Showing 90001 words to 93000 words out of 261814 words

Chapter 31 - AMEENATOU

Mamuhgee   

21 Nov 2024

9885

a gurin Shima duk yanda Yan Sanda suka so samunsa da Rai tini Rai yayi halinsa cikeda baqin ciki suka dauki gawarsa Shima aka jefa wata motar daban.

Dad Omar da Babbah sune Basu rasu ba Amma sunfi wainda suka rasu kakkaryewa sosai tareda wahalalliyar azaba hakama gabaki Daya sun sauya daga mutanen da aka Sansu Dan Babu Wanda ake gane ko fuskansa sunyi mummunan raunana Tako ina Dan haka a cikinsu Babu ma Wanda alamun sauran Rai yake a jikinsa amma dai an duba suna raye din Dan haka Akai gaggawan daukansu zuwa asibiti,
Sai Ahmed da Hafiz da Suma sukai Mummunan kariya ta hannuwa da kafa hakama sun raunana sosai sedai su suna hayyacinsu sedai rikitacciyar azaba Da jininsu Dake zuba kaman ba daga jikinsu yake fitowa ba.

Suma kwasansu Akai zuwa asibiti gaba Daya,

Jamaal har acikin ambulance din rungume yake da gawar Dan uwansa ya kasa sakonsa duka jikinsa rawa yakeyi sosai kaman zai jijjige Haroon din Dan haka koda aka Isa asibitinma da qyar aka bambare gawar daga jikinsa Akai ciki da ita.

Dad Koda ya iso Lameenu na biye dashi sbd kada ya Fadi hakama su Mum Atee tini suka qaraso asibitin
Hakama su Aunt Didi matar Ahmed da Fatmah duk sun iso
Mum Nur kuwa Kuka kawai takeyi sbd tsoron dataji duk ya dabaibaiyeta.

Siddeeq Daya kasa hakuri wayoyin kowa kira yakeyi gashi itama Ameenatou din taqi farfadowan sai ruwa ake zuba mata Dan haka ya daukosu tareda dadah cikin sabon tashin hankali sukayo asibitin da ita.

Suna isowa itama aka karbeta sedai samun ahalin seelahs kaf a asibitin ya Saka su dadah cikin masifaffen tashin hankali kafin dukkaninsu su motsa daga inda dukansu suke tsaye Dr zayyan ya fito daga dakin emergency din da suke ciki da duka su Omar da Haroon din bayan fama da taqaddamar da sukasha da Jamaal kafin ya yadda Allah ya karbi ran 'dan uwansa ya koma garesa Dan haka kallansu Dr zayyan din yayi idanuwansa jajir hakama Shima hannuwansa yar rawa sukeyi idanuwansa na cikowa da kwallan Daya kasa riqewa ya kasa kallan Dad dake tsaye shi yake jiran abinda zai fada,mum Atee da Dad Lameenu na gefensa kowa Dr zayyan din yake kalla,
Su mum Sarat da Dadah ma duk a tsinke suke,
Sai su mum Nur da kukanta ya tsaya cak suna kallo bakin Dr zayyan din ya Bude cikin sauti me tsananin sanyin gaske yace

"Sai hakuri,sai hakuri, Haroon seelah da AbdulRasheed Allah ya Riga ya dauki ransu lokaci yariga yayi Babu abinda zamu iya sai hakuri da rungumar hukuncin ubangiji"
#MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBiyar

57
Ahankali Dad ya daga hannunsa da yayi masa wani irin mugun nauyi ya Dora a kirjinsa inda yaji wani abu ya tsaya masa Yana hanasa Jan numfashi kwata kwata kafin ma ya sake kokarin Jan numfashin ya yanke jiki a gurin Yana kokawa da numfashin Daya Yanke daga kirjinsa gabaki Daya idanuwansa na tsiyayo wasu zafafan hawayen masu radadi ahankali.

Mum Atee da Dad Lameenu ne suka durkushe gabansa suna ambatar sunansa cikin tsananin tashin hankali da rikicewa.

Dr zayyan ma cikin tashin hankalin me tsanani ya kira nurses da masu daukansa tini aka daukesa Akai ciki dashi Dr zayyan na cewa cikin sauri a kawo oxygen da gaggawa kafin numfashin nasa ya yanke.

Dadah kuwa da Karan farko Bata gane Abdul dinta ake nufi ba saida umman fadila ta rungumeta tana fashewa da kuka sbd dawo mata sabuwa da ranar rasuwar Taya 'yar tayi a wannan asibitin itama ranar aurenta.

