Showing 138001 words to 141000 words out of 261814 words
sanyi sosai tareda rashin kuzari ta Bude Baki tace
"Ameenatou tanason sister Ashley,tanason Haro.....
Kasa qarasawa tayi tinawa da sunan Daya fada mata a cikin kunnenta lokacinda yake cikin yimata Wani irin shafa a wuta zuwa kirjinta yakai bakinsa kan fatar kunnenta Saida ya sake mata wani fitinanniyar numfashinsa me dumi ya kashe duka jikinta kafin ya Bude Baki lips dinsa suna shafan fatar kunnenta ya ambaci
"JAMAAL,not Haroon,
JAMAAL"
Idanuwanta da sukai ja ta Bude a lokacinda kalman sunan ya shiga kunnuwanta da Kuma yanda Jamaal din ya ambaci sunan tareda numfashinsa dayake dukanta Yana tada tsikar jikinsu gaba Daya.
Ahankali cikin sanyi da rashin sani ta furta sunan Daya fada mata din Wanda ya Saka sister Ashley Dan juyowa ta kalleta sbd yanda ta ambaci JAMAAL din ko ita Saida taji tausayinta Dan tasan Ameenatou dinta idan ta warke za'a iya yin rigima sosai akan Aminta da auren 'dan uwan Haroon ba Haroon dinba idanma angama tashin hankalin amsar zancen rasuwarsa kenan.
Shafa kanta ta ringa yi tana mata Yan maganganun yanda tayi kewan mijinta Dan yanda itama tayi kewanta tace ita kadai take gani yanzu taji sanyi duk da Basu hada komaiba Amma itace kadai sanyin idaniyarta yanzu.
Da dare zazzabin yaso sake tasowa Dan haka abinci ta Bata tareda magani ta kwantar da ita take bacci yazo ta rufeta ta koma dakinsu.
Da asuba Koda yazo still dai akwai zazzabin haka ta sake shiryata tareda koyarda iya yin sallah kaman yanda Dr JEEY din yakeyi mata kuma ya saka a ringa mata din.
Da safen bayan ta gama mata komai ta sake komawa bacci gida ta tafi se Rana sosai ta dawo tazo mata da siyayyar fruits da abubuwan amfaninta duk da kusan komai akwai Dan Dr JEEY yayi siyayyar da Bata qarasa qarewa ba Amma kudin Da aka Saka mata ne masu yawa sosai ya Sakata sake siyayyar.
Haka taci gaba da kulawa da ita har dare ta tafi itama ta kwanta.
Kwana uku sukai suna jinya sosai kafin zazzabin ya sake Ameenatou ta dawo daidai Dan kuwa a kwanaki ukun Nan batada kuzari ko iya Rigiman ko kadan Se sunan JAMAAL HAROON data hada yanzu take kira.
Dr JEEY din Bai samu Daman Kiransu ba sai Siddeeq ne dayake Kiransu kusan so hudu ko biyar a wuni yanajin lafiyar Ameenatou din kafin JAMAAL din ya Samu kansa daga tashin hankalin dayake ciki na Mum dinsa da Rabin jikinta ya shanye gaba Daya bayan mummunan jijjigan data samu Wanda ya hada da zucuyarta data kasa dauka taketa aman jini.
Abinda ya gigitasa ya rikitar da kansa bayan wannan mummunan tashin hankalin na munin ciwon shine kasancewan Dad dinsa Baya Nigeria Dan haka komai zai iya yiyuwa garesa duk da yasan Yana Greece tareda Siddeeq Amma yasan zai iya zuwa yayi Wani abin y koma batareda kowa y saniba,
Dan hakane tinda ya Isa ya shiga asibitinsu Yana asibitin Bai fitoba Dan shine ya karbi kusan case din sunata fama Wanda sai anyiwa Mum din aikin zuciya Amma Kuma yanayinta ya Saka Hakan Abune da zaiyi wuya da hadari Dan haka yake cikin tsaka me wuya da gwagwarmayar ganin yanda zaayi aikin cikin chances masu kyau ba chance da suke dashi yanzu ba yayi qanqantar da hadarin yafi yawa.
