Showing 87001 words to 90000 words out of 261814 words
din yayi Mai sanyi kafin yace
"Ban manta ba shiyasa nayi Maka Godia.
Magana yakeson yi Amma bazai iya ba sbd hakanan zuciyarsa da bakinsa basa son furta komai bayan idanuwansa Daya zubawa Jamaal din Yana kallansa jikinsa na mutuwa hakama idanuwansa sunyi jajir.
Shima Jamaal Jin yayi bakinsa da zuciyarsa sunyi nauyi sosai bazai iya cewa komaiba bayan yin shiru suna sauraron numfashin junansu.
*******Mam a cikin Daren Lameenu daya kasa zama ya kasa tsayi yasaka BB ya kawo musu rahoton abinda yake Neman zautashi tinda yaji a bakin Haroon.
BB a cikin asibitin ya sanar da Mam wacece 'yar Omar Jaden da Kuma alaqarsa da Babbah akan cewa shine da kunnensa yaji lokacinda ya bisu.
BB na gama fada Lameenu ya sauke ajiyan zuciyarsa Dake cikin balai da masifa tinda yaji zancen shi kadai,
Maganar da farko kaman a mafarki Mam ya jita Saida ya dago idanuwansa da sukai jajir ya Kalli BB
BB din ya jinjin masa Kai alamar haka zancen yake.
Da hannu Mam yayi musu alama dasu kira masa likita numfashinsa tsayawa zaiyi.
Da sauri BB ya fice ya kirawo likita Wanda y dawo dakin tareda Mum Atee da itama tana asibitin Taki tafiya.
Tsaban tashin hankalin firgitan da Mam yayi Saida aka Saka masa oxygen na wucen gadi daqyar yakai asuba sbd tinane tinane da sakawa da warwarewa.
Asubar fari yaji dukkanin ciwonsa dayake ji a jikinsa ya warke,
Bai taba sanin Kowane 'da da baiwar da Allah yayi masa ba da kalan arzikinsa sai yanzu,
Haroon ayau ya tabbatar masa da Hakan sbd zai basa abinda yayi shekaru Yana nema tin kafin ya Saka ran haihuwarsuba,
Bai taba Saka ran duk wannan tashin hankalin da sukaita fama dashina karshen dukiyar Omar a gidansa zata dawo,
Wannan auren shine babbar taskar arzikinsa Daya Dade Yana kashe kashe gurin mallaka,
Wannan auren da yace bazaiyiba ayau Yana tabbatarwa kansa idan baayi auren Nan ba to shine Baya raye Amma wallahi tallahi Babu Wanda zai Hana auren Nan dauruwa ayau kaman yanda ayau din Omar Zai bar duniyar dukiyar tashiga hannunsa da dalili....
Lameenu da Mam din ya Sakasa zuwa asibiti gurinsa tin asubar fari gama tattaunawa sukai inda kansa ya shiga wani zafi da duhu ya shiga lissafin abinda zai faru Idan auren ya tabbata.
Wannan auren idan anyi sa Ameenatou Jden ta zama matar Haroon sirikar Mam ayau Kuma idan Omar ya mutu gadonta na dukiyarsa gaba Daya zata zama a karkashin mijinta wanda dukiyar gaban dayanta zata koma ne akan yanzu gadon sirikar Mam ce ba tasu ba da zasu mallake su Raba tsakaninsu.
Jin yayi kansa na Neman kuncewa da lissafi Amma Kuma ko yayane su Raba Omar din da duniyar tukuna zasu fuskanci juna shida Mam din akan dukiyar sbd tabbas dole kasonsu me tsoka Yana cikinta.
Mam ne ya shiga dakin da Haroon yake kwance sedai idanuwansa biyu har lokacin shida Jamaal Babu me magana sai da Dad din ya shigo Jamaal ya fice ya basu guri dad din ya Kalli Haroon Wanda Shima Haroon din shi ya kalla Yana Jin tausayin mahaifin nasa akan rayuwar Daya samu kansa Dan haka yake Jin inama zai iya sauya Dad din dayayi Hakan.
