Showing 183001 words to 186000 words out of 261814 words
bugawa da shirun nasa tareda jiran abinda zai fada sbd Dad Omar maganar bakin Jamaal din kadai yakeson ji bana kowa ba.
Fatmah kuwa zufane sharaf ya jiqa doguwan rigan jikinta a take hakama zuciyarta Wani harbawan wuce lafiya takeyi ta Tako daqyar ta sake matsowa gap da AM ta tsaye sbd taji abinda zai fada din daidai.
AM din kuwa fuskanta itama hadewa tayi ba rahama ko daya a Cikinta sbd Batama San me suke kokarin fada ba tinda dai ba hauka akeyiba zaace ita matar Wani ce batareda ko mutum daya a Yan uwanta ko iyayenta sun sani ba,hakama aure da wanda Bata taba sani ba,
Dan uwansa ta sani shine masoyinta Kuma ya rasu to tayaya zaa fara wannan soki burutsun zancen.
Juyawa tayi zata bar gurin sbd numfashinta ma dayake Neman tsayawa da yanda zuciyarta ke bugawa daga Cikin kirjinta.
Tako daya tayi ya miqa hannunsa daya ya kamo nata tareda dawo da ita gabansa ya Kalli Cikin tsakiyar Idanuwanta kafin ya dawo da ita gefensa ya dago ya Kalli Dad Omar da har lokacin shi yake jira Kai tsaye Cikin nutsuwa da kwanciyar hankali yace
"I'm sorry Dad Omar,
Amma Ameeenatou is my wife,
Aurena yana kanta tsawon shekarun Nan,
A ranar da Kuka bar Nigeria a wancan lokaci a ranar na daura aure da ita,
I paid for her sadaki, Matatace, my halal.......
Numfashi me zafin gaske Dad Omar ya sauke Cikin nutsuwa Amma Wani irin tafasa jininsa keyi da zuciyarsa,
Babbah kuwa Jiri ne ya dibesa Amma dadah da jikinta itama yake rawa tayi saurin riqesa tareda Hafiz da Shima jirin da tafasar jini da zuciya yake Ciki Dan har Idanuwansa sunyi Wani irin jajir take.
Uncle Ahmed ma nauyi yaji jikinsa yai masa ya silale ya zauna kujeran dayake kusa dashi.
Fatmah kuwa da sauri Didi tayi saurin matsawa kusa da ita Dan tareta batareda kowa yaga halin Data shiga ba na Wani irin rawar jiki da zufa.
Mam Wani sabon farin Cikin ne ya sake mamayesa sbd maganar Jamaal din Kai tsaye ya sake tabbatar masa da Jamaal jininsa ne yake yawo a jikinsa.
Dad Omar dayaketa kokarin hadiye abinda yakejin kallan Jamaal yayi da jajayen Idanuwansa tsawon seconds kafin ya Bude Baki a shaqe ya furta
"A Ina?
Waye shedan hakan?
Meye dalilinka na yin hakan?
A bisa wane hujja?
Da izinin waye?
Siddeeq dayake a shiryensa dan jiran hakan matsowa yayi ya zai miqawa Dad Omar din ipad dinsa Mam ya taresa da cewa
"Muna buqatan zama sbd zance irin wannan Yana buqatan nutsuwa a tattaunasa"
Kaman wainda duka akaiwa Baki zaunawa kowa yayi Banda Ameeenatou data fizge hannunta daga Cikin nasa tana matsawa nesa dashi cikeda radadi da nauyin zuciya Dan har yanzu ta kasa yadda da abinda suke fada shi da Dad din nasa.
Babbah miqewa yayi wuf ya kamota ya riqe hannunta tareda dawowa da ita gefensa sbd da alama a Cikin daren yau idan har maganar auren Nan ta tabbata akwai to guduwa zaiyi da yarsa bazai taba bawa jinin Mam 'yarsa ba,
Yafison su komawa talaucin da suka fito da wannan mummunan kaddarar ta tabbata a kan idonsa ace ya hada zuria da Mam.
Dadah ma riqe Ameeenatou din tayi kaman yanda Hafiz ya dawo Shima gefensu babban suka sakata a tsakiyarsu Dan Babu maganar aure tsakaninta da JAMAAL har abada.
Ipad din Siddeeq ya ajiye gabansu wadda take dauke da video din saurin auren tsaf tin daga farkonsa har qarshensa wanda shine da hannunsa ya dauka sbd yasan wannan ranar zata taho tinda basuda shedan daurin auren,
Video din na gama playing Mam ya daga wayarsa ya kira bullet Dake wajen mansion din Cikin mota tareda baqo yace su shigo.
