Showing 153001 words to 156000 words out of 261814 words
yawon kawai yakeyi hadarin mota ya qarasa mishi shi,........wait wait wait wait.. accident din auren Haroon mota ce ta takasu,Kuma drivern motan a gurin mutane suka rufesa da duka suka kashesa,Motar Omar Haroon yabi.........
Ajiye wayarsa yayi hannuwansa na daukan rawa sosai zufa na tsinke masa,
Ruwan Dake gabansa ya dauka yakai bakinsa yasha.
Daya bayan Daya yake sake jera abubuwan kansa cikin tinaninsa,
JAMAAL kenan yana tinanin illata Haroon Akai duk tsawon wannan lokacin?
Yana sane kenan yake bincikensa a boye Dan Ganowa,
Kwayoyin da suka kashe Dr Dee sune suka kashe Haroon?
Menene hadin kwayoyinsu?
Kwayar data kashe Dr Dee yanada tabbacin kwayarsu ce Amma Bai taba kawo tinanin ko a mafarki ba 'dansa na cikinsa kwayar ce tayi masa illa,
Meya hada haroon da wannan kwayoyin?
Kota Yaya kwayoyin Nan suka Isa ga dansa BB Ya sani Kuma zai bayyanarda saninsa Dan kuwa Koda Haroon ne da kansa ya Siya yasha Saiya tabbatarda Wanda ya siyar masa din yabisa inda yake,
Idan Kuma Wani ne ma ya illata masa shi to bayanin dai duka dayane.
Wayarsa ya daga cikin nutsuwa ya Saka Kiran Lameenu Yana daidaita kansa tareda bayyanarda nutsuwansa a sauti.
Lokacinda Kiran ya shiga wayar Lameenu Yana zaune tareda matarsa mum Sarah suna magana tana zuba masa fresh Madara me sanyi a cikin bowl din fruit Dake gabansa.
Kallan wayar yayi Yaga sunan Mam,
Da mamaki ya sake kallan wayar sbd saninsa Mam Baya kasar,
Sake dubawa yayi da kyau sai yaga Whatsapp call ne Dan haka ya dauki wayar Yana ambatar sunansa da cewa
"Ya sauka ne??
Dan murmushi Mam yayi Yana jeho masa gaisuwa suka gaisa suna shiga zancen abubuwa daban daban tsawon lokaci kafin Mam yace
"Ina Poland tareda Jamaal yayi rashin lfy nazo dubasa Amma bamu Hadu ba sbd zafin kansa yaqi sauka har yanzu,
Amma Kuma na samu Wani zance me daure Kai akan rasuwar Haroon a bakin Siddeeq batareda sun San naji Hakan ba,
Jamaal Yana zargin mune muka kashe Haroon Dan haka bincike ake masa sosai,
Binciken ba abin damuwarmu bane sbd nasan Babu Wanda ya Isa ya kashe 'dan Mamman Seelah idan ba Allah ba,
Amma abin mamaki anan shine Dr zayyan naji ya kira siddeeq Yana sanar dashi sun samu hada results din Haroon Dana Wani Dr da akace ya rasu kwanaki.............
Ruwan Madarar da aka zuba cikin fruit salad dayake Sha ne ta biyo ta hancinsa da karfi cikin sarkewan tashin Yana dire bowl din har Yana zubewa a shaqe yana dedeta muryansa yace
"Me yake kokarin yi da results din Wani daban Kuma??
Meye amfani ko dalilin Hakan?
Haroon ya Riga ya rasu yabar Dan uwansa ya kwanta lafiya,
Kuma yasan dai Babu yanda zaayi mu illata Haroon da kanmu sbd shi 'dan mu ne"
Murmushi me sauti tareda ajiyan zuciya Mam ya sauke Yana sakewa a natse yace
"Nabari su hadasa da results din Dan Nima inason Jin Menene sakamakon"
Zufa lam ya share Yana miqawa Mum Sarah hannu ta Sako masa tissue ya sake goge hancinsa da ruwan Madara ke fitowa ciki har lokacin.
