Showing 57001 words to 60000 words out of 261814 words
Daya kashesu da ransu a Rana tsaka.
Lameenu da tini jininsa ya sake hayewa akan babban tashin hankalin da Basu Saka masa Rana ba da sauri aka sake dawo da likita.
Da sauri likita ya dawo Yana cewa a kwantar masa dashi flat.
Mam tsaban tafasa da qunan da zuciyarsa keyi Jin yayi Haroon baida sauran amfani a garesa ko kadan Dan haka take ya Bada umarnin a Siya masa ticket a ranar zashi Nasarawan.
Lameenu na Jin Hakan yaso wartsakewa su tafi Amma Ina hawan jinin ya sharbesa da kyau Dan haka Yana ji Yana Gani Mam din ya tafi.
##MAMUH#
#DR JEEY
#AMEENATOU
#MAM SEELAH
#BABBAH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
37
Motoci ne na alfamar guda biyu harda securities suka dauko Alh Mam seelah daga airport.
Wayarsa Dake gefensa ya dauka tareda kasheta gabaki dayanta Dan kuwa Baya buqatan Kiran kowa sbd har lokacin zuciyarsa a cikin wani matsanancin zafi da radadin take Mai tsanani.
Daga Haroon har sauran ma'aikatansu manya da abokan huldan Babu Wanda yasan da zuwansa a ranar Kuma aaukan dare sukai Dan haka Kai tsaye masaukinsa Dake cikin Abuja aka nufa dashi Saida safe zai fuskanci Haroon, Haroon dinma ya fuskacesa.
Bayan samun nutsuwa da komai cikin Daren kasa tintsawa yayi ya shiga tinani masu zurfi da sakawa da warwaran ta Ina zai bullowa wannan masifu haka wani bayan wani,
Idan har Haroon na son wannan yarinyar sosai Yana buqatan sauya ha yar handling na abubuwan ta wata hanyar ba irin hanyar dayayi ta farko ba ta rabasa da Jamaal a daidai lokacin dayafi buqatansa da sonsa a kusa fiyeda komai dayake buqata a duniya Dan ko dukiyar Omar da sukeso idan basuda tasu dukiyar tayaya zasu karbeta?
Dole Yana buqatan sauya takun kammala komai cikin hanya mafi sanyi da karfin gaske Amma kwata kwata Babu maganar yabar Haroon yin auren wannan auren a yanzu Dan baima gama zama me amfanin dasuke buqatan ya zama ba ya moru bare idan yayi auren gaba Daya qarasa zama mara amfanin zeyi Kuma sai yanda mace tayi dashi Wanda baqin cikin haka zai iya sakashi yafesa ko illatasa Dan haka bazai taba barin ayi Hakan ba a yanzu saiyaga sauyin Haroon din.
****Har washe gari Haroon Baya cikin cikakkiyar lafiyan hankalinsa Dan shock da tsoron da zuciyarsa take ciki tareda mummunan firgici da tashin hankali ya Hanasa dawowa daidai duk da maganin Daya kwana Yana Sha a cikinsa Wanda harya wuce kaidarsa.
Ya boye kansa bayan siddeeq Babu Wanda yake iya ganinsa duk da ma'aikatansu da yawa dakeson ganinsa da masu zuwa da masu bugo waya duk ya kasa ganin kowa sbd state din dayake ciki bamai dubuwa bane hakama siddeeq din kansa duk ya dage sosai da kokarin hada mafitar gagurumar matsalar shiyasa Shima kansa Baya guri Daya.
Duk daqiqa Daya Dake wucewa sai Haroon ya Tina mahaifinsa da abinda zai iya biyo bayan wannan mummunan aikin kaddarar Daya samesa Dan haka hankalinsa ke sake tashi.
Tinda safe ya samu labarin Dad dinsa na Abuja daga bakin siddeeq Dan haka cikin sabon rikicewa duk da halin dayake ciki ya shirya ya fita aiki Dan Neman mafita koman kankantarta akan aikin kafin Dad ya iso Nasarawan.
Hafiz da siddeeq ganin Halinda yake ciki yana aiki gaba Daya cikin ficewa hayyacinsa riqesa sukai tareda zaunar dashi sai a lokacin idanuwansa suka ciko da wasu irin hawaye masu radadin gaske.
Kallan Hafiz siddeeq yayi tareda cewa ya tafi aikinsa kawai inshallah zaa samu mafita.
Dayake duk ma'aikatansu manya da wainda sukeda kusanci sosai irin Hafiz sunsan ansamu gagarumar matsala Amma bayansu Babu Wanda ya sani shiyasa Hafiz yake cikin damuwa sosai na ganin Halinda Haroon ya shiga akan Hakan.
