Showing 159001 words to 162000 words out of 261814 words

Chapter 54 - AMEENATOU

Mamuhgee   

21 Nov 2024

9859

Tako ina dukkaninsu suna buqatansa musamman Ameenatou hakama shi nasa karfin Neman Yana Neman qarewa kaman Wanda Bai taba shiga aji ba,ga babba ma duk da ya samu lafiya yanzu Amma Babu karfin nema yanzu,ga Dadah ma duk wahala na Neman tsofar da ita,

Babu me farin ciki ko walwala a cikinsu shiyasa haryanxu sun kasa sakewa sosai a cikin mutanen anguwansu koyaushe suna kame a guri Daya.


Koda Ameenatou ta shiga watan haihuwanta ta sauya sosai tin daga kan lafiyan jikinta harta kanta sbd Takoma shiru shiru sosai ko magana batason yi hakama komai na juyewan kanta kusan ya dawo daidai kawai abinda take kasa tinawa kanta na juyewa wasu lokutan shine shin haroon Yana Ina??
Waye Jamaal a gurinta hakama waye Haroon??
Hakama kamanninsu na mutum Daya take Gani a idonta Kuma ta kasa tantance Ina kanta yake yanzu Ina ta baro.

Babbah da Dadah daidai gwargwado sunata Shirin haihuwarta Kuma Shima Babbah yanzu Babu abinda yakewa yarsa fata bayan kyakkyawar rayuwa ingantacciya itada abinda zata Haifa masa Wanda sun Riga sun rungumi kaddara basa fatan ma tsayawa Wani janye janyen Neman uban sbd rufawa Kai asiri.

Ta bangaren Hafiz ya zurfafa Neman hanyar isarwa da Omar Jaden Sako ta duk inda zai iya Amma rashin kudi ya Hanasa Isa ga wasu hanyoyin da yawa na Isa ga garesa dashi.

Har Abuja yaje so biyu Dan samun isarda sakonsa a companies dinsa Amma kwata kwata ko Daman shiga Bai samu ba bare Isa ga manyan da sune zasu dan iya masa hanyar magana da Jden din ko Kuma Ahmed hakanan yake kashe kudin mota a banza ya dawo.
#MAMUH#*_Arewabooks@Mamuhgee_*
#ZafafaBiyar
97

*_AISHA's COLLECTION_*
Hajiyata Kinason kiyi kasuwanci amma bakida jari?
Ko kuma kinada jarin amma bakisan maiya kamata ki fara saidawa ba?
Tou hajiya nesa tazo kusa ga sauki yazo na kawo muku inda zaku samu kaya a cikin farashin sari,muna saida kaya kala-kala inda zaki samu a cikin sauqi da rahusa.Akwai varieties of women accessories ranging from Atamfa, Laces and shoes at both wholesale and retail..
Hajiya da kayan da kika sani da Wanda Baki saniba harma da Wanda Baki taba Gani ba na kayan alfarma da burgewa da asalin kyau na quality kizo karki bari ayi Babu ke,
ko kasuwaci ko sanyawa,ko ankon biki,lefen alfarma,kayan sallah..komaima namu inshallah na musamman ne da zakiji dadin kasancewa a cikin kasuwanci damu...
Join our group to see lot of our amazing products 👇

Location: LAGOS
We deliver nationwide

09013833502

https://chat.whatsapp.com/JRkPEIt0xVj2vuE8HAGRUL

************
EDD din Ameenatou sauran sati uku Hafiz ya shirya kudaden da suka Tara na haihuwar ya cewa Babbah interview aka kirashi Abuja ya tafi Lagos kwanansa biyu Yana yawo a tsakanin companies din JDENS Dake Lagos Babu nasara harya Yanke shawarar dawowa dai sai Kuma ya tafi Dayan kamfanin Wanda shine ma ya fara zuwa daga farko.

Cikin ma'aikatan da zaawa interview ya samu ya shige daqyar Allah ma yasaka da takardunsa ya tafi Daman Dan Koda Allah zai basa wani aikin duk da basuda raayi ko kadan na zaman Lagos Kuma.

Director din kamfanin ne ya kallesa lokacinda ya gama jero masa bayanin Omar Jaden da kansa yakeson magana dashi idan da hali Kokuma a Isar masa da Sako Dan Allah.

Sake kallansa yayi a wulaqance zai kira securities Hafiz din yayi saurin sanar dashi 'yar Jden dince ta cikinsa ake magana Akai yayi masa alkawarin ba karya yakeyiba.