"Hakan ma shine daidai muna buqatan samun results din kafin JAMAAL din Amma sbd kada Akai masa abinda zai ruguza mu batareda mun saniba"
Murmushi Mam ya sake sakewa Yana cewa
"Dayake shi din jinina ne Magajina zai iya samun Hakan Amma bayan shi kansa ganin akwai Wanda zai taba Mam Seelah tabawa irin wannan ya miqe kuwa?"
Dariyan karfin hali lam ya sake Yana janyo Wani zancen.
Sallama sukai Mam Yana ajiye wayarsa gefensa idanuwansa na sauyawa sosai sbd ya karanci abinda yakeson karantar.
Lameenu seelah yayi wautan datafi shiga ruwa da hular dutse.
Wayarsa y dauka Kai tsaye ya kira bullet yace a Saka ido a gidan Dr zayyan a Gani idan zaa Kai masa hari a gidansa.
Hakama a tanadar masa kwayoyinsu zaiyi gwajin overdose da normal dose ga mutum biyu Daya overdose Daya normal dose Kuma a cikin ahalin seelahs zaiyi kwajin idan har ayau ankai farmaki gidan Dr zayyan zancen ya sake Bude masa da kyau.
Yana kashe wayarsa miqewa yayi ya shige ciki Yana Jin Asalin jininsa na Seelahs na Wani irin tafasa da kunar da Bai taba samun kansa a cikiba,
'dan cikinsa ake maganar anyiwa mummunan illan da tai kusan sanadinsa koma tayi din Dan ko baiyi accident ba mutuwar zaiyi sbd kwayoyin bazasu taba barinsa ya rayun ba,
Tabbas zaiyi gwajin abinda yagani a ranar da Haroon dinsa ya ringa aman jini da kusan mutuwa,
Zaiyi gwaji ga mutane biyu da Hakan zai girgiza kowa Dan tantanve yawan adadin Wanda suka durawa 'dansa kafin ya waiwayi Wanda yayi aikin gaba daya.
Lameenu kuwa tinda ya ajiye wayar yake Neman wayar BB Amma kwata kwata Baya samu Dan haka dole bullet ya kira Kai tsaye sbd idan gari ya waye komai zai iya faruwa idan Dr zayyan ya aikawa JAMAAL sakamakon komai zai iya faruwa Wanda yasan sanin JAMAAL kadai zai iya zautashi bare Mam ya sani.
Mum Sarah Kuma itama tashin hankalin take Neman shiga na Neman Aliyah da aketa yi tin dazu Babu zancenta Babu labari,
Siyam kuwa ma Bata qasar sai satin zata dawo Dan haka hankalinta ya tashi tanason sanar masa Amma ganin Halinda yake ciki na Kaida kawo Yana hada zufa ya Sakata kasa sanar masa taci gaba da Kiran Aliyahn.
*********Sai dare sosai suka Isa lokoja lokacin Ameenatou tayi Nisa sosai a bacci,
Taxi suka dauka har kofar sabon Dan qaramin gidan dasuke haya Hafiz ne ya Bude gidan bayan ya sallami me motar suka shiga Ameenatou na qanqame hannun Babbah sbd duhun datake Gani tafara Kiran sunan jamaal Dana sister Ashley.
Da sauri Hafiz ya qarasa ya kunna wutar tsakar gidan Yana cewa gashinan ya kunna mata haske.
Rintse ido tayi tana Jin kaman zata tsorota Amma yanda suka zagayeta kowa na kokarin rarrashinta ya Sakata fasa rikicewa ta Bude Baki a hankali cikin sanyi da kasala tace
"Ameenatou zatayi fitsari,
Kuma Ameenatou zatasha tea"
Dadah ce ta zare mata qaramar hijab din kanta tareda kama hannunta zuwa toilet din tsakar gidan dayake fes takaita Tayo suka fito.