Kasa aikin yayi ya taho gida Shima bayan siddeeq ya sauke Haroon din sunbar site gaba Daya Dan ciwonsa Daya tashi gadan gadan a gurin tin kafin kowa ya fahimci wani abu ko a gane musamman Hafiz da bazasu so yagani ko ya san ciwon Haroon din ba.
Yana Isa gida jikinsa duk a mace zuciyarsa ba dadi,
Bai boyewa su Babbah ba ya sanar dashi damuwa me tsananin da Haroon yake ciki take Babbah ya daga wayarsa ya Saka Kiran Haroon din Dan basa kwarin gwiwa da adduar samun mafita da nasara a duk inda take Amma wayar Haroon din a kashe Bata shiga kwata kwata.
Ameenatou ma Kiran nasa ta Saka kaman zatai kuka Jin halinda yake ciki Amma kayinsa Baya shiga kwata kwata.
Yaya Abdul ma ya gwada Kiran da tasa wayar duk dai Bata shiga.
Dadah da tashiga damuwar itama kallan Abdul tayi bayan sunkai har kusan rana Ana kiransa baa samu tace
"Bara na sauke abinci saina hada masa nasa kwando ka Kai masa saika dubo mana lafiyar tasa tinda Kiran ya kasa samuwa"
Ameenatou na Jin Hakan ta marairaice fuska akan zata bisa
Dadah ta girgiza mata Kai tana cewa
"Kul na haneki da wanna tinanin Dan Babu inda Zaki....
Karbe zancen Abdul yayi da cewa
"Har sai kin fada? Ni hauka nakeyi zanje da ita gurinsa"
Tana Jin Hakan ta Bata fuska tana komawa jikin dadah din ta kwanta tana kokarin fara Hawaye Hafiz Dake gefen Babbah Yana rubuta text yace
"Kina tsiyayo Hawaye a gurin Nan saina fasa ruwan idonki Daya muga karshen hawayen rainin wayo."
Katsesa babba yayi da cewa
"Ba zataiba ta fasa"
Maida kallansa yayi kan Ameenatoun Yana cewa
"Mayar da abinki yar budurwan gidan Babbah tare zamu dubosa idan naje ai kaman kinje ne ko??"
Gyada Kai tayi tana mayar da hawayenta tana hararan inda Hafiz yake zaune Yana jifanta da tasa hararar me zafi Shima.
Saida sukai sallah sukaci abinci dayake Babbah baida gurin zuwa ranar sai suka fita tareda Abdul din Dan dubo Haroon din.
******Isarsu yayi daidai da isowan Alh Mam seelah Wanda tin a masaukin Haroon din ya tabbatarda Haroon Baya cikin cikakkiyar hankalinsa me amfani Dan kuwa duk kyau da tsananin tsadan hotel din ganin yayi 'dan cikinsa jinin Seelahs yafi karfin zama yayi rayuwa a gurin Amma sbd ba shine ya kawosa ba abinda ya kawosa yafi wannan mahimmanci a yanzu.
Babban abinda yasa yake fatan ganawar gaske suyi budaddiyar wasika da Haroon din shine yasan Lameenu akan lamari na faduwa bayada hakuri,
Bayason abinda zai Saka Lameenu ya kasa hakurin dazai iya aikata wani abin batareda saninsu ba Dan idan har zaisa abibiya lamuran Haroon din batareda saninsa ba zai iya rashin hakurin yin wani abun batareda saninsa ba haka zalika alkawarinsu ne dayake yawo a jininsu Dan zuciyarsu kowa ya shiga hanyar shiga tsakaninsu da arzikinsu ciresa sukeyi daga hanyar kwata kwata Dan haka yake buqatan Saka hankali acikin tosashiyar kwakwalwan Haroon din idan ba Hakan ba zai barwa lameenu kulawa da komai Wanda yasan me Hakan ke nufi.
Su babbah ne suka Riga Mam din isowa Dan haka ko ganinsa Basu samu yi ba Yana bedroom dinsa Dayake suite ne yake rayuwa a ciki saiga shigowan siddeeq a gaba Alh Mam seelah din da securities dinsa duk a tsaye bakin Kofar dakin ya shigo siddeeq ya rufe kofar Yana biyo bayansa cikin tsananin girmamawa.
Yaya Abdul na ganin Hakan ya miqe a natse daga inda yake zaune Shima cikin nuna girmamawa Yana masa barka da zuwa cikeda nutsuwa.