Sake mamaki da takaicin zancen yayi sbd a saninsu Jden baida 'ya ko 'da.

Rantsuwa da magiya cikin qasqantar da Kai Hafiz yaci gaba da rokonsa akan Sako kadai yakeson ya sanar masa Wanda yayi masa alkawarin wlh tallahi sai Jden yayi masa matsayin da baiwa kowa ba akan wannan sakon.

Tsoki director ya sake Yana daga wayarsa ya kira securities kawai.

Da sauri Hafiz ya Ciro numbernsa Dake dauke da cikakken sunansa Dana Babbah ya ajiye gaban director Yana magiya da rokonsa akan wannan sakon kadai yakeson a isarwa Jden din batareda cewa komaiba.

Jansa securities sukai ciki zafi da wulaqantawa suka fice dashi har wajen gate suka miqawa Yan Sanda Dake waje suna Jira.

A station Hafiz din ya kwana washe gari suka sakesa da kansu ya fito a wahalance yunwa da zazzabin wahala na Neman illatasa Amma hakanan ya daure tareda dangana ya hakura akan maganar Neman Jden yabarwa Allah komai inshallah zasu samu mafitan da zasu reni babynsu da kansu.

A ranar ya tattara ya shigo motar dawowa gida.

Bayan dawowansa jinyar wahala datake cin jikinsa da rayuwarsa yayi tsawon kwanaki Amma dole ya daure ya tashi yaci gaba da fita nema sbd Babu me nemowan sai shi.

Acan kuwa director bayan tafiyar da Akai da Hafiz samun kansa yayi da rarrabuwar tinani,

A iya saninsa Sir Jden Bai taba haihuwa ba Amma Kuma kaman yanda ake magana dukkanin dukiyarsa sunan AMEENATOU ne Akai Wanda da yawa suke cewa sunan matarsa ne data rasu wasu Kuma suce matarsa ta rasu bazai yiyu yaci gaba da Saka sunanta akan kadarorinsa ba da dukiyarsa,
Wannan shine sirrinsa Daya da kowa ya rasa gane gaskiyarsa ko maanarsa,
To idan da gaske wannan yaron yakeyi Jden nada 'ya Kuma tana hannunsu???

Idan ya miqa sakon zai iya samun matsayin dayake buri kuwa??

Tabbas zai gwada sbd a banza wannan matashin bazaiqi fadan komaiba ya Bada number kawai da suna Wanda Hakan na nufin Jden din na Gani zai iya gane komai kenan??

Kwana biyu director yayi Yana shawara da Tinanin gwada sa'arsa Dan haka a kwana na hudu ya dauko sakon Ya zubawa takardar idanuwansa dakyau ya qarewa sunan Hafiz Nuhu babbah da Nuhu babbah sai Kuma AMEENATOU NUHU BABBAH da manyan baqaqe kafin numbernsa a qasa.

Shiru yayi Yana sake karanta sunan AMEENATOU din Wanda yanda yake rubucen Nan kusan haka sunan yake rubucen a cikin zuciyarsa na tinanin Allah yasa Hakan ne a zuciyar Jden.

Shi kansa baida matsayin magana da Jden din direct Wanda ya Yanke alaqar komai da Nigeria Yana jinya Amma a saninsu ya warke a kwanakin akace Amma dai babu Wanda yasan a qasar dayake.

Da Sir Ahmed suke magana Shima kusan sai Wanda yakai yake iya magana dashi sbd shi kansa babba ne me girman da sai me babban matsayi Amma shi dayake Yana cikin masu yawan gaidasa a waya Dan haka Yana communicating dashi Kokuma yace Yana bibiye dashi sbd duk sati Yana tura masa sakwan gaisuwa sbd Baya daukan waya sedai ka ajiye masa Sako.

A yanda takardar take hotonta kawai ya dauka tareda turawa Sir Ahmed din ta Whatsapp sbd yasan ko ya kira ba dauka zaiyiba Dan haka ya tura Yana fatan gwajin sa'ar da yayi ya zamar masa alkhairi.


Ameenatou na shiga satin haihuwanta Hafiz yaje Nasarawa ya qarasa siyar da Rabin gidansu ya dawo da kudin suka Siya mashin din da zai fara sana'ar Dan Acaba Sbd dole Saida Hakan tinda haihuwa zaa musu,
Rago suka siyo aka daure na radin sunan abinda zaa Haifa,
Sauran kudin Kuma abinci suka Siya da Yan kayan buqatan Ameenatou wadda zuwa lokacin gadan gadan sauki yake zuwan mata sbd halin quncin dasuke ciki tini ya Dade da tafiya da walwalanta.