Babu maganar gyara a tsakar dare Dan haka salloli sukai Dadah tayiwa Ameenatoun wanka Hafiz ya kawo tea da bread tareda kwai aka Bata Tasha tea sosai Amma bataci kwan ba tana gamawa tafara neman Jamaal kafin ta rikice bacci yayi gaba da ita.
washe gari da safe gyaran gidan dadah tayi tareda gyare dakin Ameenatou din tsaf tai mata wanka ta Saka mata kayanta ta zaunar da ita tana binsu da kallo kowa na faman yimata hidima kaman zasu cire mata ciwonta a rana Daya lokaci lokaci tana Ambatar a kira mata Jamaal da sister Ashley.
Abinci dadah ta Dora Babbah kuwa gefen Ameenatou Shima Akai masa shimfidar ya zauna Yana tayata duka shiririta ko rikicin da zatai
Hafiz kuwa wankin kayansu da suka dawo dasu yayi harma Dana Ameenatou din Yana gamawa ya fita aiki Super market din dayake Aikin yamma.
##MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
#ZafafaBiyar
94
*_AISHA's COLLECTION_*
Hajiyata Kinason kiyi kasuwanci amma bakida jari?
Ko kuma kinada jarin amma bakisan maiya kamata ki fara saidawa ba?
Tou hajiya nesa tazo kusa ga sauki yazo na kawo muku inda zaku samu kaya a cikin farashin sari,muna saida kaya kala-kala inda zaki samu a cikin sauqi da rahusa.Akwai varieties of women accessories ranging from Atamfa, Laces and shoes at both wholesale and retail..
Hajiya da kayan da kika sani da Wanda Baki saniba harma da Wanda Baki taba Gani ba na kayan alfarma da burgewa da asalin kyau na quality kizo karki bari ayi Babu ke,
ko kasuwaci ko sanyawa,ko ankon biki,lefen alfarma,kayan sallah..komaima namu inshallah na musamman ne da zakiji dadin kasancewa a cikin kasuwanci damu...
Join our group to see lot of our amazing products 👇
Location: LAGOS
We deliver nationwide
09013833502
https://chat.whatsapp.com/JRkPEIt0xVj2vuE8HAGRUL
***********Karfe 8 na safe siddeeq yayi parking motarsu a kofar gidansu Babbah tareda fitowa motar Yana gaisawa da Jamaar dasuka tarar kofar gidan suna firar safe.
Shima fitowa yayi idanuwansa a sauye sosai sbd ciwon Kai da rashin baccin da baiyiba,
Bai iya kallansu ba ko barin Suma su Kallesa da kyau ya amsa gaisuwansu Yana wucewa gaba sedai ko kofan gidan Basu Isa ba aka sanar dasu Babu kowa a gidan.
Dakatawa yayi batareda ya juyo ba
Siddeeq ne ya juya Yana tambayarsu a natse suka basa tabbacin Babu kowa tsawon lokaci hakama gidan tini su Babbah suka siyar dashi Babu Wanda yasan inda suka koma.
Rintse idanuwansa da suka qara ja a take a gurin Jamaal yayi kalaman da ake fada suna ratsashi da radadi.
Juyowa yayi sai a lokacin ya Kalli mutanen ya bude baki yace
"Tsawon Wane lokaci suka siyar da gidan?
Babu me communicating dasu?
Waye yasan inda suka koma?
Wane anguwa a cikin Nasarawa suka koma kokuwa wane gari suka tattara suka koma??
Babu me amsar tambayarsa ko Daya sbd yanda ya jerosu a tare cikin tsananin tashin hankali da buqatan amsa kawai ya sake rudar dasu akan tambayar Amma tinda Basu da sani haka suka sanar dashi babu ko Daya.