Securities Saida uncle Ahmed ya kirasu a waya suka bari bakon ya shigo mai Aiki taje har gate ta shigo dashi har palon.
Siddeeq na ganinsa saurin kallan Jamaal yayi sbd limamin daya daura auren ne sun nemesa kaman me Basu iya samunsa ba.
Jamaal bayansa ya jingina jikin kujera ahankali Yana Dan rufe Idanuwansa da sukai jajir ya Bude yasan Dad dinsa zaiyi fiyeda hakan akan cikar burinsa.
Kowa palon kallo daya yayiwa mutumin ya gane shine madaurin auren Dan haka take Fatmah ta fasa Wani irin Kuka me cin Rai daya kasa dannuwa duk yanda taso ta dannesa tin dazu.
Didi ce tayi saurin Janta suka bar palon Mum Nur ma ita tsoro ne takeji Tako Ina Yana shigarta Dan kuwa ziyara gidan Mam batajin zata iya kaiwa bare zaman dindindin a Cikin familynsa.
Bayani daya bayan daya a tsare mutumin ya jero tareda Basu tabbacin aure Kam akwaisa shine ya daura a bisa ga bayanin komai da Jamaal yayi masa na halinda ake Ciki Kuma Shima yayi Naam da hakan ya daura auren.
Uncle Ahmed ne kadai yakeda karfin halin tambayoyi da duba komai daki daki ya tabbatarda dai aure akwaisa Ameeenatou matar JAMAAL ce his halal kaman yanda ya fada.
Nauyi kirjin babbah yayi ya zubawa Jamaal din Idanuwansa yanajin yanason yayi masa tsanar dayakewa mahaifinsa Amma hakan Bai samu ba sedai Kuma tsanar auren dayake ji daidai take da tsanar dayakewa Mam Dan haka ya miqe daqyar dadah ba riqe hannunsa ya Kalli Omar muryansa na rawa yace
"Indai nine uban Ameeenatou ban karba wannan auren ba wlh tallahi a warwaresa"
Ameeenatou dinma data kasa motsi sbd tsananin shock da baqin ciki tareda tashin hankali me tsanani dago jajayen Idanuwanta ta Kalli Dad dinta da Idanuwansa suka kada sukai jajir sbd tabbas Mam ya shammacesa ya bullo masa a hanya mafi kaifi garesa sbd 'yarsa itace kaifinda kadai yake iya hudasa,
Aure masa 'ya da sukai tabbas sun masa mummunan shammata tareda kutsen da ya tarwatsa zuciyarsa,
A binciken dayake Yi na asibitin datai zama an tabbatar masa da akwai baturen da yayi Aiki a asibitin na Dan lokaci Amma ankasa samun wanda zai fada sunansa,
Tabbas Arfat koma waye ubansa to jinin Tarawa ne sbd komai nasa a bayyane yake na jinin turawa dayake jikinsa,
Aleena ce wadda Arfat yake kama da ita sai yau Yana ganinta komai ya bayyanar masa ya gane fuskarta ce yake Gani a fuskan Arfat
Me hakan ke nufi??
Badai Jamaal ne mahaifin Arfat dinsu ba??
Mam yasan da hakan kuwa??
Idan wanna tinanin da abinda yake Gani gaskiya ne ba Ameeenatou ce kadai a hadarin ba Arfat ne,
Daga lokacinda Mam yasan yanada jininsa dayake yawo da Rai a gidan Nan komai yazama babba,
Barin Mam yasan ya hada jinin gasken Dani to tabbas burinsa girmama da karfafa zaiyi da komai zai iya lalacewa kowa.
Duk rintsi duk wuya Shima bazai yadda da auren Nan ba sbd Tako Ina Babu alkhairi a cikinsa fitinar shekaru ce zata qara habbakuwa ta girmama Kuma a yanzu babu wanda ya isa ya basa tsoro ko barazana sbd yarsa da jikarsa a hannunsa suke,
Shine uban daya haifi yarsa Dan haka Babu wanda zaiyi auren manufa ko jari da ita.
Kai tsaye ta Bude bakinta tana kallan Dad dinta ta murya a shaqe tace
"Dad bana buqatan auren kowa a kaina yanzu Dan haka Nima Nan aminta da aurenba a warwaresa sbd Babu buqatan auren da Babu wanda yakeso Kuma anyi ne Dan Neman mafita mafitan ta samu so I am out."