******Satinsa Daya da tafiya tukuna ya Samu Dan sassaucin abinda yake ciki ya koma gida acan ne ya zauna ya huta tareda samun hadda baccin kusan awa biyu kafin ya tashi yayi wanka ya zauna cin abincin da ba wani iya cinsa zaiyi a dadin Rai ba tukuna ya dauko wayoyinsa ya kunna Dan kuwa ko Siddeeq Bai taba samunsa ba tin bayan zuwansa sai yau din.
Yana kunnawa numbern sister Ashley Dake layinsa na Nigeria ya fara dauka ya Saka kiranta Kai tsaye.
A lokacinda kiran ya shigo sister Ashley na tareda Ameenatou din tana mata gyaran farce tana ganin yanayin numbern zuciyarta ta Dan ayyana mata ko shine sbd numbern Siddeeq ta can din dayake Kiransu da ita tayi Savin Dan haka ajiye Neil cutter din hannunta tayi tareda daukan wayar cikin nutsuwa tayi receiving tareda Sanya handsfree tace
"Hello,Aslm alailkm"
Cikin muryansa me cikeda nutsuwa da kamewa ya amsa sallaman tareda doro tasa gaisuwan da tambayarta Yaya suke.
Ameenatou dake zaune dagowa tayi a hankali da kanta ya zubawa wayar hannun sister Ashley din idanuwanta da sukai haske sosai tana kalla.
Amsawa sister Ashley tayi tana cewa
"Lfyanmu kalau,AM ma gatanan lafiyanta kalau ba rigima sedai kullum seta ambaceka"
Shiru yayi tareda Dan kwantar da bayansa jikin kujeran dayake zaune kafin ya bude baki yace
"Akwai Wani ci gaba gameda rashin lafiyanta?
Me takeyi yanzu?
Kallanta sister Ashley tayi Taga yanda take kallan wayar Jin muryansa na fitowa a natse cikin sanyi.
"Zakiyi magana da JAMAAL Haroon??
Gyada Kai Ameenatou din tayi tana kallan wayar.
Matsar da wayar tayi zuwa gareta tace
"Kiyi magana"
Shiru tayi batace komaiba sai sanyi da jikinta yayi sosai da Jinsa sbd kewansa datai a bayyane take.
Cikin nutsuwa da kulawan datake bayyane sosai akanta taji yace
"AMEENATOU,
Ameenatou tana son ganin JAMAAL ko?
Zan dawo idan Mum taji sauki na taho dake,
Zaki taho right??
Gyada Kai tayi Wanda yaji Hakan Dan haka ya sauke ajiyan zuciya cikin kulawa yace
"Me Ameenatou takeso??
Kaman Yana kusa da ita ta dago ta sake kallan wayar kafin ta kalli Ashley ta dawo da kallanta kan wayar tana narkewa kaman zatai hawaye tace
"Ameenatou tanason JAMAAL Haroon"
Rintse idanuwansa yayi ahankali cikin Wani irin yanayi me nutsuwa kalman ta shigesa kafin ya Bude tareda sauke numfashi mara sauti da wata irin murya me sanyi yace
"JAMAAL zaizo gurin Ameenatou ba dadewa,
Zai tafi da Ameenatou"
Murmushin Jin dadi ta sake me sautin Daya sauka har cikin kunnensa ya sake lumshe ido Yana sauraronta.
Tambayarta yayi taci abinci tace eh,
Ya tambayeta taci chocolate Shima tace Eh,.