Dadah sai alokacin ta fahimci me ake nufi Dan haka ta silale qasa tana Neman numfashin itama sbd kukan ma mantawa tayi da ana yinsa a duniya iskan numfashi kawai take nema a kirjinta kafin ayi yunqurin Kiran likita ya some a gurin gaba Daya jikin umma.

Mum Nur dasu Aunt Didi kukan baqin cikin rasuwar Haroon din dana farin cikin mazajensu dake raye suka sake lokaci Daya tareda tausayinsu.
Fatmah ma kukan takeyi sbd ta dauka zaace Dad dinta da Dad Omar sun rasu suma sun barsu.

Mummy Sarat ma dasu Aliyah kuka sukeyi sosai musamman Ayeesha datafi kowa shakuwa dashi Kuma ita kadaice yakeda kauna mara sirki daga zuciya a tsakaninsa da ita duk cikin family Dan haka ta zube a gurin kasa tana fasa kukan Daya Saka gaba Daya gurin daukan shiru tana Kiran sunan Haroon din.

Emergency Akai gaggawan shigewa da Dad sbd oxygen din Neman gagararsa ja ma yakeyi Dan haka hankalin likitocin ya fara tashi Dan hak suka Taru akansa ana yaqin cetan numfashin nasa hankali tashe.

Su Lameenu Dake waje ma hankalinsu tashi yayi Dan haka kusan asibitin tayi tsit ba dogon motsi bare hayaniya sbd masu asibitin ne da kansu cikinta a mafi wahalan yanayi da tashin hankalin dasuke ganin Basu taba shigarsaba.

JAMAAL Babu Wanda yagansa har lokacin sbd Yana ciki inda gawar Haroon din take tareda ta Abdul a gefensa,
Gawar Haroon itace gawar datafi masa rayuwar duka Wanda yake duniyarma yake Gani,
Gawar Haroon itace abinda ya kasa dauke idanuwansa daka kansa,
Rabin jikinsa ya tafi yabarsa,
Haroon yasha wahala da baqin cikin rayuwa fiyeda komai,
Bai samu farin ciki ba tinda ya taso harya komawa ubangijinsa,
Yaso samun sauyin rayuwa a tareda Dan uwansa da mahaifiyarsa Dan matarsa bayan auren sedai Allah baiyi zaiga hakanba,

Meyasa suka kasance acikin zuria da jinin marasa imanin duk duniya da rashin tausayi?

Kasa riqe kansa yayi daidai lokacinda ya Tina maganar Dan uwan nasa ta karshe akan farin cikin dayake ciki a yau din sbd zai auri farin cikin rayuwarsa.....

Wani irin kuka Mai tsananin radadin zuciya ne ya fashe dashi Yana Dora goshinsa gefen kan gawar Haroon din duka jikinsa na rawa da jijjigan kukan da yakeyi Mai ciwo da baqin cikin ya rabu kenan da Dan uwansa shikenan.

"Innalillahi wainna ilaihirrajiun"

Kukansa ne sosai ya Saka siddeeq kasa riqe nasa kukan tausayin Haroon da irin rayuwar rashin kaunar da ake nuna masa Daya gudanar tareda wahalan ciwo Daya ringa fama dashi batareda kowa ya sani ba daga karshe ya tafiyarsa yabar duniyar da Babu komai a cikinta sai son zuciya da azaba a gurinsa.

Dadah da Akai gaggawan taimakawa tana farfadowa wani kuka Mai ratsa zuciyan duk uwar Datake da 'yaya ne da uban dayake da yayane ta fasa tana Jin kirjinta Yana kasa daukan radadin Datake Jin kanta acikinsa,

Rashin 'dan ta Babba tareda mummunan halinda mijinta yake ciki na tsakanin Rai ko mutuwa baa San wanne zai faru ba da Kuma Hafiz da Shima aketa kokarin ganin an ceta rayuwarsa sbd jininsa da kusan ya tsiyaye da kariyar datafi nawa a jikinsa.

Mum Nur ma da Aunt Didi lokacinda suka samu bayanin halinda su Dad Omar suke ciki mum Nur kasa dauka tayi dole Akai gaggawan mayar da ita gida tinda itama lafiyar tata sai ahankali,

Dadah tin tana iya kuka Dan idanuwanta har lamarin yaci karfina ta sake rikicewa jikinta ya rikice gaba Daya dole dai itama akai gaggawan Bata kulawa aka mayar da ita baccin dole da wahala sbd zuciyarta Dake Neman samun matsala sbd BP dinta yayi mummunan hawan daya fara Sakata kaman zatai jijjiga.

