaban Dad dinsa jikinsa gabaki Daya a mace,
Daga shi har Dad da Dad Lameenu dasuke palon su a zaune Babu me walwala ko farin ciki ko kadan a zuciya da fuskokinsu,

Tarin bacin Rai da baqin ciki ne yake sake tirnike zuciyar kowannensu Yana Kona jininsu.

Dad Lameenu dayake Jin kwata kwata baiga amfanin Haroon a rayuwarsu ba sbd Babu inda suka Kara gaba kullum sai Baya sukeyi suna Neman durkushewa ba shiri,

Rashin JAMAAL a rayuwarsu wani babbar balai da masifa ne Dan kuwa sun sheda Hakan Kuma suna kan shedawa tin daga ranar Daya barsu komai sai rushe musu yakeyi,

Shi baimaga dalilin wani Yanke yanken alaqa ba da Mam yayi da Jamaal din dan kuwa da Haroon din ya miqawa Dr Aleena can taje dashi tayita kayan rashin amfanin dashi.

Mam kasa cewa komai yayi sbd yanason ya kasawa ransa iya danne tsananin rashin 'dansa JAMAAL a taredashi,
Yanason ya Hana abinda yake cin zuciyarsa gameda rashin Dansa,

A tsawon shekarun Nan da suka diba basa tare Babu ranar da Baya kwana ya tashi da tsananin son kasancewa da JAMAAL,
Babu ranar da Baya kewansa,
Babu ranar da Baya baqin cikin faduwa da rushewan da sukeyi sbd rashinsa.

Kallan Haroon ya sake yi Yana ajiye takardun hannunsa Daya gama karantawa y
Zuciyarsa na quna yace

"Se yaushe ne zaka zama me amfanin dazanyi alfahari dakai amatsayin Dana?
Kasan irin millions din da muke rasawa akowace safiya tindaga ranar da Jamaal ya tafi kuwa??

Zaka iya lissafa asara da faduwan da muketa yi kullum?

Menene yake faruwa acikin kanka ne da kwata kwata Babu Abu Daya a cikin lamuranmu dayake tafiya daidai?

Aikin site dincan a yanzu shi kadai ne abinda ya rage a tayar shine abinda zai hanamu karasa rugujewa sbd ka lalata komai,
Ka rusa abinda mukai aiki tukuru da jini da majina muka hada,
Ka rusa abinda Dan uwanka yayi aiki dare da Rana ya hada duk kana Neman lalata komai a cikin shekaru kalilan."

Dad Lameenu kuwa kasa magana yayi sbd Jan da idanuwansa sukai zuciyarsa na quna cikin baqin ciki da tashin hankali.

Har abada bazasu hada Haroon da Jamaal ba sbd Jamaal zakin namiji ne da kosu suke shakkarsa,

Ga Haroon yau ya Sakasu a tsaka me wuya sbd Bai iya komaiba sai rusasu yakeyi da rashin amfaninsa.

Cikin zafin zuciyar Dad yace

"Ka tafi ka fara Shirin tafiya wancan babban project din,
Abu Daya nakeso ka sani,
Wannan aikin shine aikin dana Saka dukkanin burina akansa yanzu
Samun matsala akan wannan aikin shine rugujewanmu gaba Daya Dan haka ko rayuwa nawa zaa ci a aikin Nan banason ka tinkaroni da matsala duk tsanani duk rintsi,

Ka nutsu dakyau ka fahimci mahimmanci wannan aikin a gurinmu,
Ka tafi kasan abinda kakeyi idanma haryanxu rabuwarka da Dan uwankane ta kasa sakinka to ka sani wannan Karan a shirye nake da kawar da matsalata kowace iri ce."

Wani abu me dacin gaske Haroon ya hadiye kansa da kirjinsa na wani irin nauyi da radadin dayake cikinsa na tsawon shekarun Nan,

Tinda Jamaal ya rabu da Dad Bai sake sanin farin ciki ko samun kauna daga mahaifinsa ba Kona Rana Daya ne,

Shi kansa ya sani baida jarumta ko ilimin aiki irin wanna da Kuma izzar gudanar da manyan huldodin kasuwanciba irin Jamaal,

Baida sa'a kaman Jamaal,
Baida cika ido da kwarjinin kasuwanci acikin manyan mutane na gida Dana waje kamar Jamaal

Rayuwarsa gaba dayanta akan abinda ya karanta ya kwallafa ta sedai Kuma babbar jarabansa itace kauna da son kyautatawa mahaifinsa Daya rufe masa zuciya da ido Amma duk yanda yake kokari Dan zama hasken idaniyar Dad din Hakan Bai taba samuwa ba saima lalacewa da komai yakeyi.
Baya tareda mahaifiyarsa,Baya tareda Dan uwansa Baya da kowa sai mahaifinsa da sauran dangin seelahs da duk Babu Wanda yake appreciating nasa ta koina da komai sai Hakan yafara tabasa ahankali ahankali har depression na shigarsa batareda kowa ya sani ba bare fahimta.

A yanzu da shine komai na Seelahs yadawo hannunsa shine yake juyata Babu abinda Bai saniba na sirrinsu Dad sedai bazai taba iya fadawa Dan uwansa Hakan ba,

Bai iya illegal huldodinsu ba,
Bai iya juya business na Seelahs ba na bayyane Dan haka gaba Daya rayuwarsa ta tashi daga Haroon seelahs Takoma wani mutumin daban dabai San kowanne farin ciki ba bare walwala sbd haryanxu Babu abinda yakeso kaman burge mahaifinsa ya samu yabo da alfahari daga garesa.

Wannan aikin na site a yanzu shine abinda zai basa Daman samun yabo da kauna daga Dad dinsa yanda yake buri Dan haka yayi alkawari tareda sakawa ransa zaiyi aiki tuquri akan wannan project din.
Shiri ya fara na tafiya Nasarawa tareda sakawa Akai masa booking na hotel da komai.
##MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
31
Bayan ficewan Haroon daga palon kallan Mam Dad Lameenu yayi cikin nauyin zuciya da rashin Jin dadin komai na duniya yace

"Dole muna buqatan tsananta binciken abinda àka haifawa Omar duk inda yake sbd sanin inda suke zai Saka Omar din dawowa daga inda yake ya dawo cikinmu sbd sanin munsan yanada 'da a duniya,

Idan ba Hakan mukaiba cikin gaggawa wlh muna gap da rasa komai munaji muna Gani Dan haka yanzu Kam dole mu tashi tsaye dakyau mu samo 'dan Omar"

Mam da zuciyarsa tafi ta lameenu tsananta a cikin baqin ciki da tafasa tareda bacin Rai baice komaiba sbd Daman ya hangowa kansu Hakan daga ranar da suka Dora Haroon akan komai nasu,
Sam baida jarumta ko amfanin da zai musu yanda ya kamata.

Ta bangare Daya yasan duk Wanda zasu Saka a magajin nasu me gudanar da komai bazasu taba samun Jamaal ba Dan kuwa shi din zakinsu ne.

Numfashi ya sauke ahankali Yana kallan takardun gabansa da idanuwansa da sukai jajir Yana kokarin daidaita tafasar da zuciyarsa keyi,
A yanzu shima Babu abinda ruhi da zuciyarsa suke tsananin buqata kaman dukiyar Omar Dan ita kadaice zasu mallaka suyi

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login