Sama sama ya ringa tambayarta tana amsawa cikin Jin dadi shikuwa jikinsa ne yake sake mutuwa harya gama wayar dasu tukuna sukai sallama bayan ya sake magana da sister Ashley din sosai akan yanayin jikin nata yaji Kuma Babu matsalan komai data taso Dan ya rubuta a file dinta ya dakatar da alluranta Dan haka aka Dena mata kwata kwata sai maganin Daya Dorata Akai,alluran Kuma an Barwa su nurse Fahat Wanda gaba Daya kusan yafi kowa hauka a asibitin Dan gabaki Daya JEEY din ya jujutasa haukansa ta gasken ce tuburan yake yinta shiyasa shi kullum a daure yake a gadonsa.
Suna gama wayar Ameenatou taketa murna tana Jin dadi JAMAAL din yace zai taho gurin Ameenatou.
Sister Ashley ma da Bata cikin farin ciki ko walwala kwata kwata ganin Ameenatou din nata farin ciki da murnan ya sakasata Jin itama sanyi harda murmushinta tana tayata farin ciki da murnan da ita kanta tayi kewan kulawansa akansu Dan tinda mijinta ya rasu ya dauke nauyin komai na rayuwarta Dan gidanta kansa Saida ya sauya mata sbd taimaka mata gurin rage radadin kewan mijin da kadaicin gidan datai rayuwa da mijin.
A can nasa bangaren tinda yayi wayar ma komai ya sake yi masa nauyi sbd zancenta na son Jamaal data fada wanda ya shiga zuciyarsa sosai gashi anan din abubuwan a daure suke Babu ranar tafiyansa a kusa sai anyi aikin mum dinsa zai iya barowa ya taho shiyasa ya matsu Siddeeq ya gama ya koma Nigeria duk da idan ya Tina Mam Baya Nigeria saiyiji sauki saukin barinta da yayi din acan.
****Tin daga ranar Babu ranar da Baya waya dasu Kuma yayi magana da ita duk tsananin zamansa busy kuwa Saiya kirasu din Ameenatou ke samun walwalan kyale sister Ashley da Rigiman a kirasa hakama Shima saiyayi magana da ita din yake samun nutsuwar ranar duk tushewan abubuwan kuwa.
Sabo da hakan ya Saka idan Bai Kiraba ta ringa rigima kenan tana Hana sister Ashley zaman lafiya har takai video call yake Kiransu Duk da baiso Hakan ba Dan duk yanda yakeson ganinsa ya Hana kansa yin video call dasu ne sbd zuciyarsa Dake son Raba tinaninsa,hakama itama yasan rigimarta ta son ganinsa zata qaru ne ta Hana sister Ashley zaman kalau.
Aikuwa Hakan ne ya faru Dan idan ya kira tana karban wayar daga sister Ashley Taga Babu fuskansa Akai ta ringa rigima kenan dole suka koma video call din kullum Wanda Hakan ke yaga zuciyarsa Amma Yana basarwa da dannewa Amma baya Wani dadewa duk rigimarta haka yake lallabawa ya kashe.
Hakan yasaka kullum sai anyi rigima da ita yanzu dan Babu Daman ayi wayar a kashe ta ringa rigima da fitina kenan harda su kuka sosai wasu lokutan wasu lokutan kuwa rigima ce sosai har sai ciwonta ya tashi ta rikice musu da kyar ake samu a shawo kanta ta saurara duk da baa san menene yake kawo hakan ba sister Ashley ce kadai tasan menene abinda yake kawo hakan amma babu ma abinda zai sakata fada ko barin ma a sani.
#MAMUH#
#AMEENATOU
#JAMAAL JEEY SEELAH
#HOT
#ROMANCE
#BESTLOVE
#SEELAHS
#JDENS
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
#ZafafaBiyar
86
*_AISHA's COLLECTIONs_*
Hajiyata Kinason kiyi kasuwanci amma bakida jari?
Ko kuma kinada jarin amma bakisan maiya kamata ki fara saidawa ba?