Wani jiri ne ya dipesa sbd BP dinsa da yayi raising take,
Da sauri cikin tashin hankali siddeeq ya riqesa tareda Bude masa mota yace ya koma Amma Sam Bai yadda da Hakan ba idan ba gidan ya shiga ya Gani da idonsa cewan basa ciki ba.
Da kafa yayiwa kofar gidan bugu Daya ta Bude ya shiga gidan Kai tsaye Siddeeq na biye dashi sbd ganin Baya Wani Gani sosai zai iya faduwa,
Ga rashin lafiyansa da Bai gama warwarewaba ga tashin hankalin rashinta da rashin baccin dayake tareda shi.
Kofofin dakunan gidan ya ringa shiga Daya bayan Daya Babu komai sai qura da qadangaru.
Rintse ido yayi Yana yiwa Baya kirjinsa na tsananta Wani irin nauyi da radadin da Bai taba jinsa ba a rayuwarsa,
Ina suka tafi da Ameenatou?
Ina suka boyeta?
Meyasa zasuyi masa Hakan?
Meyasa zasu dauketa batareda sani ko izininsa ba.
Siddeeq dayaga Yana Neman kasa tsayuwar da sauri ya qaraso ya kamasa suka fito ya sakashi mota sedai ko tafiyan Mintina biyu basuyiba jikinsa ya rikice da mummunan zazzabin Daya Saka har Wani rawa jikinsa yakeyi me ban tsoro.
Masaukinsu ya nufa dashi da sauri tareda Neman likita a waya Babu jimawa likitan ya iso yafara dubasa tareda basa taimakon gaggawa jikin ya Dan samu sassauci Amma ciwon Kam Yana Nan.
Ganin Hakan siddeeq ya fita bayan Jamaal din ya samu bacci ya bazama cikin mutanen dayasan dukkaninsu sunyi Hulda da muamala dasu Babbah da Hafiz harma da Marigayi Abdul ya ringa tambaya da bincike ko zai samu Wani Dan bayanin dazai taimaka musu Gano inda su babban suke Amma Sam Babu wani bayani ko kadan.
Haka ya wuni Shima a wahalce ya raba hankalinsa biyu tsakanin Jamaal dayake kwance da bincikesa.
Sai dare ya dawo ba Wani bayani Shima Bai Wani jima a zaune ba ya wuce dakinsa sbd zazzabin dayake cinsa na wahala da damuwa me tsananin gaske.
Washe gari daga shi har Jamaal acikin ciwon kowannensu ya daure suka sake bazama nema Jamaal kansa na Neman kuncewa Dan Bayan tashin Haroon dayake na mutuwa bai taba rasa abinda yakejin zai iya zauncewa ba idan ba ita din ba,
Jin yakeyi Yana zarewa daga cikin kansa,
Jin yakeyi kaman ya cinnawa koina wuta sbd rashin sanin inda take.
Duk yanda yaso dannewa ciwon da zucuyarsa keyi ya kasa dannuwa ba tsammani ciwo me tsanani ya kwantar dashi Wanda ya Saka dole Siddeeq daukansa suka koma Abuja kwanansu Daya a can suka wuce Lagos suka dasa sabon bincike acan.
Rama da sauyin da JAMAAL SEELAH yayi a cikin kankanin lokaci ya Saka hankalin Mam tashi tareda Siddeeq Dan haka kowannensu ya sake haukacewa gurin Neman inda su Babbah suke.
Mam yafi kowa sanin Babu Dan ta'addan dayakai Babbah Dan kuwa ya iya boyon da wlh bazaka iya gane inda yake ba sai idan kaddara ce ya Sakaka haduwa dashi sbd sune shedan Hakan,Saida sukai shekaru ashirin suna Nemansa kafin Allah ya kawo musu kaddarar haduwa dashi,
Sbd Jamaal da nasa burin Shima bazai taba iya zama ba batareda ya Nemo Sirikitarsa ba Dan kuwa har abada sirikitarsa bazatai rayuwar talauci da garari ba.