Daidai wannan lokacin ne Ameenatou ta farfado sedai umma kasa barinta tayi tasan meyake faruwa ta dawo gida da ita a taxi sedai Koda suka Isa gida gaba Daya gidan anyi cirko cirko kowa idanuwansa jajir masu kuka sunyi masu shiga tsananin damuwa da tashin hankali duk suna ciki Dan kuwa labarin wannan mummunan ranar ta ahalin SEELAHs ya isarwa kowa.

Duk yanda akaso taimakon Dad abin yaci tura sai da kyar suka samu damar daidaita numfashinsa sedai Kuma Bai San inda kansa yake ba Dan a cikin qanqanin lokaci Allah ya mayar dashi abin tausayi kaman Wanda yayi watanni a kwance take ya jeme.

Lameenu ma cikin tashin hankalin da jemewan yake sbd bazai taba son ya rasa Mam ba tinda a yanzu shi kadai ne yake dashi a rayuwarsa,
Idan ya rasa Mam bazai taba iya komai na rayuwarsa shi Daya ba Babu Dan uwan nasa,

Sun rasa sauran Yan uwansu Badan basa sonsu ba sai Dan son zuciya da shedan tareda muguwar zuciya datake rinjayarsu,
A yanzu tashin Mam da ganin lafiyansa shine abinda yake cikeda zuciyarsa ya Sanyaya jikinsa Dan haka gaba Daya ya koma Kalan jemewan Shima yana cikin tsaka me wuya.

*******Hudu bayan la'asar aka iso da gawar Haroon da Abdul mansion din Dad Omar sbd jamaal Daya Bada umarnin anan zaayi janazah dinsu wadda tini mutane masu yawan gaske suka fara halarta sbd daurin auren da sukai Niya tafiya shine ya koma janazah din Dan haka manyan mutane da Jamaa Tako ina.

Saida aka gama suturtasu siddeeq yaje gida ya dauko Ameenatou wadda take gida ta rikice musu gaba Daya Babbah da Yaya Abdul da Yaya Hafiz kawai take ambata sbd wayarta ce numbern da aka fara kira a wayar Babbah cewan sun samu mummunan accident wanda Dayan police din Kuma numbern Jamaal ya kira da wayar Dad Omar.

Zuwan siddeeq gidan ya tararda sauyawan lokaci Daya da Ameenatou din tayi sbd duk abinda yake jikinta na adon auren da Akai mata ta ciresa ko Dan kunne Bata bari ba daga ita sai doguwar Riga mara nauyi da mayafi ya fito ko gabanta Bata Gani Saida umma ta riqeta suka shiga motar datake jin kirjinta na sake toshewa tana Jan numfashi kaman me asthma.

Suna isowa har cikin harabar Mansion din gidan tana fitowa mota kafafunsa suka sare ta kasa daukan kanta sbd ganin tarin mutane Tako ina.

Umma da Aliyah data fito ne suka kamata har cikin palon farko na mansion din Wanda gawar biyu suke a shimfide fuskan Abdul an Riga anrufe ta Haroon ce ake kokarin rufewa ta iso gurin idanuwanta akan fuskan ta fara sauka kafin ta kyafta idanuwata suka sauka akan dadah Dake gaban dayar gawar zaune kaman mutum mutumi take numfashinta yayi sama Yana Neman fita daga kirjinta jikin tsananin tashin hankalin da Bata taba shiga ba da mummunan shock kafin suyi yunqurin tarota tafara kokawa da numfashinta Wanda yake kokarin ficewa.....

Umma datai saurin Kiran sunanta Bata ma gama rufe Baki ba kwakwalwan Ameenatou din ta juye gaba Daya sbd rashin Babbah da Haroon shine abu na karshe da kanta zai iya dauka Yanke jiki tayi a jikin umma ta zube qasa umma na binta kasan tana Kiran sunanta da tsananin tsoro da tashin hankali sbd wannan yanayin nata ya banbanta matiqar gaske Dana farko data Suma.

Daukanta Akai akayi ciki da ita sedai ko qarasa shigewa da ita baayi ba aka dauke gawar Dan yi musu sallah aka fice dasu.

Ficewan da Akai dasu yayi daidai da sake Saka dadah mummunan halin Daya Saka ita Kam dole asibiti Akai da ita.

Daga gurin janazah din suna dawowa wayar Jamaal ta samu mummunan sakon Daya Saka kansa sake ciki fitinanniyar tashin hankali sbd mum dinsu data yanke jiki kasamakon Jin rasuwar 'danta Kuma likitan ya tabbatar masa data samu paralyze suke tinanin Amma dai Bata farfadoba Dan haka suna tsananin buqatansa da gaggawa kafin ta farfado din.

