Showing 51001 words to 54000 words out of 261814 words
Kuma zuciyarta tafi sonsa idan Yana daga nesa da ita ne.
Magana Jafar yayi mata a hankali wadda ta Sakata Dan fitowa kadan batareda ta kallesaba ta gaidasa cikin nutsuwa batareda tayi tinanin Yana Jin hausar ba.
Shi dariya ma ta basa Dan haka Saida ya saki Dan murmushi kadan kafin ya amsa Yana kallan Hafiz yace ya tafi da ita gida kawai yabar aikinsa zuwa gobe.
Ita kanta kaman tana jiran ya fada Hakan Dan haka ta wuce gaba batareda ta waiwayoba Hafiz kuwa wanke hannuwansa yayi tareda daukan Jakarta data barmasa yayiwa Haroon din godiya yabi bayanta Yana Bude mata umbrella data manta Yana cewa
"Salon ta ishesu da kukan zazzabi zai kashewa Babbah yar budewa ne yasakata biyosa cikin wanna uwar ranar gashi duk ta ruda masa aiki"
Shiru tayi masa Saida sukai Nisa ta waiwayo tana sake kallan Haroon Dake tsaye har lokacin Yana magana akan abinda sukazo dubawa.
Tin a hanya bakinta ya mutu har suka Isa gida Bata wani ishesa da magana ba Dan haka suna shiga gidan wanka kawai tayi taci abinci tafara kokarin kwantawa yasata gaba suka wuce islamiya Badan tayi niyar zuwa lolacinba Amma sbd tanason ringa biyawa ta gurinsa site hakanan ta shirya suke tafi.
Su kansu malaman sunyi mamakin zuwanta batareda latti ba yau din Amma dai dayake batajin hayaniyar Babu Wanda ya takurata da tambaya haka ta wuni makarantar ba hayaniya har suka tashi ta dawo gida tareda Yaya Abdul.
Washe gari ma haka suka biya site ya qarasa aikinsa ta zauna tana bin duk inda Haroon yayi da idanuwanta masu haske da kyau tana Jin kaman tace ya zauna ya Dena shiga rana duk da duk motsinsa biye ake dashi da umbrella sbd Rana karta tabasa.
Tinda take zuwa Bata sake bari ya ganta ba harta gama binsa da kallo tana murmushin su koma gida.
Abinda Bata saniba tinda kwanakin suka fara ja Yana sane da duk zuwanta da tafiyarta kuma ahankali ahankali ya fahimci sbd shine yake zuwan ta dauka bature ne shi da gasken.
Da farko lamarin mamaki da dariya yake basa sbd Bai taba Ganin inda asalin gata da tattalin 'yaya yake ba sai akanta hakama baitaba ganin kauna da kulawa me tsananin gaske ba da yanne kewa kanwa irin Wanda ahankali yaga anaiwa yarinyar.
Tinda tafara zuwa Bata taba tsallaken zuwa ba Saida exams dinsu ta karato sosai suna farawa shikenan ta Dena zuwa kwata kwata sbd karatu sosai da Yaya Abdul ya sakota gaba dashi
Shi kansa Hafiz sosai yake Bata lokacinsa suyi karatun exams din tare.
Barin zuwanta ya Saka Haroon tambayar Hafiz ko lafiyanta kalau ya sanar masa axams takeyi Kuma dai Bata jin dadi sosai sbd wahalan karatun.
A nata bangaren ahankali ta dawo hayyacinta akan zuwa ganinsa Dan haka Koda suka gama exam kwata kwata Dena zuwa tayi ga rashin lafiya sosai Daya kwantar da ita na kusan kwanaki Dan haka suketa fama da ita anata lallabawa da ita kaman kwai.
Shi kansa Haroon duk tsananin damuwa da quncin zuciyar dayake ciki Saida yazo har gida ya dubata Wanda Hakan ya Sakata Jin dadi sosai Suma su Babbah haka suka nuna masa Jin dadinsa sosai sbd Ameenatoun.
A nasa bangaren yanda ya samu iyayenta da karamci dakuma sake ganin irin so da tsananin gatan da ake nuna mata ya sakashi fara jinta a zuciyarsa sbd kallan datake masa lokuta da dama idan ta zuba masa kyawawan idanuwanta sai yakejin damuwar datake lullube da rayuwarsa kaman tana ragewa Dan haka ya Dan saki jiki da gidansu Ameenatou din musamman Hafiz dayake qarqashinsa.