Lameenu da hankalinsa yake kwance cikin Jin dadinsa baisan abinda yake faruwa ba sbd a ranar Daya kira BB Bai samuba bullet ne da kansa ya bugar da BB yakuma Kashe wayarsa Dan yasan shi Lam din zai kira idan Bai samu BB ba hakan ce kuma ta faru dan haka yana kiransa ya sanar dashi akwai sakon da dr zayyan zai turawa jamaal yaje ya tabbatarda sakon bazai taba zuwa ba koda daukan ran zayyan dinne ayi.
"Ba case Boss" yafada masa tareda kashewa.
Mam bullet ya kira ya Sanar masa komai.
Numfashi me sanyi Mam din ya sauke yace masa yayi abin ya kamata yayi akan aiken ya kashe wayarsa.
A tsakiyar Daren bullet yakaiwa Lam laptop Dake dauke da results din aciki da wayoyi biyu da Suma duka akwai result din a ciki sai takardun results din da akai printing duka Wanda aka turawa Mam ne suka rarraba a wayoyin da laptop tareda printing ya sanar da Lam ga komai nan babu copy ko daya a hannun kowa harshi dr zayyan din.
Hakan yayiwa Lameenun daidai Dan haka da hannunsa ya fasa laptop da wayoyin ya hadasu guri Daya da takardun ya kona tukuna yaji sanyi.
Wannan ne ya Saka ya jisa daidai ya dawo da hankalinsa kan Aliyah da akace Bata dawoba Batama kwana gida ba tin jiya.
Kasancewan tana Hakan wani time din ya Saka Bai kawo tinanin komai akan 'yarsa ba seda dare ya Kuma yi sai gashi Kuma Tayo sakon tafiyan gaggawa ce ta kamata ya wuce South Africa motanta ma tana office a aika a dauko akwai key a hannun pa dinta.
Daddy dinta da mummy Sarat ya turawa Dan haka hankalinsu ya Dan kwanta sbd ba yanzu ne ta Saba Hakan ba.
Damuwan yanayin JAMAAL data rashin ko information Daya me amfani da zai kaisu inda Babbah suke ya Saka Mam barin lam tukuna Dan daman ko Bada wannan tashin hankalin ba a tsare yake lamarinsa bazai taba lam ba Saiya fara gwajin dosage da sukai amfani dashi ga dansa tukuna,
Bazai illata lam ba ta hanyar tabasa Amma yayi alkawarin cikin qanqanin lokaci zai rabasa da dukkanin abinda yakeso duniya tin daga kan mutum har takarmin sakawa.
*********Duk yanda suke tsammanin JAMAAL nada karfin hali da dauriya lamarin yakai Wani matakin da dole Mam ya sanar da Siddeeq ya lallaba Jamaal din su koma Poland yayi jinyar acan idan ya warware ya dawo Kuma yayi masa alkawarin kafin ya dawo bazai taba zaunawa batareda angano su Ameenatou dinba.
Siddeeq ma yayi Naam da Hakan sbd yasan Mam a yanzu dayasan Ameenatou matar JAMAAL ce bazai taba iya cutatar da ita ba haka zalika bazai bari kowa yayi Hakan ba sbd Jamaal din sosai yake jin jikinsa.
Duk yanda sukai JAMAAL Baima Basu fuskan aminta da tafiyansa yabar qasar ba batareda ya Nemosu Ameenatou dinba.
Kudi ya sake sosai anata nema da bincike Amma Babu inda ake samun komai,
Siddeeq kansa ramar yakeyi sosai duka sun tashi daga Yan kwalisar Maza masu class da dukiya sbd tashin hankali da damuwa,
Jamaal Wani irin Sumar Kai data qasumba ya tara ya qara haske sosai ya koma kaman balarabe ba batureba hakama ramarsa ta dan bayyana,
Gaba Daya yanzu Baya kowanne Aiki daga na asibitin harna office bayan yawon masallatan Lagos Babu abinda yakeyi ko zai Hadu da babban a masallaci kaman yanda Dad Omar yayi,..