Sunansa Dad ya ambata cikeda kulawa da farin ciki shimfide a fuskansa Yace
"Haroon Allah ya albarkaci rayuwar da zaka fara daga yau dinnan har ranar tashin qiyama,
Allah ya haskaka zuciyarka yanda ka haskaka tawa,
Allah yayi Maka kyakkyawar karshe ya albarkaci zuriar da zaka Haifa."
Hawaye ne kawai suka silalo daga idanuwan Haroon sbd Bai taba samun wannan kyakkyawar adduar Mai dadin sauraro daga mahaifin nasa ba Dan haka ya rintse idanuwansa jikinsa gaba Daya na yin sanyi da mutuwa ahankali ya Bude bakinsa cikin kaunar Dad dinsa da har lokacin yakeji yace
"Amin Dad nagode Allah ya Saka da Khairan,
Allah ya tsarkake Maka zuciyarka ya wanketa Dad ya Kuma baka ikon gyarawa da tubar masa"
Shima Dad din cikin farin ciki da tsananin kaunar dansa yace "Ameen Haroon"
Jamaal ne ya dawo dakin daukeda takardun Haroon din Daya karbo dasu zai tafi akwai binciken da zaiyi akansu.
Duk da rashin karfi dayake jikin Haroon din hakanan Jamaal ya daukesa daga asibiti sbd bazai taba barin a daga daurin auren ba daga ranar sbd hakanan a yanzu zuciyarsa tafi ta Haroon cika da tsoron Da baisan na Menene ba Idan ba ganin yayi igiyan auren Haroon din sun rataya akan Ameenatou ba.
Dad ma bayajin akwai abinda zai Hana wannan auren ayanzu Dan haka gida suka dawo kowa na kokarin fara Shirin daurin auren Wanda zaayi da karfe goma Sha Daya na rana.
Dad Omar ma hankalinsa kwantawa yayi Daya samu tabbacin su Mam Basu ma samu damar magana da Haroon ba tin jiyan Dan haka yasan sirrinsu Bai fita ba Dan haka ya kira Babbah Wanda Shima yake a tsinke tini ya sake yafara Shirin daurin auren shi dasu Hafiz da zuciyoyinsu suke cikin farin ciki Mai tsananin gaske.
Amarya Ameenatou kuwa da batai waya da Haroon ba sai da safen Jin tayi kaman yayi mata caji Dan haka ta sake daga sanyin jikin datake fama dashi yin jiyan zuciyarta da kirjinta na nauyi.
Dan haka ta sake Wainda suka taho shirinta ta Basu Daman shigowa inda take Dan fara shiryata sbd daurin auren ma ya kusa ga gidan nasu a cike yake sosai da Yan bikin gashi Babbah yace bayan daurin auren zai sanar da ita abinda Bai taba sanar da ita ba Mai tsananin mahimmanci Dan haka duk ta sake zaquwa da ayi daurin auren ta zama ta Haroon ya zama nata.
Wannan tinanin kadai sake narkar da zuciyarta yakeji cikin farin ciki Mai sanyin gaske.
******A yanzu kusan dukkanin seelah Babu Wanda tin daga zuciyarsa yake cikin tsananin farin ciki da wannan auren ba Dan haka sosai ake cikin annuwan gaske Dan haka tini suka kammala nufinsu da komai akan Omar Wanda Shima yake cikin nutsuwa da farin ciki Dan ana daura auren zasu tafiyarsu hadda Haroon din da Ameenatou da Jamaal shiyasa ma suka dakatar da Dr Aleena daga zuwan tinda Nan zasu taho.
Ahmed ma Yana cikin farin cikin gaske Jamaal ne kadai yake Jin kirjinsa da zuciyarsa cikin nauyin Daya hanasa ko numfashin daidai.