A bangaren siddeeq kuwa komai na Haroon shine yake basa kulawa da tsaro yanda ya kamata Dan haka Koda yaga Haroon din yafara samun walwala da yar sakewa a cikin Iyalin Babbah sai Shima yaji ya samu nutsuwa da Hakan take Shima ya sake suka fara samun sabo da mutunci dasu din.
A bangare Daya rayuwar Haroon din na cikin matsanancin daci da damuwa tareda rashin farin ciki ko Daya sbd Dad dinsa da suka Saka ido sosai a lamarinsa hakama Babu alaman aikin Nan nasu zai samu karbuwa a inda zasu gabatar dashi Dan haka kowace dakika ta rayuwarsa cikin damuwa da 'daci me tsanani take Dan haka ciwonsa ma keyin gaba gaba koyaushe batareda sanin kowaba sai siddeeq Wanda ko numfashinsa Baya boyewa JEEY.
Shigarsa cikin Iyalin Babbah ya Saka Dan haske da farin ciki shigowa rayuwarsa a duk lokacinda yake cikinsu Dan takai kusan abinci ma wasu lokutan a gidan yake ci na dadah.
Ameenatou Kam zuwa yanzu tagama shiga zuciyarsa fiyeda yanda yake tinani duk da shagwabarta yayi yawa Amma shi Hakan ne ya kashe zuciyarsa ta mutu gabaki Daya akanta ita Kuma a nata bangaren a yanzu dayake tareda su sai ta aje maganan son datake masa ta jefasu a layinsu Hafiz duk da haryanxu kallansa takeyi a Wanda yafi kowa kyau da tsari Bata taba Ganin kamansa ba.
******Su Dad sun dukafa ba ji ba Gani sai barin kudi sukeyi hankali tashe gurin Neman Maryama Dan kuwa suna gap da zubewa gaba Daya Dan haka suka fice hayyacinsu.
BB ma sun haukace Baki ba ganin sunata tsananta bincike da zufafasa akan Maryama wadda daga karshe suka gano kauyensu.
Bayan barin dukiya me yawan gaske su BB Saida suka gano Maryama saigasu da ita har cikin Lagos sedai ko kwana batai a lagos ba Su Mam suka taho har inda su BB suka boyeta da daddare.
Mam ne ya fara tsayuwa akanta kafin Lameenu ya shigo bayan ya kashe wayarsa gabaki Daya daga wayar dayayi ya tsaya Shima yayi mata kallo Daya Yana komawa ya zauna kujeran alfarma dasu BB suka kawo musu na zama.
Shima Mam zama yayi Yana kallan BB batareda Bata lokaci ba Dan baida time na batawan yace
"Tatso mana bayanin komai daga bakinta banason rasa kalma ko Daya komai nakeson Jin a yanda yake dinsa."
Qwayar datake bakin BB ya qarasa hadiyewa idanuwansa na sake rinewa jajir ya miqawa yaronsa Daya hannu ya Saka masa wata mahaukaciyar wuqa da shape dinta kadai abin tsoro ne.
Nufar Maryama din da idanuwanta suke a daure yayi tareda tsayuwa a kanta ya kamo kanta ya Bude idanuwanta ya Saka mata wuqar gaban idanuwanta da sukasha mugun dauri cikin muryansa me kauri da karajin rashin Imani yace
"Ki kalla Menene a gaban idanunki"
Kafin ma taja numfashin tsoro da tashin hankali bare taga wainda ke zaune a gurin ya mayar mata da daurin idanuwan ya rufe.
Mayar da kaifin wuqar yayi akan jijiyan maqoshin wuyanya Kai tsaye yace
"Meya faru a Daren ranar da matar sir Omar ya ta rasu?
Akwai ciki a jikinta koda ranar tazo?
Wata nawa?
Ta haihu?
Me ya Haifa?
Ina abinda ta Haifa yake?
Waye taredaku a Daren ranar?
Ya Akai kika tsira a Daren????
Cikakken bayani zakiyi sbd rashin kalma Daya daidai take da ficewan ruhinki daga gangar jikinki."
Wasu Hawaye masu tsananin zafi ne suka gangaro daga idanuwanta dasuke a rufe zuciyarta na wani irin rawar tashin hankali da tsoro Dan kuwa tasan shikenan nata karshen yazo abinda taketa yiwa gudu sbd tasan Hakan zai iya faruwa wata ran sbd akwai tabbacin asan data tsira.
Sake daga wuyanta BB yayi Yana qarawa wuqar seti har seda ta Dan fasa wuyan jini ya Dan fito.