Siddeeq da damuwan Jamaal din ta tsayar da tasa rayuwar Shima tinin ya sauya Shima daka gansa zakasan ya sauya komai nasu ya tsaya cak bayan yawo a garin Lagos da kewanta Babu abinda sukeyi.
Hakan yana mugun cin Mam gashi duk wata hanyar da Lam zaisan abinda ake ciki ya biya ya toshe suna cigaba da huldodinsu batareda ya taba nuna wutar datake cin jini da zucuyarsa ba akan lam din.
A cikin wannan lokacin ne Mam yayi tafiya daga can ya wuce Poland ya taba lafiyar Dr Aleena sbd son Jamaal ya dawo Poland din
Aikuwa Hakan Akai lokacinda aka kirasa kan mum dinsa jikinta ta rikice sosai gaba Daya kwana biyu kacal ya qara ya tattara ya tafi Poland din da nufin tsayawa ya samarwa mum din sauki wannan Karan Nigeria zai tattara da mum dinsa gabaki Daya su dawo inshallah sbd bazai taba iya rayuwa a wata qasar ba Kuma sanin AM tana Nigeria koma inane.
Tafiyarsu ta Saka hankalin Mam kwantawa Amma har lokacin Bai motsaba Yana jiran Lameenu ya illata Aliyah Dake asibitin tukuna Dan haka ta nasu bangaren komai ya lafa Yana tafiya a tsanake ba hayaniya lokaci kadai Mam ke jira sedai ta bayan fage Yana Tara dukiyarsa da sunayen 'yayansa da tsohuwar matarsa Dr Aleena da nufin Yana ware musu dukiyarsu ne Daya cinye Kuma duka Hakan ba tareda sanin lam ba Dan kuwa ya Siya gidaje sosai da motoci tareda filaye ba iya cikin Lagos ba Dan so yakeyi ya rusa lam da kyau.
#MAMUH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_*_Arewabooks@Mamuhgee_*
#ZafafaBiyar
95
*_AISHA's COLLECTION_*
Hajiyata Kinason kiyi kasuwanci amma bakida jari?
Ko kuma kinada jarin amma bakisan maiya kamata ki fara saidawa ba?
Tou hajiya nesa tazo kusa ga sauki yazo na kawo muku inda zaku samu kaya a cikin farashin sari,muna saida kaya kala-kala inda zaki samu a cikin sauqi da rahusa.Akwai varieties of women accessories ranging from Atamfa, Laces and shoes at both wholesale and retail..
Hajiya da kayan da kika sani da Wanda Baki saniba harma da Wanda Baki taba Gani ba na kayan alfarma da burgewa da asalin kyau na quality kizo karki bari ayi Babu ke,
ko kasuwaci ko sanyawa,ko ankon biki,lefen alfarma,kayan sallah..komaima namu inshallah na musamman ne da zakiji dadin kasancewa a cikin kasuwanci damu...
Join our group to see lot of our amazing products 👇
Location: LAGOS
We deliver nationwide
09013833502
https://chat.whatsapp.com/JRkPEIt0xVj2vuE8HAGRUL
***************
Rayuwar su Babbah yanzu ta rufin asiri ce sbd Basuda Wani abin riqe Kai sai Yan dubaru da aikin da Hafiz yayi ya samo kudi,
Lallaba rayuwarsu sukeyi duk da Babu ranar da Babbah Baya tsinewa hada zuria da jinin SEELAHs sbd sune sanadin lalacewan ahalinsa Dake zaune cikin zaman lafiya da Kwanciyar hankali gasu yanzu sun qare kullum a sauyin guri yake da boyo,
Yariga ya dauki kaddarar rashin