Babbah ma miqewan yayi Yanawa mahaifin Haroon din barka da zuwa a mutunce suna kallan juna sbd kowannensu sai fuskan tayi masa kama da Wanda ya sani Amma sbd kada su kure juna da kallo sai kowannensu ya Dan dauke kallansa Dad din Yana amsa gaisuwan a mutunce Shima Dan Daman shi mutum ne Daya iya taku da mu'amalantar mutane shiyasa SEELAHs sukeda mutunci sosai a idanuwan mutane sbd iya tafiyan da lamuransa.
Yanda suka gaisa a mutunce Babu girman Kai ko nuna musu banbanci ya Saka su Babbah din sukai masa sallama suka tafiyarsu Dan Basu guri da 'dansa batareda Haroon din ya fito ba Dan abinda Basu saniba Haroon din Yana jinsu Amma bazai iya fitowa a halinda yake ciki ba su gansa.
Saida suka fice siddeeq yaje rakasu kafin Haroon din ya fito hannuwansa na tsananin rawa kansa a qasa idanuwansa jajir Babu kyan Gani hakama a jiqe yake da zufa Mai tsananin gaske,
Babu inda yakejin azaba me tsananin gaske kaman a tsakiyar kansa da kirjinsa,
Jin muryan Dad dinsa a dakin ya karasa karya dukkanin Wani karfin halinsa shiyasa ya kasa fitowa Saida su Babbah suka fice Dan ganinsa a wannan halin na mafi Munin rauni zai karya zuciyoyinsu akansa gameda Basu auren macen da bayajin zai iya rayuwar Nan Babu ita su kuwa Ayanda suke tsananin kaunar Ameenatunsu bayajin zasu taba bawa Wanda bazai iya tsayuwa a gaban mahaifinsa bama ya dago kansa aurenta sbd tinanin bazai iya Bata kariya ba ko kare martabarta.
Hannuwansa Dake rawa sosai kaman zasu qanqame yayi Baya dasu Yana kasa dagowa har lokacin kansa Juyewa yake Neman yi.
Zuba masa nasa jajayen idanuwan Mam yaji Yana kallansa sbd baisan ma me zai fara dashi ba sbd baqin ciki da damuwa me tsananin gaske Dan Shima Yana tsaka me wuyar da baisan ta inda zai fara bullowa zancen ba.
Tsadaddiyar wayarsa Daya ajiye gefensa bayan ya zauna ya miqa hannu ya dauka tareda kunnawa ya Nemo hoton Ameenatou ya ajiyewa Haroon din kan centr table Dake gabansa batareda yace komai ba tukuna.
Haroon Daya kasa motsawa bare magana dago jajayen idanuwansa yayi ya Kalli wayar da Dad din ya ajiye masa idanuwan suka sauka akan hoton Ameenatou Dake bayyane a ciki tana murmushi sanye da hijab din islamiya.
Mummunan bugawa kirjinsa yayi ya dago idanuwan da sauri sai alokacin ya Kalli Dad din da Shima shi yake kalla Yana kokarin karantar yanayinsa.
Hannuwansa Dake tsananin rawa ya sake kankamewa Yana sake kallan Dad din da kyau kafin ya Bude bakinsa Dake rawa da muryan Dake bayyanarda tashin hankalin dayafi wanda yake ciki yace
"Dad Kayi hakuri na.....
Katsesa Dad din yayi da cewa
"Ka manta mace ce ta Raba Dan uwanka da mahaifinsa rabuwa ta har abada?
Ka manta matsalolin rayuwar da muke cikinsu duka ayanzu duk sbd macen da Dan uwanka ya so ne fiyeda kansa da ni mahaifinsa?
Wasu Hawaye ne masu tsananin zafi da radadi suka gangarowa Haroon Dan Bai taba tinanin samun kansa a cikin irin yanayin da Jamaal ya samu kansa ba,
Gwara kaddarar Jamaal sbd shi yanada jarumta da karfin zuciyarsa fuskantar duk Wanda zai shiga tsakaninsa da farin cikinsa matars wadda ya tsayawa har ranar karshenta harma a bayan ranta ya tsayawa macen dayake so da dukkanin zuciyarsa.
Wasu zafafan hawayen ne suka sake gangaro masa Yana rintse idanuwansa sbd Yana fatan inama wannan jarumtar zata shigesa ya tsaya akan macen dayakewa mugun son dayakejin yafi Wanda Dan uwansa yayiwa tasa macen.