Wannan mummunan labarin sabon tashin hankalin ya kusan Saka zuciyar JAMAAL bugawa take yafara kokarin tafiya sedai Kuma hankalinsa na rabuwa biyu da barin Ameenatou baa hannun kowaba,.

Babu Haroon,Babu Babbah,Babu Dad Omar,Babu Abdul Babu Hafiz bare Ahmed Dan haka barinta a daidai wannan lokacin kaman barin nama ne a tsakiyar damisoshi.

Babbar tashin hankalin sabo shine Ameenatou din gaba Daya anyi anyi taqi farfadowa dole Akai asibiti da ita itama aka jere su kowa da dakinsa Babu Wanda yasan inda kansa yake tsakanin ita da Dad da Dadah ga su Babbah da sai yanda hali yayi Suma.

Ahmed Daya Dan samu kansa cikin karfin hali ya sanar da Aunt Didi ayi gaggawan shirin fitar da Omar zuwa gurin dangin Didi din Dake Angola sbd jinyarsu acan tinda shi baida lafiyan basa kariya ko jinyarsa Dan haka su tattara su tafi can hankalinsa zaifi Kwanciya sbd zaa iya tinanin qarasa Omar din daga Nan tinda Yariga ya shige coma shi da Babbah sai yanda Allah yayi dasu.

Mum Nur Daman Batada niyar barin mijinta a Nigeria din ayi jinyarsa sbd ko zai tashi dukkaninsu sunsan ba yanzu ba ko duba da yanayin niqan da mota tai masa Dan haka a take washe garin ranar suka hada komai suka bar Lagos zuwa Abuja sbd acan zaa tashi.

Kaman abin da ake Jira qanqanin lokaci aka rufe mansion din suka tafiyarsu batareda sun tafi da Babbah ba kaman yanda Ahmed yaso sedai Shima ba qaramin Jin jiki yakeyiba tinda ya Bada umarnin tafiyar Bai sake sanin inda kansa yake ba shima har suka bar qasar.

Jamaal Neman haukacewa yakeyi a Nigeria din sbd duk yanda yaso wucewa yabar qasar da Ameenatou lamarin ya gagara sbd Babu abinda take dashi na barin qasar hakama acan kiransa akeyi mahaifiyarsa na tsananin buqatansa da gaggawa sbd tsoron sukeyi wani abu ya faru Jamaal din Baya kusa sunsan bazai taba yafewa kowa ba..Dan haka Jamaal din yake cikin tsananin mawuyacin hali da Neman mafitan yanda zai Hana su Dad taba ko farcen Ameenatou din Tako ina.

Washe gari da wucewansu JDENS Dad dinsa ya farfado Dan haka ya sake Jin kansa ya dauki zafin da Bai taba dauka ba Dan haka Kai tsaye karfe biyun Rana ana fitowa sallahn azahar aka daura Aurensa da Ameenatou wadda ita Kuma karfe biyu da rabi ta farka sedai abinda bai taba tinanin zaiwa wani ba a rayuwarsa shine juyar Maka da hankali shine abinda yasan kadai mafita a garesa kafin yaje ya dawo ya tafi din sbd matiqar tana cikin cikakkiyar hankalinta Koda igiyoyin aurensa Dake kanta bazasu Bata cikakkiyar tsira daga su Dad da Lameenu ba sai Hakan,

Kasancewanta mara cikakkiyar hankali a yanzu shine kadai zai Hanasu mallakar ko tsintsiya daga dukiyar Omar kaf datake kasar duka sun bari daga gareta,

Babu maganar kudi ko wani gado tinda Omar yana raye ayanzu Amma sbd tsoron Omar din zai iya rasa rayuwarsa daga can ya sakashi yin Hakan sbd alluran duka duka wata Daya zatayi tana mata aiki zata dawo daidai Wanda yake Saka ran kafin can ya dawo gareta.

Siddeeq kuka yakeyi sosai jikinsa na cira sbd tausayin kansa,Dana Ameenatou din Dana Jamaal din Wanda ya kasance a tsaka me wuyar gaske gashi ya kasa yadda da kowa akan Ameenatou tinda wainda ya yadda dasu gasucan a kwance asibiti Babu Wanda yasan ranar tashinsu.

Hankalin lameenu tashi yayi mummunan yi da samun labarin juyewan kan Ameenatoun Daya fara Jin farin ciki da tsananin Jin dadin an tafi anbarta a hannunsu sune iyayenta sune sukeda cikakkiyar ikonta da dukiyarta.