Tou hajiya nesa tazo kusa ga sauki yazo na kawo muku inda zaku samu kaya a cikin farashin sari,muna saida kaya kala-kala inda zaki samu a cikin sauqi da rahusa.Akwai varieties of women accessories ranging from Atamfa, Laces and shoes at both wholesale and retail..
Hajiya da kayan da kika sani da Wanda Baki saniba harma da Wanda Baki taba Gani ba na kayan alfarma da burgewa da asalin kyau na quality kizo karki bari ayi Babu ke,
ko kasuwaci ko sanyawa,ko ankon biki,lefen alfarma,kayan sallah..komaima namu inshallah na musamman ne da zakiji dadin kasancewa a cikin kasuwanci damu...
Join our group to see lot of our amazing products 👇
Location: LAGOS
We deliver nationwide
09013833502
https://chat.whatsapp.com/JRkPEIt0xVj2vuE8HAGRUL
************
Kwanaki nata Dan tafiya,yawan Rigiman datakeyi yanzu ya Saka take jawa kanta zazzabi suyita fama saita kwana biyu sister Ashley ta samu ta warke,
Sister Ashley tana sanar masa ko ciwon Kai Ameenatou din tayi Dan haka ya rage yawan Kiran da mugun shagawabatan dayake yi a wayar sbd bayason yawan ciwon Shima,
A nata bangaren kuwa rage yawan Kiran ya Saka ta qarasa rikicewa kullum sai anyi gama da ita ta koma kawai wata rigimammiya kullum sister Ashley cikin dawainiya da fama da ita take sai itama ta koma Abar tausayi sauran nurses kuwa duk sai suka ji basa kaunar Ameenatou din ko kulata basa iyawa kowa ya Barwa Ashley wahalarta duk da Daman Tim can itace me wahalar Amma dai idan rigimarta ta tashi kusan nurses na taruwa akanta.
Wannan rigimar tata tasaka lafiya take Neman gagararta yau lafiya gobe ciwo take tafara rama haka kawai tana Wani irin haske kaman zata koma jinjira,
Ciwo me wahala takeyi sbd sosai take laushi idan ya tashi ko motsin kirki Bata iyawa ko tayar da ita sai sister Ashley tayi,
Itama sister Ashley din yanayi na zuciya na rashin mijinta da rigimar Ameenatou din datai yawa tareda wahalar ya Sakata itama layin Ameenatou din zazzabi takeyi sosai da rashin lafiyan Dan haka suka koma dukkaninsu sai ahankali.
JAMAAL ma dole ya sake rage Kiransu sosai tinda Kiran ke Saka Ameenatou din rigima da tashin ciwon...
Wannan yasa abubuwan suka fara cabe musu Amma duk da Hakan karfin hali sister Ashley keyi sosai tana kulawa da Ameenatou Dan tafita jin jikinta sosai hakama batason asan dukkaninsu Basu da lafiya sosai irin Hakan Dan zaa iya Bata Hutu ita ace saita warke to Kuma a yanzu da Ameenatou batada lafiyan batajin tafiyanta shine maslaharsu Dan kuwa qarasa rikicewa Ameenatou din zatai.
A nasa bangaren kuwa Shima abubuwan sun tsananta Dan haka Shima suka jisa shiru ba labari kwana biyu,
Ana cikin Hakan jikin Ameenatou yaqi sauki Tako ina Sam Dan haka dole likitoci suka Maida hankali sosai akanta sbd patient din Dr JEEY ce kowa yasan tanada mahimmanci a gurinsa a asibitin dan duk yanda yakeda basarwa da kamewa duka an fahimci mahimmancinta a gurinsa Dan Yanda yake dubata daban da sauran patients hakama suna lure da kyautatawan dayake wa sister Ashley akan yanda take kulawa da ita batareda sunsan asalin alaqarsa da ita ba har yanzu din.