Hawayen Dake zubawa daga idanuwan Haroon dinne masu bayyanarda tsananin radadin da zuciyarsa take ciki ya Saka Dad zubawa masa idanuwansa hankalinsa na Neman tashi Dan kuwa duk tsananin quncin da rayuwar Haroon din take ciki Bai taba zubar da Hawaye ba sai yanxu.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
38
Ahankali Haroon din yayi qasa sbd kasa riqe jikinsa Dake kakkarwa sosai da yayi har lokacin idanuwansa na kan hoton Ameenatou Dake kan wayar Dad din Yana tsoron me Dad zeyi da hoton nata.
Zuciyar Dad Dake tsallen tafasa tana quna sosai akan abinda idanuwansa ke gane masa na azabbiyar Son yarinyar dayake hangowa a idanuwa da hawayen 'dansa kwalli Daya daya rage a hannunsa.
Cikin sanyi da tattara nutsuwansa dan fahimtar komai yanda zai fishesa ya Kalli wayarsa shima tareda zubawa hoton Ameenatou idanuwansa zuciyarsa na shiga shakka da rarrabar tinani akan Aminta da ita ko sabanin Hakan sbd bazaiso tarihi ya Kuma maimaita kansa ba.
Dawo da kallansa yayi akan Haroon Yana dauke wayarsa daga kan table din yace
"Sbd itane ka tattarawa dukkanin nutsuwansa kayi Watsi da ita daga aikin dayake gabanka na cika mun alkawarin dakai na sakani alfahari dakai??
Kasan wane yaqin ne a gabanmu akan wannan masifar daka jefamu akan mace?
Muryansa na kasa fitowa sosai yafara kokarin magana Amma zuwa lokacin ran Dad din ya gama tafasa Dan haka ko sauraronsa beyiba ya miqe tsaye Yana cewa
"Ka shirya a yau din zaka bar Nasarawa ban aminta da zamanka ananba bare sake ziyartar Nan din,
Kasan me zai faru daga lokacin da na sake samun labarin ko 'dan uwan yarinyar Nan Daya ka sake muamala dashi???
Zasu bata ne gabaki dayansu danginta bazaka sake samun ko labarin Wanda ya taba saninsu ba bare sanin duniyar da suka tafi...
Qarasa zubewa yayi gaban Dad din Yana fashewa da wani irin kuka Mai tsananin tausayi da tashin hankali tareda Neman ficewa hayyaci Yana bawa Dad din hakuri jikinsa da hannuwansa na tsananta rawar Daya fara bawa Dad din mamaki da tsoro ya janye kafafunsa da karfi cikin zafi zaiyi magana Haroon din ya sake rarrafowa wannan Karan Yana rokonsa da cewa
"Dad Dan Allah kayi hakuri kada ka hanani Ameenatou,
Itace ke bawa zuciyata karfin hali da zuciyan da Banda shi,
Dad nayi Maka alkawarin wanna Karan wlh zan cika dukkanin buri da abinda kakeso idan ka barni da ita,
Dan Allah Dad ban taba tambayarka komai ba sai ayau din Ina rokon ka barni na aureta nikuma nayi Maka alkawarin zama duka abinda kakeso na zama,
Ka bani Daman karshe Dad zan gyara dukkanin matsalan da aka samu a wannan aikin nayi alkawarin Hakan please Dad.
Tafasa zuciyar Dad din ke karawa yanajin kaman ya shaqe Haroon din da kansa ya qarasashi Amma Kuma zuciyarsa na yaqi da Hakan Dan bayason rasa Dan Daya rage masa.
Rikicewa Haroon yayi ganin Dad din baida niyar sauraronsa hakama yasan kaman yanda Dad din ya fada batar dasu Ameenatou Abu ne me saukin gaske duk da Baya tinanin kashesu zaai ko makamancin hakan Amma dai koma Menene rabasa da Ameenatou kaman rabasa da dukkanin sauran Dan hankalin Daya rage masa ne Dan haka yaji Yana Neman zaucewa gaba Daya Yana tino yanda Jamaal ya rasa fadila har abada sai kawai yaji kansa ya kasa dauka ya sake rarrafowa Yana biyo Dad din cikin matsanancin fita hayyaci daidai Nan siddeeq ya shigo sedai kafin ya karasa gurin Haroon din tini yafara wani irin jijjiga Yana buga kansa da kasa Yana ambatar sunan Dad din Dana Ameenatou batareda ma yasan meyakeyiba.
Jini hancinsa da goshinsa suka fara fitarwa harma da bakinsa Yana wani irin fizga take hankalin Dad din yayi mummunan tashin da baitaba tinanin zaishiga ba ya dawo da sauri Yana Kiran sunan Haroon din da sauri sedai tini ya fice hayyacinsa dukkanin jikinsa na qara jijjiga sosai.