Karfe goma saura kusan kowa ya gama Shirin daurin auren,
Haroon Wanda Jamaal ne ya tayasa shiryawa cikin kyakkyawar farar shaddar datai masa wani irin kyau haskensa da Bai taba sanin yana dashiba bayyana sosai.
Ayau hatta turare iri Daya sukai amfani dashi sbd komai dayake jikinsu iri dayane babu banbanci abinda Basu taba yiba kenan tin suna kanana har girmansu sai yau din.
Time Haroon ya kalla yaji jikinsa ya mutu da farin cikin wannan ranar Dan haka ya Ciro wayarsa ya Saka Kiran Ameenatou wadda itama kusan ankusa gama shirinta tana dauka ajiyar zuciya kawai ya fara saukewa kafin ya ambaci sunanta Yana ce mata Yana Sonta kawai ya kashe.
Murmushi kawai tayi tana damqe wayar a hannunta tareda cigaba da shiryawa.
Jamaal tsayuwa yayi bakin window ranar aurensa na dawowa sabuwa acikin zuciyarsa Dan haka nauyin kirjinsa yake sake karuwa Yana sakashi shiga yanayin tashin tsikar jikinsa idanuwansa na Neman sauya Amma ya kasa Hana zuciyarsa shiga wani irin tsoro duk jarumtarsa.
Matsowa Haroon yayi Yana kallan time da yayi yace
"Muje ko time yayi"
Juyowa Jamaal yayi ahankali ya zuba masa idanuwansa da suka sauya sedai Bai iya cewa komaiba.
Tsoro yakeji sosai Dan haka ya Dan dauke idanuwansa daga Haroon yanayin gaba Haroon din ya biyosa yana gyara zaman babbar rigar jikinsa.
Motar Mam da securities dinsa ce ta fara barin gidan ya wuce daurin auren zuciyarsa fes,
Fitowan su Jamaal yayi daidai da fitowan Dad Omar tareda Ahmed zasu shiga mota Dan haka Kai tsaye ya kofar harabar Daya hada gidajen suna nufa suka Isa gurinsa idanuwansa na kansu Yana kallansu a tare zuciyarsa na cika da farin ganin auren yarsa Dan haka Kai tsaye rungume Jamaal yayi kafin ya rungume Haroon da yau Shima yake cikawa kowa idanuwa da kwarjini Mai sanyi.
Cikin kulawa da kauna Dad Omar ya kallo Haroon yace su shiga motarsa suje daurin auren tare.
Cikin farin cikin Hakan Haroon ya juyo ya kallo Jamaal zaice da Dan uwansa yake son zuwa daurin aurensa sai Jamaal din Wanda ya kasa samun nutsuwa ya girgiza masa Kai Yana kallan fuskansa Yace yabi Dad din kawai.
Murmushi me sanyi Haroon yayi tareda gyada Kai kaman qaramin yaro yabi dad da Ahmed dukkaninsu suna murmushi suka shige mota.
Jamaal na kallo suka tada motar suka bar harabar gidan Shima ya juya yabar harabar gidan.
Dayake sun Dade da fita kafin ya fita Kai tsaye biyawa sukai suka dauki Babbah sbd Shi Daman da Omar zasu tafi daurin auren sai gashi Kuma sunzo da Haroon sai Hakan yayiwa Babbah dadi sbd zaiso ya sake bawa Haroon amanar Ameenatou
Babbah na shiga suka tada motar suka bar gurin.
Jamaal na kama hanyar zuwa gurin daurin auren siddeeq ya kirasa kaman bazai daukaba Saiya Isa sai kuma ya dauka
Abinda siddeeq din ke sanar masa yaji Yanzu daga bakin Lameenu da BB a Mansion shine ya sakashi juya kan motarsa ya kama hanyar gidansu Ameenatou sbd bazai taba barin wani abu ya samu matar Haroon ba aranar aurensu kaman yanda Shima ranar auren ya rasa tasa matar.