Zufa take fitarwa sosai kirjinta na wani irin mugun bugawar da kusan Suma su mam din kirjin nasu harbawa yakeyi sosai Dan kuwa a Baya duk zance ne sukeyi Basu tabbatarba sai yau din zasu tabbatarda masifar Dake gabansu tana can tana yawo a duniya batareda sunsan a Ina ba.
Lameenu kuwa har wani zufa yake tsiyayowa hannuwansa na rawa Da matsuwan Jin Abinda zata fadan,
Allah yasa Omar din Bai haihuba zance ne kawai,
Allah yasa suji abinda zai kawo karshen matsalar tasu idan ba Hakan ba akwai babbar matsala da kura a gaba.
##MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
34
Maryama gaba Daya ta cire tsammani daga rayuwa Dan haka cikin rawar murya da tashin hankalin da Bata taba Shiga ba ta fashe Da kuka zata fara rokonsu karsu kasheta BB ya sakar mata wani mugun marin bayan hannu Saida bakinta ya fashe Da jini sosai ya sake cakumo wuyanta Yana Dora wuqar kafin yace komai Baki na jini tace
"Koda ranar tazo tana daukeda tsohon ciki wata Tara......
Wani mummunan zufa da sarawan Kai tareda bugawan zuciya ne ya saukarwa Lameenu da Mam lokaci Daya,
Lameenu yayi saurin kallan Mam zuciyarsa na wani irin bugawa da karfi da tsalle sbd baitaba tinanin Jin Hakan ba,
Da gasken kenan dai Omar nada magajinsa,
Magajin dukiyar da baimasan Yaya zeyi da ita ba,
Gadon dukiyar tin suna samari suke dakonta cikin ransu,
Dukiyar da suka zama abinda su kansu basuyi tinanin zama ba ko a mafarki Amma daga karshe ace share fage ne kawai sukaiwa abinda Omar ze Haifa.
Mam kasa motsawa yayi bare juyawa ya kalla Lameenu sedai zuciyarsa kusan tafi ta Lameenun shiga mafi girman tashin hankali da firgici.
Shi kansa BB wani irin zufan tashin hankalin ne ya jiqasa Dan haka ya sake danna wuyanta Yana jiran sauran bayanan
Cikin rawar murya da ficewa hayyaci taci gaba da cewa
"Bata rasu ba a Daren sai bayan data haife cikin dayake jikinta,
Sir Omar yasan ta haihu sbd da kansa ma ya karbi abinda ta Haifa,
Oga Ahmed ma yasan ta haihu a daren...."
Kukanta karuwa yayi muryanta ya tsinkewa sbd tsoro numfashinta na Neman daukewa tsaban tashin hankali da tsoron wuqar Dake wuyanta tanajin kaifinta.
Lam da duka jikinsa ke rawa da zufa kasa hakuri yayi cikin zafi da matsuwa yace
"Me ta Haifa a Daren?
Waye Wanda kuke tareda shi a gidan wannan Daren?
Ina abinda aka haifa din yake?
Waye ya tafi dashi?
Wani sabon mari BB ya falla mata cikin rashin tausayi bare Imani Yana cewa
"Koro bayanin amsosin abinda aka tambayeki kafin na ratsa wuqar Nan cikin makoshinki"
Bakinta da duka jikinta na rikicewa da jijjiga Hawaye da majina duk sun cakude a fuskanta cikin matsanancin tsoron rayuwarta tace,
"Banda tabbacin abinda ta Haifa sbd a dare duka muna cikin tsoro da tashin hankali daga sir Omar Se oga Ahmed da 'yayan Hajiya Ameenatu din ne kadai suka San Menene aka Haifa tsakanin mace ko namiji...
A Daren yayanta yazo daga gombe gurinta Kuma shine ya tafi da babyn"
Wata sabuwar zufa ce ta tsiyayowa kowannensu Dan kuwa abin yazo a yanda basuyi tsammaninsa ba.
Sake danne wuyanta BB yayi tafara jero musu bayanin komai Daya bayan Daya har address din gidan Babbah dake gombe da yanda suka tsare da Kuma yanda Taga girman son dayake wa yar uwarsa da abinda ta Haifa din tabar masa.
Abu dayane ta boye shine cewan tasan mace ce aka Haifa sbd tsaban rufewa da shiga tashin hankali kwata kwata ta manta mema aka Haifa din.
Tana gama fadan kalamanta na karshe Mam ya miqe tsaye Yana ficewa daga dakin zuciyarsa Babu inda Bata tafasa da daukan nauyi.