********Tashin farko abinda Dr Zakeer ya samu a results nata shine ya sakasa Zare farin glasses dinsa ya Ciro handkerchief dinsa ya goge glass din da kyau a natse ya sake mayarwa fuskansa ya Saka tareda sake daukan takardun ya Bude da kyau Yana sake karantawa.
Abinda ya Gani farko ya sake Gani Wani zufa na tsatsafowa daga goshinsa har tafin hannuwansa.
Baya tayi da kujeran dayake Kai ta office dinsa ya miqe tareda daukan sauran takardun ya nufi kofa ya fice zuwa office din Dr Ibrahim Yana sake dubawa da kyau Dan kada yaje aga ba Hakan bane ya zamana ya hadawa kansa masifa.
Harya Isa office din Abu Daya yake Gani ba gizo bane.
Yana zuwa office din cikin sa'a dr Charles ma Yana office din suna tattauna maganar Nurse Fahat da familynsa ke rokon a tsananta musu Neman lafiyansa,
Zufansa ya share ya iso gurinsa tareda ajiye takardun hannunsa kan table din gabansu batareda ya sake gaisawa dasu din ba bayan wadda sukai da safe da suka Hadu.
Kallan takardun sukai a tare kafin Dr Ibrahim ya dawo da kallansa kan Dr Zakeer din
Shikuwa Dr Charles takardun yake kalla har lokacin Yana Kai hannu ya dauka Yana cewa
"Menene?
Results din waye?"
Bude takardun yakeyi Yana fara karantawa.
Yana gamawa ya dago ya Kalli Dr Ibrahim Dake jiran Jin Menene kafin ya dawo da kallansa kan Dr Zakeer cikeda mamaki me girma yace
"pregna....""
Katsesa Dr Zakeer yayi da qarasa masa da cewa
"Yes,patient 6, Ameenatou Omar"
Dr Ibrahim Dake Neman shiga duhu akan rashin ganewa ne ya karbi takardun ya fara karantawa a bayyane.
Ajiye takardun yayi tareda dagowa ya Kalli Dr Zakeer cikin son Bude zancen sa kyau kan kowa ya sake yace
"Ciki ne a jikin patient dinmu?
A wannan asibitin?
A cikin asibitinmu?
Cikin haihuwa fa,
Cikin haihuwan 'dan mutum fa??ko dai na aljanu ne??
Tayaya zaa samu wannan mummunan masifar Rana tsaka a asibitin Nan??
Kun San me Hakan ke nufi??
Kunsan license dinmu ne gabaki dayanmu ya hau Wani mummunan siradi kuwa na rayuwa da mutuwa?
Kaiii innalillahi."
Dr Zakeer ma dayake cikin mummunan tashin hankalin share zufansa yayi sbd sanin Suma makomarsu irin ta dr Dee ce kenan,
Tayaya zaa samu patient dinsu da ciki?
Tayaya zata samu ciki a qarqashin kulawansu?
Me zasu fadawa Wainda suka kawota?
Me zasu fuskanta daga lokacinda zancen cikin ya fita Dan hukun Hakan me girma ne tinda mahaukata ne basa iya gane Wanda yayi musu Cikin sbd tabbas tabbas dole daga cikin ma'aikatan asibitin ne dole aka samu Wanda yake lalata patient tinda angansu Basu da hankali shiyasa ake hukunci me tsananin da zai lalata career din aikin mutum gaba Daya to su yanzu da baa San ta inda zaa San ina wannan masifar ta bullo ba.