Wayar Dad Omar yake kira cikin gaggawa Amma Sam Bata shiga,
Ta Ahmed ya koma kira kwata kwata Bata shiga itama,
Ta Haroon ya kira ita Kuma Saiya jita a cikin motar dayake din Dan haka yayi wurgi da wayar seat din gefensa tareda qarawa motar tsananin gudu yana nufar gidan.
Yana Isa kofar gidan Hafiz da Abdul sun fito kenan cikin Shirin wucewa ko kashe motar baiyiba ya fito da sauri Yana kallan Abdul yace
"Yi sauri karbi bayansu Dad da Babbah ka sanar musu kada su bi ta Aneyam nzki road,
Ka tabbatarda Basu bi hanyar ba yi sauri, yi sauri...
Abdul na Jin Hakan da Kuma ganin yanda Jamaal din yake a zafafe ya sakashi fadawa motar Hafiz ma ya fada suka bi bayan su Haroon din da mugun gudun gaske.
Shikuwa Kai tsaye harabar gidan ya shiga daidai fitowan Ameenatou din zata bawa Hafiz agogonsa Daya manta gurin sauri cikin mahaukacin navy blue tsadaddiyar lace din Daya fidda kayanta da kuruciyarta akansa idanuwanta akansa suka sauka ta tsaya cak daga inda take tana masa kallan Daya Sakasa qin kallan fuskanta bare gane kamanninta.
Takowa tafara yi ahankali tana nufosa cikin sanyin da duka jikinta kawai taji yayi hakama kirjinta nauyi yayi mata take me tsananin.
Gap take da isowa gurinsa wayar hannunta tayi ringing daidai Nan tasa wayar Shima tayi ringing itace ta fara daukan tata tareda kaiwa kunnenta tareda tsayawa cak daga inda take.
Daga nasa Kiran yayi da siddeeq yayi masa sedai baima gama Jin Abinda yafara fada masa ba Ameenatou ta Yanke jiki ta zube a jikinsa kaman matacciya Shima Neman zubewan yakeyi siddeeq daya iso bakin gate din gidan a haukace sbd mummunan tashin hankalin da baa Saka masa Rana ba ya shigo da mugun gudu.ya taresu gaba dayansu.
##MAMUH#*_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabook@Mamuhgee
#ZafadaBiyar
56
A jikin Jamaal gaba Dayanta Ameenatou din ta zube Dan haka baida zabin Daya wuce riqeta da hannuwansa Shima nasa kafafun na gagararsa daukansa.
Siddeeq da idanuwansa ke rikice da wani mugun ja riqesa Shima yayi Yana Kasa kallan fuskarsa data fara gaba Daya.
Umman fadila ce tareda anti zulaihat cikin mutanen dadah da suka taho daga Nasarawa biki ne suka fito daukan kaya a harabar gidan suka tarar da wanna tashin hankalin da sauri siddeeq yace umman tazo ta dauke Ameenatou daga jikin Jamaal din.
Da sauri suka qaraso tare umman ta tattaro Ameenatou din daga jikinsa tana tambayar lafiya a rude Tana raba idanuwa a tsakanin Ameenatou din da Jamaal da Kuma siddeeq din.
Siddeeq Bai iya cewa komai bayan cewan suyi ciki da Ameenatou din shikuma ya kama Jamaal Wanda har lokacin kaman jiri yake Gani suka fito daga harabar gidan Kai tsaye motar da Jamaal din yazo da ita suka nufa shi siddeeq din yabar wadda yazo da ita a gurin.
Saida ya zaunar da Jamaal din a mota kafin ya zagaya da sauri ya shiga motar zai tayar Jamaal ya dago jajayen idanuwansa ya kallesa daqyar ya iya Bude Baki yace
"Bani key ni zanje na dubo Kai ka Jira anan din Sbd A,dole Ina buqatan barin wani anan din incase.