Lameenu kuwa bayan ya miqe BB ya kalla da idanuwansa tareda yi masa kallan dayasan me yake nufi kafin Shima ya fice Yana Jin ihun Maryama din datai so Daya Bata Kara ba aka rufe bakinta.
Mota suka suka nufa da sauri BB ya qaraso ya budewa Mam driver Kuma ya budewa lameenu suka shiga Kai tsaye aka rufe driver ya shiga da sauri ya tayar da motar BB na musu a sauka lafiya suka bar gurin.
Tinda suka kama hanya Babu me cewa komai sbd kowa da Saka da warwaran da yakeyi a zuciyarsa cikin tinanin Neman mafita data inda zasu fara Neman Dan uwan matar Omar Wanda a yanzu sukeda cikakkiyar tabbacin 'dan Omar Yana hannunsa.
Lameenu da hankalinsa yafi na Mam tashi sbd yanada labarin project dinsu ba lallai yakai labari ba Dan kuwa komai Baya tafiya yanda akeso,
Idan Mam yaji Hakan abun sake lalacewa zeyi Dan shi Kam ya gaji da Mam Yana sake bawa Haroon Daman shikuma Yana sake rusa su sbd bazai taba zaba me amfanin da sukeso ba Babu amfanin basa damammakin da ake basa,
Shi a nasa son su cire Haroon daga komai nasu Dan baida amfani kawai su bazama Neman magajin Omar Dan kuwa Babu abinda zasuyi yanzu dukiyar ta dawo yanda take koma fiye da yanda suke tsammani bayan su mallaki dukiyarsu ta Omar Dake ransu tin shekara da shekaru.
Mam ma a cikin ransa kusan tinanin ne a ransa Dan kuwa idan ba bazama sukai suka haukace gurin Neman magajin Omar ba faduwansu zai Sakasa yiwa dansa abinda baitaba tsammata yi din ba Dan kuwa ya tabbatarda Haroon yafi kowanne 'da rashin amfani,
Ya rasa wane irin Kai ne dashi gashi tsaban rashin basira ya kasa roko ko rarrashin Jamaal ya dawo musu,
Ba komai ya sakashi sakar masa pressure da nuna masa hantara da rashin kauna ba sai Dan ya rufe ido ya dage ya Saka Jamaal dawowa garesu ba Dan yasan duk duniya Haroon ne kadai zai iya Saka Haroon dawo musu Dan kuwa duk Wanda yasansa yasan Haroon ne abinda yafi komai so da kauna fiyeda komai bayan mahaifiyarsa Dan haka suke zafafawa Haroon komai Dan Jamaal ya dawo musu Amma Haroon din kaman kansa Babu komai a ciki Se iska,
Duk maganin da suka Saka masa a drink suna susuta kwakwalwansa Dan ya zama abin tausayin da zai Saka Jamaal ya dawo garesa abin ya gagara sbd yasan duk abinda Haroon zai koma bazai taba zabar barinsaba Koda Jamaal da mum dinsa sunso daukesa bazai taba binsu ba Dan haka yakeda tabbacin Jamaal zai dawo sbd Dan uwansa.
Suna Isa gida kowa mansion dinsa ya shige batareda tsayawa office nasu Dan tattaunawa ba Dan kowannensu Yana buqatan kadaicewa Dan dawowa daidai.
Mum Atee na ganinsa da yanayinsa bayan shigowansa tasan akwai damuwa me girma Dan haka tabarwa Ayesha zaban kayan datakeyi a waya ta bisa zuwa sama tana fatan ba matsalar Haroon bane da itama zuwa yanzu lamarinsa yafara isarta Dan itace kullum me zuba maganin da suke basa a drink dinsa na cin abinci sai kuma ta tabbatarda yasha cikin kulawa da dadin Baki Wanda ahankali ahankali yake yiwa kwakwalwansa illa harma da kuzarinsa batareda sanin Dad dinba Dan abinda yasaka ta ringa basa daban da abinda take basa din.
******Barr Haroon seelah a yanzu ba zaman Nasarawa ne ke basa nutsuwa da farin ciki ba ganin Ameenatou ne da rayuwar ahalinta da yanzu ya zamar musu tamkar Dan uwa,
Ayanzu Daya sabu da zamanta a cikin zuciyarsa Babu ranar da Baya zuwa gidan duk yanda zai gaji da ayyuka kuwa saiyaje gidan da daddare acan yake fira cikinsu sai dare sosai yake komawa masauki.