Miqewa tayi tabar gurin tabi ta gefen kujeran dayake zaune ta wuce iskan qamshinta y shiga hancinsa ya shaqa a natse tareda lumshe Ido Dan shi zancentama babu gurin shugarsa kwata kwata a kunnensa
Siddeeq ma daya San da hakan Satan kallan Jamaal din yayi Yana Dan shafa kansa,
Tinda sai sun sauke nauyin dayake zuciyarsu kowa yasan da auren angama me wuyar aminta da auren ko rashinta raayi ne na kowa wannan.
Dad Omar ma dagowa yayi ya Kalli Jamaal kafin ya Maida kallansa kan Mam Dake zaune a natse Yana jiran abinda zai fada din ya mayar da bayansa a hankali ya jingina tareda sauke numfashi me zafi ya Bude Baki Kai tsaye Babu batawa Kai lokaci yace
"A matsayina na mahaifin Ameeenatou ban aminta da aurenta ba Dan haka Ina buqatan takardanta batareda an sake tada zancen Nan ba na kashesa a yanzu Kuma anan."
Yana kaiwa karshe Shima miqewa yayi yabar palon kiejinsa n tsananin nauyi ciwon zuciyarsa na Neman tashi.
Da sauri Mum Nur ta miqe ta bisa tana kama hannunsa daya.
Babbah ma dayaji Wani nauyin dayake kirjinsa ya Dan ragu sbd abinda Omar ya fada din sauke ajiyan zuciya yayi Yana barin palon Shima.
Jamaal ma miqewa yayi ya fice riqesa Mum dinsa da duk hankalinta ya fara tashi ta shiga damuwa sosai sbd batason auren ya rabu duk wuya.
Siddeeq ma bayan uban gidansa yabi bayajin komai gameda rashin karban auren da Akai sbd yasan waye JAMAAL.
#MAMUH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
111
*_HONEEY DROPS_*
Albishir! Albishir! Albishirrrr!!!
Kin gaji da wula’kancin miji, ke ke nan kullum hantara da kyara , an hana miki rawar gaban hantsi a gidan aurenki, shin ko baki San gabad’aya dadin aure ba?. Hajiyata idan kina da kyau ki ‘kara da wanka, ke ke nan kullum babu wani sauyin dandano kullum zuwa kike wajen oga yadda kike, haba mana ba darajarki ba ne, mace ai ‘yar gyara ce, a d’in ga yi ana cleansing ana kuma spicing other room affairs. Sannan a gyara boobs d’in nan su cika su yi ma sha Allah a bar barinsu kamar guga, yanzu mace figure 8 bata burgeki ki ga ko ina ma sha Allah ga na Oyoyoo ga na bye bye, kina da HONEYDROPS me ya kai ki shaawar wata bayan kema tsaf zaki koma haka. To gyara ki ji ni da kyau HONEYDROPS wannan shahararren kamfanin na Aphrodisiac ma’ana kayan mata sun shirya tsaf don kawo muku zafafan kayan gyara wanda zaki mallake oga tsaf tsananin dadinki da niimarki, kayanmu aiki suke kamar yankan wu’ka kuma babu boka ba Malam, tsananin sanin makamar aiki ne kawai. Kayanmu na saka oga kyautar dole, muna soyayya da kulawar dole, suna birkita lissafin kishiya don dole ta ha’kura ta zama borar coz yan ajin HONEYDROPS a kullum sune Mowa, Muna…Muna… Muna…Muna fitattun kayan da ba su da na biyu kamar su
Infection flusher big 5k, small 3k
Breast firming sabaya 4k
Breast enlargement and hips sabaya 4k
Echoes of forever 3k
Her royal highness 2500
Milky vjay cake 3500
Ever bond 3k
Eternal flame 2k
Love nectar 2k
Cleanser pro 2500
Endless seduction 1500
Intensive love 1500
Swan 3k
Mowa’s secret 4k
Sugar queen 7k
Cloud9 4k
Sweet16 tightening gel 4k da sauransu. Muna da gumba kala-kala, tsumi kala-kala, muna dahuwar kaza, nama, tantabara, Ciccibi da sauransu. Muna da branches a garin Sokoto da Kano, sannan muna aike ko wani gari kowacce ‘kasa cikin amincin Allah, muna maraba da masu siyan daidai ko sari. Za a iya tuntubarmu ta lambobi kamar haka
08167888934 ko
07026039714.