Siddeeq kallansa yayi da nasa jajayen idanuwan Shima Yana girgiza Kai sbd bazai iya barinsa yayi tuqi ba a lokacin da kansa.
Bude motar Jamaal yayi tareda fitowa ya zagayo ko gabansa Baya Gani dakyau wani irin wuta da radadin azabar nauyi yake ji a kirjinsa Babu abinda yakeso kaman ganinsa gurin da ake maganar.
Karban key din yayi Bai tsaya komaiba ya fada motar Yana rufewa ya tayar Kai tsaye yayi mata wani irin mugun ja yabar gurin siddeeq na bin bayan motar da kallo hankalinsa na mummunan sake tashi sbd kaman zata tashi sama tsaban mugun gudun da Jamaal din keyi.
Jamaal na barin gurin yayi cikin harabar gidan Yana fiddo wayarsa aljihu Yana rasa a cikin wainda suka tafin waye zai kira tinda Babu me lafiyan dauka Kila.
Jamaal kuwa tuqin yakeyi idanuwansa na Neman rufewa Amma karfin hali Dana zuciyarsa Basu bar hakanba Saida ya hau titin da zai Kaisa Aneyam nzki road Wanda yake kaman bypass Babu mutune sosai.
Yana Jin Nisa sosai a kan titin
Tin daga nesa yafara hango mutane da Jamaan tsaro sun rufe titin hakama hadda masu daukan hotuna da wata katuwar mota a gurin datake kokarin kamawa da wuta anata ihu da hayaniya.
Tin anan Kunnuwansa sukai masa wani irin dim suna kokarin dauke jinsu,
Idanuwansa kuwa wani dishi dishi suke son fara masa Amma ya rintse su da karfi tareda budewa Yana budewa motarsa da sauri ya fito batareda ya kasheta ba hakama wani parking din tsakiyar Titi yayi Yana qarasowa gurin da gudun gaske ganin motar Dad Omar data Abdul sun hade guri Daya kaman kayan wankin da aka hada aka matse cikin mafi muni da tashin hankalin kallo a kusan karkashin babbar motar wadda da alama itace tayi musu hawan tela.
Daukewa ganinsa yafara yi da gaske hakama kunnuwansa Dan haka take yafara Neman kasa karasawa sbd jiri da rashin Gani,
Daidai lokacin Mam ya iso gurin da drivernsa tareda Lameenu cikin matsanancin tashin hankalin da Bai taba Shiga ba Shima nasa ganin da Jin kusan daukewa yayi can sama sama yakejin maganganun mutane da iska suna kadawa hakama gabansa Baya Gani sosai Yana Sako Kai inda police din gurin janye masa shida Jamaal daidai lokacinda aka shimfide gawar Haroon da aka samu cirowa a gabansu cikin fararen kayansa da suka sauya take Babu ko dogon haskensu koina jininsa ne ya sauya kalar kayan gabaki dayanta.
Daga Jamaal har Dad lokaci Daya kafafuwansu suka sare a gaban gaban gawar suna zubewa Jamaal take ya qarasa zubewa qasa Yana rarrafowa gaban Haroon din Dan cetan ransa sbd Bai yadda da wani abin ya Riga ya faru ba da Haroon dinsa, Dad kuwa zubawa gawar idanuwansa yayi hannuwansa na wata irin rawar tashin hankali bakinsa na rawa yace
"Kuyi sauri ku kawo mota muje asibiti Dan uwansa likita ne kwararre gashinan zai taimaka masa kuyi sauri,
A kawo mota,
Me kuke Jira?