Bai shiga Mummunan tashin hankalin Daya Sakasa faduwa ba Saida akayo asibitin dashi Shima Saida yaji AN DAURA AUREN JAMAAL DIN DA ITA,
AMEENATOU OMAR JEEDEN SEELAH DIN A YANZU CIKAKKIYAR MATAR JAMAAL SEELAH DINCE HALAK MALAK...... Innalillahi wainna ilaihirrajiun.

Dad ma da farfafowansa kenan zancen girgiza yayi har Saida Shima jikin ya sake Neman rikicewa.

Sunaji suna Gani Jamaal ya dauke Ameenatou din ya Kaita wani tsadaddiyar asibitin masu matsalan kwakwalwa na wani abokin aikinsa acan Poland kwararre Shima ya Bada Amanarta gasu da wani irin tsananin tsaron gaske a asibitin wanda acan ne kadai zai samu nutsuwan barinta,
Hakama radadi da tashin hankalin da zatai ta shiga akan rasuwarsu Haroon da Babbah datake tinanin shine ya rasu bazasu taba dawo mata ba sbd bazata taba tinawa ba sai ta dawo daidai zasuyi mata saukin gaske.

Da zai tafi haka ta zaune a dakinta da Babu abinda ya rasa tana kallonsa da fararen idanuwanta da suka rame lokaci Daya harya fice aka rufe mata dakin.

A ranar jirginsa yabar kasar bayan yabarwa siddeeq komai da zai kula dasu Babbah da Hafiz harma da Dadah da umma ke dawainiya da ita.

END OF PART 1
DAN ALLAH DUK INDA NAHI KUSKURE A DAUKESA A MANTUWA KO AJIZANCI,
Insha Allah bayan sallah zamu Dora part 2
Allah ya bamu ikon ibada cikin aminci da yardar Allah
Allah Kuma ya nuna mana kaman yanda mukaje hutun Nan ayau lafiya mun dawo lafiya.
##MAMUH
#AMEENATOU JDEN SEELAH
#JAMAAL SEELAH
#BABY ARFAT SEELAH
#LOVE
#DEEP
#ROMANCE
#THE SELAHS
#WARISCOMING
#ZAFAFA BIYAR


*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#bestloveStory
#Zafafabiyar
#Arewabooks@Mamuhgee

58
BismillahirRahmanirRaheem!

_Bayan wata uku!_
Navy blue uniform ne a jikinta na patients masu taushi da rashin nauyi ko damuwa a jikinta sai qaramar hula fara mara nauyi itama da Bata rufe gashin kanta duka ba musamman dayake a kunce sister Ashley ta kunce mata shi Bata wanke mata da gyara mata ba aka nemeta da gaggawa a emergency ta barta ta tafi bayan ta kama mata shi da band ta saka mata hular.

Yanda sister Ashley ta barta a zaune kan gadonta tana kallan dan hasken dayake ratso dakin kadan ta windon dayake sama sosai Dan Babu dakin patient din da window dinsa yake qasa qasa,

Shi take kalla har lokacin batareda ta motsa ba bare yin wani abin tsawon lokaci,
Ahankali fararen idanuwanta masu haske sosai suka lumshe cikin sanyi da nutsuwa ta budesu taci gaba da kallan hasken.

Hannunta na dama ta daga ahankali takai daidai setin hasken tareda ware yatsun hannun nata masu tsayi da kyau sun qara haske da wani irin kyan fata sosai tana son kama hasken,

Jin hasken Bai kamu ba ya Sakata motsawa ahankali tareda ware kafafunta Dake a hade sbd zaman nutsuwan da sister Ashley tayi mata Dan Bata barinta yin kowane irin zama,komai nata sister Ashley na mata masu daraja da gata take gudanar mata dashi Bata taba barin ciwon tabin kwakwalwanta maidata cikakkiyar mahaukaciya ba kaman sauran patients dinsu da hauka sukeyi tuburan ba sauki da yawansu.

Ziro kafafunta qasa tayi ta ajiyesu kasan ko gama sauka basuyiba tayi saurin daukesu da sauri tana kallan qasan da idanuwanta da suke cikeda zallan hasken kyau da sanyi,

Sanyi ne taji ya ratsata na qasan dakin dayayi mata sanyi sosai sbd Koda wasa sister Ashley Bata taba barinta saukowa kasan dakinta tayi yawo ba takarmi ba Wanda Takarman kadai datake sakawa slippers designers ne wanda da yawa wasu sakawa daya takeyi zuwa biyu ace sun Bata ko ta tsinkashi da kanta bayan ba hakan

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login