Babbah da dukkaninsu har zuciyarsu sun basa matsayi me kyau da kauna me sanyi kallansa sukeyi a Dan uwa duk da tsananin tazarar datake tsakaninsu Dan kuwa idan ya zauna cikinsu kaman saika wanke hannu zaka tabasa Dan yanda yake fita daban kaman wata acikin taurari.
Ameenatou sosai suka shaku cikin qanqanin lokaci Kuma a bayyane yake yanzu tsananin son dayake mata duk da itama tana sonsa sosai sedai hakanan wasu lokutan sai takejin kaman irin son datakewa su Yaya Hafiz take masa Amma Kuma tace bazata auri kowa ba sai shi Dan Hakan ne ma yakejin samunta a rayuwarsa zai samu nutsuwa da Kwanciyar hankalin Daya rasa tareda kadaicin rayuwar dayake ciki.
Bai taba sanin wannan son dayake a cikin kirjinsa yanzu ba shine abinda Dan uwansa Jamaal yake ji a lokacinda fadilansa tana raye ba,
Baitaba dauka zaiso mace irin son da Jamaal yayiwa fadila ba sai yanzu dayake Jin Ameenatou har cikin jininsa da ruhinsa Dan kuwa akanta ne yafara Jin Koda Dad dinsa zai yafesa idan har zata zama cikin rayuwarsa zai iya fuskantar Hakan.
Dukkaninsu Babbah sun San so me tsanani yakewa Ameenatoun Dan haka yake sake matsayi sosai a zuciyoyinsu musamman Hafiz dayake Jin farin cikin Ameenatoun zata samu rayuwar da zata zufafa iliminta Dan sunada burin tayi karatu me zurfin da zata dogara da kanta tinda bazata zauna karkashinsuba har abada.
Aikin Daya kawosa fara lalacewa yayi matsaloli suka fara bayyana sbd gabaki Daya hankalinsa da nutsuwan dayake samu a gurin Ameenatou suna can,
Idan ciwonsa yafara tasowa na damuwa Baya gane komai Baya ganin komai idan ba gidansu Ameenatou ya taho ba ya zauna ya zuba mata idanuwansa tana magana yana sauraronta Kokuma Idan tana tareda su Babbah tana zuba sangartanta son ranta batareda damuwa da Yana gurinba Dan matiqar tana taredasu Bata duba kowa duk abinda takeso zatayi Abinta shi Kuma Hakan yake sake kashesa akanta musamman idan tana fadan shi kadai ne zai zama mijinta Babbah zai aura masa ita.
Wannan kalman itace kalman da ayanzu take fin komai Sakasa farin cikin Da bayada shi kwata kwata a rayuwarsa.
Siddeeq hankalinsa yafara tashi sosai da irin son da Haroon yakewa Ameenatou Dan karfinsa yafara Sakasa shakkar lafiyansa ga Kuma bangare Daya aikin dayake gabansu fa Babu haske ko kadan kullum sabuwar matsala ake samu Dan haka yake cikin tashin hankalin.
Ranar dasu Dad suka zauna da turawan da suke cikin aikin suka fara samun barazanar janyewa daga hadin gwiwan kwata kwata jinin Mam Hawa yayi sosai Saida aka kira likitoci gida suka dubasa aka basa magani hadda su ruwa.
Mum Atee hankalinta tashi yayi Dan haka ta dagawa Haroon hankali da kuka Saida ya dawo Lagos a ranar cikin mummunan tashin hankalin abinda ya samu Dad dinsa.
Dad Lameenu kuwa kusan zaucewa yafara kokarin yi Dan ganin Mam a halinda yake ciki yasan balain Da yakai Mam kwance ba qaramin balain da zai kawo karshensu ba kwata kwata ne ba Dan haka ya kira BB ya Bude musu wuta akan tsananta bincikensu ko Wanda ya taba sanin dangin Aminatu ne aka samu a kamosa a kawosa.
#MAMUH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
35
Tinda Haroon ya dawo Dad dinsa ya Hanasa ganinsa Dan Baya buqatan ganin ko fuskan Haroon din.
Mum Atee ce ta ringa lallaba Haroon din da duk inda hankalinsa yake ya tashi da wannan hukuncin na Dad dinsa.
Kusan Shima kwantawa yayi ciwon sbd hukuncin Dad dinsa na qin barin ya gansa.
Da wannan damar mum Atee tayi amfani ta ringa shayar dashi kwayar da suke