A kawo mota da sauri 'dana Yana buqatan taimakon gaggawa,
Yaro na Yana buqatan Isa asibiti,
Lameenuuuu a yi gaggawan kawo mota Dan Allah karku bari yarona ya mutu a Haka yanada raunin zuciyaa, HAROON,HAROON,
HAROON my boy,
Yarona 'dan Albarka Karka tafi ka barni Kai kadai nake dashi a cikin abinda nake tsananin so a duniyar Nan,
Haroon,Haroon...... innalillahi wainna ilaihirrajiun....
Dukkanin maganganun da Dad din keyi Baya hayyacinsa sbd Bai yadda da Babu Rai a jikin Haroon ba sbd jamaal ma kwata kwata ya kasa yadda da Babu Rai a jikin Dan uwansa Dan haka yaketa kokarin dawo da numfashi a jikinsa ya hanyar dubarunsu na likitoci hannuwansa na wani irin tsananin rawa hakama nasa fararen kayan tini sukai kaca kaca da jinin Yana rungumo Haroon din idanuwansa na qanqancewa Yana ihun su kawo ambulance Shima.
Lameenu rudewa yayi Shima yafara cewa a kawo ambulance Maza Maza daga SEELAHs hospital Yana Jin tsananin tashin hankali da tausayin halin da yaga Mam a ciki yau harma da tsoro da fargaba duk ya shiga sbd dukkaninsu Basu taba kawo tinanin Haroon zai shiga motar Omar ba,to mema ya shigar dashi,
Babban tsoro da tashin hankali da mugun firgicin dayake ciki shine bayan wucewansu Omar din tareda Haroon Saida ya Jira Jamaal ya gama wayoyinsa tukuna ya fice kafin ya fidda wayarsa ya kira Lameenu din Kuma daidai wannan lokacin ne siddeeq ya shigo mansion din Bai dauka su Jamaal din sun wuce ba sbd yanata Kiran wayarsa busy yake.
BB ya sanar da Lameenu cewan Haroon fa yabi motar Sir Omar a dakatar da aikin kokuwa a qaddamar dashi yanda aka tsara sbd Haroon na ciki,
Kai tsaye Lameenu Bada umarnin yayi ayi aikin kaman yanda aka tsara sbd Ameenatou bazata taba zama sirikar Mam ba ta yanda zai fisa Iko ko mallakar dukiyar gaba dayanta bayan wuyar da suka shawo akanta Dan haka gwara Bata zama sirikar tasaba tin farko suna gamawa da Omar itama su gama da ita shikenan sune magada tinda sune ake kallan uwa Daya Uba Daya dashi Kuma kada a kuskura duk tsanani bayan aiki a cewa Mam an sani su tsaya akan Basu San Haroon yabi motar ba.
Hakan da siddeeq yaji ne ya sakashi Kiran Jamaal Wanda ya gama wayarsa harya fara Nisa a hanya ya fada masa take shikuma ya sauya hanya yabi zuwa gidansu Ameenatou Dan cimma su Dad din da bawa Ameenatou kariya kafin ya samu a dauro auren a dawo yasan Dan uwansa ya samu mallakar macen zuciyarsa.
Wuto babbar motar ta fara ci dashi Dan haka Akai saurin Bude ambulance din data iso aka fara dauke gawar Haroon aka Saka kafin ta Abdul wadda itama kallo Daya zakai masa ka fashewa gawar da kuka sbd daidai lokacinda su Abdul din suka iso gap da motar su Dad sun musu magana kenan babbar motar data taho da mugun gudun ta haye kansu gaba Daya cikin rashin tausayi kuma Yana hayewa kansu da motar sedai kafin ayi wata wata drivern ya Bude motarsa yana kokarin guduwa a raunane Dan Shima ya raunana sosai
Sedai Yana fitowa motan zai gudu yaran BB Dake gurin a rarrabe suka taso suna rufesa da dukan mutuwa suna cewa ya kashe mutane zai gudu
Take mutane da Jamaar gurin suka tayasu aka rufesa da dukan da take aka kashesa