Ki yi ‘ko’karin ki tuntubemu don tabbas kukan damuwarki ta qare. Zaki iya tuntubarmu ta Instagram link dinmu kamar haka
https://www.instagram.com/honeydrops013?igsh=MW5saThrY3N0Z2Zjag%3D%3D&utm_source=qr
************
Suna isa gida Jamaal ko kallan Dad dinsa baiyiba ya wuce sama Yana kokarin hadiyewa da Danne tsananin bacin Rai da zafin dayake Ciki sbd kansa da zuciyarsa kaman zasu kama da wuta,
Yayi controlin kansa ne acan tareda dannewa ya boye dan baya bari ana gane yanayin da zuciyarsa take Ciki a a cikinsa jininsa quna yakeyi kaman zai kama da wuta.
Idanuwansa kadai zaka kalla kasan masifaffen yanayin dayake Ciki Kuma siddeeq da Mum dinsa ne kadai suke gane hakan Dan haka Suna fitowa gidan kallo daya siddeeq yayi masa yasha jinin jikinsa,hakama Mum dinsa kallansa tayi tasan tafarasa zuciyarsa keyi.
Dad din magana zaiyi Mum tayi saurin Shan gabansa tareda dagowa ta kallesa da Blue Idanuwanta Cikin mamaki da jikinta dayayi sanyi sbd kunya da baqin Cikin abinda yayiwa dansa tace
"Please Mam,Enough of All ths pls,
JAMAAL bazai iya magana a yanzu ba kasani sedai idan hayaniya kakeson kuyi wanda kasan baka kyauta ba,
Koda zaka fadawa Omar auren at least sai kayi ta Wani hanyar a natse Cikin girmama juna da zancen Amma ji yanda kayi,
Shin daman kanason lalata auren ne ko me?sbd wannan abin da kayi shine shine zai lalata auren koma nace ya lalata coz duka jdens Babu wanda ya amsa auren, Omar kansa yace Bai yadda ba dole a raba auren,hakan kakeso right??
Kallanta yayi Yana mamakin yanda take daga muryanta ayau sbd 'danta,
Murmushi ya sake Yana kallan time a agogon diamond din dayake hannunsa kafin ya dago yace
"Calm down Aleena,
Auren Jamaal da AM tamkar rubutu ne akan dutse baya goguwa,
Nasan waye 'dana sbd jinane yake yawo a jikinsa,
Idan Muna son Abu ko duniya ta hade bama sauyawa musamman idan akace ya shiga hannunmu to zancen Kuma ai qararre ne,
Jamaal zai iya da Omar sbd bazai taba sakin wannan auren ba sedai duk me mutuwa ya Dade Bai mutu ba aure Kam ba rabuwa."
Yana gama fadar hakan ya juya yabar palon ya fice zuwa gidansa Dan su Mum Atee tini suka wuce gidan daman Basu shigo Nan din ba sbd tasan zaayi hayaniya a tsakanin uwa da uba da Kuma 'dansu.
Siddeeq dayake gefe tsaye Shima Idanuwansa sun Dan sauya kansa yayi nauyi tam Amma yasan Babu me tinkarar Jamaal a yanzu Dan haka ya raka Mum har bedroom dinta yayi mata Saida safe Shima ya sauko ya nufi part dinsa Yana waya akan tabbas tabbas dole su tsananta binciken inda Sister Ashley take sbd itace kadai zata iya dawo musu da AM din daidai akan Son dataiwa Jamaal din asibitin wanda a zahirance bawai Haroon ne takeso ba lokacin Idanuwanta kadai zaka kalla kasan wanda yake gabanta take so har zuciya Koda shine Haroon Koda ba shine ba.
****Itama lokacinda ta baro palon ta hawo sama ta shige bedroom dinta ta rufo tsayawa tayi tsakiyar dakin tareda Jin Wani Abu me tsananin nauyi ya Danne kirjinta Yana mata radadin gaske take Kuka me Ciwo ya taho mata ta dannesa tareda Hanasa fitowa hannuwanta ma Dan rawa sbd bazata yadda tayiwa auren da ko karbansa bataiba Kuka,
Bazataiwa kowa Kuka ba sbd bazata taba auren 'dan uwan Haroon ba,
Haroon dinta kadai takeso batason Dan uwansa tinda Haroon ya tafi ta hakura da kowa.
Babbah Bai karba aurenba hakama Dad dinta tasan Babu me sakata dole sbd har abada bazasu taba hada zuria da Mam seelah ba da lameenu Seelah sbd sune sukai sanadin rasuwan mahaifiyarta,
Me zatayi a Cikin zuriarsu?
Da Haroon Yana Raye tasani zasu shiga tsaka me tsananin wuya sbd sunawa juna son da bazasu iya rayuwa ba tare ba idan har Suna Raye Amma Kuma bazata iya zama da wanda take ganin mahaifinsa ne sanadin rasuwar mamanta duk da baa sanar da ita asalin gaskiyar tayaya suka zama sanadin.