Dr Charles daya fisu shiga shock kallan result din yayi Yana cewa
"Menene abin tsayawa fargaba da tashin hankali har Wani yasan da cikin bayan a cire mata shi asiri rufe Babu sanin kowa,
Kokuma tsayawa zamuyi tinanin abin yi har nurse dinta tasan da cikin zancen ya fita,
Kuna sane da Dr JEEY SEELAH ne ya Saka aka dauke Dr Dee daga Nan daukewan wulaqanci data Saka sa kashe kansa bayan sunansa ya gama Baci akan qwayoyin da aka samu a tareda gawarsa,
Dr JEEY na sanin maganar anyiwa wannan patient din ciki a asibitin Nan zai tabbatarda careers na mutane da dama a cikinmu sun lalace,
Ku kalla nurse Fahat Wanda bibiyan yarinyar kawai ya gwada yi Amma Ina yake yanzu???
Akwai Wanda ya Isa yayi magana akan Hakan??
Dukkaninmu munsan lafiya kalau Fahat yake Amma dare daya haukan ta samesa dole muka bi yarima muna Shan kida bare yanzu ace ciki,
Ciki na haihuwa fa??
Raping dinta fa kenan akeyi da alama ba so Daya ba akwai Wanda yake Kwanciya da ita a cikin ma'aikatanmu ko likitoci ma ko nurses ko clearners koma ward attendence duk zai iya faruwa ace Wani daga cikinmu ne."
Shiru dukkaninsu sukai kowa na shiga nazari Dan sune manyan asibitin sai md Wanda Shima dole a sanar dashi asan mafita Dan kuwa daga kan likitocinsu har asibitin gabaki dayanta zaa iya sokesu.
Dr Charles ne ya buqaci abari ya sake aunata da kansa ya Gani Dan su sake tabbatarwa kafin su Sako md acikin zancen tukuna,
Naam sukai da Hakan Dan haka aka bari aga me sakamakon ze bayar.
Babu Bata lokaci Dr Charles ya koma office dinsa yayi abinda zaiyi kafin daga baya ya nufi dakin Ameenatou din.
Koda ya Isa sister Ashley na hanyar zuwa dakin itama Dan haka cikin girmamawa ta gaidasa suna qarasawa tare Yana tambayarta jikin Ameenatou din ta amsa masa da ba laifi tana samun lafiya zazzabi ne kadai yanzu yake Sakata gaba ko ya tafi Saiya dawo.
Dan juyowa yayi ya Kalli sister Ashley din wadda itama tayi wani irin zuru zuru da ita
Yayi mata kallan mintina kafin ya dauke Kai suna shiga dakin tareda wata sister fareeda data biyo Dr din.
Ameenatou na kwance lafe a gadonta tana Jin yunwa Kuma Bata son komai bayan fruits Dan yanzu su kadai takeso take Kuma ci sosai wanda itama sister Ashley sbd yawan siyansu da yanda Ameenatou Kesha yasa dole suka zama tata cimar itama Dan haka tare suke Sha ba sauki.
Har Dr ya iso gabanta ya tsaya Yana mata kallan tsaf Bata dago ta kallesa ba Danma ciwo ya Sakata laushi sosai da yanzu tafara rigimar kada ya matso inda take.
Tambayoyi yakewa sister Ashley akan yanayin jikin nata da yanda take Ji harma da tambayoyin da suka Saka sister Ashley kallansa cikin mamaki da gabanta daya Dan Fadi.
Bata amsa tambayar ba Sbd sister fareeda Dake tsaye tana kallansu,
Shima bayason fareedan ta fahimci wani abin Dan Haka ya kalleta tareda turata Wani aikin Dan bazasu kowa ya San komaiba bayan sister Ashley wadda itama Dan ta zama dole ne.
Sister fareeda n wucewa ya juyo y Kalli Ashley din ya sake maimaita Maya tambayarsa.
"When last did she see her period???
Sanyi jikin sister Ashley ke Neman yi sbd faduwan da gabanta ke tsananta yi,
A Sanyaye tace
"If na Tina daidai last month bataiba Amma na bayan na manta na last month din dai bataiba shi na Tina daidai,
Dr akwai Wani abin ne daya Saka wannan tambayar??
Shiru yayi Yana sake kallan Ameenatou din Baya buqatan qarin bayanin