Siddeeq ma cikin matsanancin tashin hankali ya kamo Haroon din Yana janyo pillow na kujera ya Saka masa Akai tareda birkitasa Yana hanasa bubbuga kansa a tiles da jininsa ke fita sosai.
Rasa abinyi Dad yai Yana shiga sabon tashin hankali da mamakin Menene yake faruwa da rayuwar Haroon din,
Badai shi Kuma haukacewa zaiyiba akan mace ba,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun"
Meke faruwa da yayansa?
Innalillahi wainna ilaihirrajiun.
Duk yanda Dad yake tsammanin lamarin ya wuce Nan sbd Haroon take ya koma tamkar me cikakkiyar tabin kwakwalwa duk tsananin zafi da bacin ran dayazo dashi jin yayi kansa Shima Yana daukan matsanancin zafi.
Siddeeq drawers ya nufa na gado da gaban mirror Yana yamutsa hankali tashe Yana Neman maganinsa Amma kwata kwata ya kasa Gani.
Cikin daga sauti da kidima Dad yake cewa
"Meyake faruwa dashi ne?
Menene Hakan nake Gani?
Ciwon hauka ya kamasa ne kokuwa?
Menene wannan din???
Duk a jere ciki daga murya da tashin hankali yake jero tambayoyi Yana kamo Haroon din Wanda yake jijjiga har lokacin.
A karkarshi pillow siddeeq ya sami maganin bayan ya haukata dakin cikin tashin hankali da mintinan da Basu Fi biyu ba ya iso da sauri yana Bude maganin ya kamo kan Haroon ya Saka masa
Tsaban rudewa Dad dinne da kansa ya dauko ruwa ya miqawa siddeeq ya basa rabi na shiga bakinsa Rabi na zubewa harya hadiye maganin.
Sakewa jikinsa yayi Dad yayi gaggawan Bada umarnin a fito dashi zuwa asibiti shi kansa siddeeq a daidai wannan lokacin yasan likitocin gaske Haroon yake buqata Dan haka ba Bata lokaci aka kwashi Haroon din sai asibiti.
Suna zuwa aka karbesa sbd duka jikinsa ya Dena rawa ko wani abin sai kawai aka miqasa da cewan faduwa yayi.
Dayake Mam yasan abinda zai iya faruwa na zuwan Yan jarida take ya Bada izinin securities kada su bar yan jarida zuwa ko sanin komai.
Har yamma sosai suna asibitin Haroon Bai farfado ba,
Dad magana yayi da siddeeq sosai yaji komai gameda ciwon Haroon da lokacinda ya fara take ya fahimci ba karamar illa maganinsu keyi masa ba Ashe Dan haka take ya sake shiga tashin hankali da damuwan kada Yan jarida ko kadan Susan dansa Barr Haroon seelah na fama da tabin kwakwalwa.
A Daren suka koma Abuja dashi sbd hankalin Dad Bai kwanta ba anan din.
Su Babbah da suka samu labarin anbar Nasarawan da Haroon hankalinsu tashi yayi Dan kuwa ciwonsa kenan yayi tsananin gaske haka suka ringa Kila mintina bayan mintina Dan Jin lafiyansa.
A cikin kwana da wunin Dad yayi sakawa da warwaran datafi dari da hamshin hakama Dad Lameenu ma hakanan ya lallabo ya taho sbd yasan Mam din na cikin damuwa da matsanancin hali Dan haka ya taho su fuskanci lamarin tare duk da Shima ya kasa warware sbd Bai dawo daidaiba idan ba Jin yayi sun samu mafitan warwara ba.
A cikin kwana da wuni Dad ya tabbatarda irin tsananin so da kwallafa Rai da Haroon yayi akan AMEENATOU sunan Daya riqe Kai tsaye sbd Tinanin dasuketa yawo akansa.
A karon farko da zai sauya raayinsa zuwa wani raayin Dan cimma burinsa cikin sauri da samun mafita biyu,tasa data rasa 'dansa.
Shi kansa Dad Lameenu yashiga firgicin tarihin dayake Neman maimaita kansa,
Idan sun rasa Jamaal sun tabarbare haka to Haroon dinma dasuke ganin baida amfani suna rasasa karasa tabarbarewa zasuyi komai yazo karshe shikenan.
Farfadowan Haroon Saida ya bawa dukkaninsu tausayi sbd yanajin jikin sosai Dan wanna Karan maganin ya Riga yayi masa illa sosai da Babu wani abinda zaa iya yi sai ikon Allah.
Su Dad kasa barin kowa yaji zancen sukai sbd a nasu tinanin maganinsu ne yayi masa wannan mummunan