Kukan take dannewa Amma Saida hawaye masu radadi duka gangaro mata sbd Bata taba Saka ran aure a gabanta ba yanzu,
Duka masu sonta da masu son hada auren kudi da ita da yayansu Babu wanda yai mata shiyasa Bata taba Saka ran auren a yanzu ba sbd duka duka yaushe ta samu kanta ta nutsu a rayuwar gabanta da zata fara maganar auren Amma a yanzu katsam ace da auren Wani a kanta tsawon shekara hudu koma biyar,bazata iya ba Koda kowa ya amsa auren wallhi ita batasonsa bazata karba ba.
Dad dinta kuwa a tsakar dare ciwok zuciyarsa ya tashi gadan gadan da gaske Amma ya Hana a bari kowa ya sani sbd bayason zancen ya fita Mam yasan yai nasara akansa sbd wannan auren yayi masa tsanani Ciwo da radadin da Babu wanda zai gane me yake ji,
Mam ya samu yanda yakeso,
JAMAAL kuwa ya Rusa yardar dayake masa tareda quntata masa sosai daya boye masa hakan har sai yaushe zai sanar dashi kenan da Mam Bai fada ba duk da Mam din ya fada ne da wata manufa.
Hankalin Mum Nur tashi yayi dole ta kira wayar uncle Ahmed ta sanar dashi ya taso ya sauko samansu ya nufi na Omar din ya haye tareda AM da itama mum Nur ta kirata.
Riqe hannuwan Dad dinta tayi tana tsiyayo hawayenta datake ta dannewa tinda abin yafaru ko zata ji sanyi itama tace
"Dad kada ka Damar da kanka Ciwo ya sameka please,
Bazan taba karban wannan aurenba Nima,
Bazan taba son auren ba dama me auren,
Haroon kawai naso Kuma nakeso Kuma zanci gaba da so Kuma ya Riga ya tafiyarsa Dan haka bazan taba aure a Cikin SEELAHs ba,Dan haka Dad pls karka bari Ciwo ya sameka akan hakan....""kukan datake riqewa ne ta fashe dashi zuciyarta haka kawai take mata Ciwo da radadin data rasa na menene.
Dad din da zuciyarsa Ciwo take masa sosai ya Bude Idanuwansa da sukai jajir ya zuba mata sbd shi kadai yasan auren Nan me yake nufi,
Jamaal yayi masa laifi me girma Kuma ya karya zuciyarsa Amma duk da hakan a Cikin tsananin so da kaunar dayake masa Babu wanda ya ragu sbd a jininsu take shida Jamaal din sedai Kuma duk son dayake masa bazai taba barin wannan auren ba bare karbansa dole a warwaresa sbd a yanzu ne ma yarsa da 'danta suke Cikin hadari me girman gaske sbd Arfat da Bai gama tabbatarda jinin Mam dinne ba Kuma koya tabbatar bazai taba barin kowama ya sake kokarin sani ko Neman mahaifin Arfat ba bare sanin gaskiyar Dan bazai taba barin Susan ma Arfat ba har gwara Jamaal din ya gansa Amma Mam dai Kam bazai taba ganin Arfat ba inshallah zai nesantasa da duk inda zai gansa.
Amma kafin Nan ma auren Nan Bai yadda ba Kuma bazai taba yadda ba dole a sakar masa 'yarsa Dan har abada a yanzu bayajin zai iya hada zuria dasu Mam
A baya ya aminta da auren AM din da Haroon dinne sbd tana tsananin sonsa da Kuma Jamaal ma dayayi alkawari kala kala Kuma da tinanin zasuyi nesa da mahaifinsu ne Amma a yanzu ko shi Mam bazai yadda bayan auren 'dan sa yayi nesa dashi Dan haka Shikuma bazai jefa 'yarsa da jikansa a tsakanin zakunan da junansu ma Basu bari Dan kuwa Yana ganin ciwon lameenu yasan uban aikin ne yake Aiki akansa.
Uncle Ahmed ma da Mum Nur Dake gurin abinda suka sake fada kenan kada ya Saka damuwan auren da Babu wanda ya karbesa Kuma ai 'yarsu ce baa aure dole,dole zaa sakar musu ita tin kafin ma kowa yasan da auren.
Ajiyan zuciya Dad din yayi a Dan wahalce sbd yasan waye Mam Dan tin Suna zannuwan goyon iyayensu suke