Kudin sun qare Dan haka Dan sauran abinda ya rage suke lallabawa Dan kuwa kudin da suka tanada na zuwa haihuwa tini suka shige a lalura Amma suna da tsammani tinda Acaba Hafiz din yakeyi Wanda shi Kuma a nasa bangaren Bai fara ganin haske ko Daya ba a Harkan acaban.

Ana gobe EDD din Ameenatou zai cika kaman a mafarki cikin dare Dadah taji Wani irin sautin kuka me karfin gaske daya Saka dukkaninsu fitowa rikice suna nufo dakinta Babbah na cewa haihuwa ce.

Hafiz Jin yayi gabansa yayi mummunan faduwa sbd Babu kudin komai a jikinsa hakama tausayin Ameenatoun yake ji kaman zai fasa kuka.

Babbah ne a gaba suka shiga dakin gabaki dayansu suna kunna hasken wutar dakin da Babu komai acikinsa bayan katifa da jakar kayanta ta sakawa.

Ganinta zaune tsakiyar katifa rungume da cikin jikinta kanta aqasa tana Wani irin kuka sosai Mai tsananin tsima zuciya Wanda Bata taba yinsaba a rayuwarta tinda aka haife takeyi dukkanin jikinta na Wani irin rawa.

Tsayawa Dadah tayi cak daga inda take sbd take ta fahimci meyake faruwa itama take Hawaye suka balle mata jikinta na tsananin sanyi tana kasa qarasawa.

Babbah da Hafiz ne sukai kanta da sauri sedai hannu Dadah ta miqa ta riqe hannuwansu tareda girgiza musu Kai tana cewa

"Ku barta tayi kukan ta dawo daidai ne Inshallah"

Da sauri Babbah ya juyo ya Kalli Ameenatoun idanuwansa na cikowa da wasu irin hawayen farin ciki da baqin cikin lokaci Daya sbd ta dawo daidai ta samu kanta da wannan mummunan kaddarar ta haihuwa irin wannan da ko ita bazata Tina waye yayi mata wannan zalincinba.

Hafiz kuwa kasa riqe nasa kukan yayi yafara Hawaye kukansa na cin karfinsa ya fasa ahankali Yana qarasawa gurinta ya ambaci sunanta cikin radadin zuciya murya na karyewa.

Ambatar sunanta da yayi ya Sakata cusa kanta cikin kafafunta tana sake fashewa da kukan dayafi na farkon tsima zuciya.

Rawa muryan babbah keyi Yana riqe kukansa yace

"Ameenatou sai hakuri,
Haka Allah yaso,
Kaddararmu ce wannan,mudai fata da burinmu Daman kece Kuma tinda munsamu kinzo hannunmu cikin Aminci da yardarsa ai mun gode masa wannan Rabo Kuma shima dai mum Barwa Allah komai mun karba allah zai Saka mana ga duk Wanda ya Miki Hakan, inshallah zamu samu kyakkyawan sakamako daga ubangiji,Abdul ya tafi sedai addua shima,Haroon ma sedai adduar......

Kasa riqe kukansa yayi ya fasa Wani kuka mara sauti me tsananin ciwo da radadi Yana sauke Kai sbd dukkaninsu baqar Rana ce wanna garesu ta haihuwan Nan,
Da ace aure ne akan Ameenatou da haihuwar Nan da sunfi kowa farin ciki da murna Amma shikenan yanzu basuda wani farin ciki bayan fatan saukanta lafiya ta tashi lafiya itada abinda zata haifar musu.

Hafiz ma kuka yakeyi sosai kaman qaramin yaro sbd dawowanta daidai sai yanzu ne zasu koka rashin Dan uwansu da sukai Abdul.

Dadah ma kukan takeyi an rasa me magana a cikinsu Daren tsit hakama gidan tsit sannan dakin ma tsit sheshekan kukansu ne ke tashi kowannensu zuciyarsa kaman zata mutu sbd radadi da Kuna tareda damuwanda basusan Yaya zasuyi ba Kokuma ta ina zasu fuskanci rayuwa yanzu.

Kukanta yafi na kowannensu tsananin radadi da azabar zuciya sbd batasan ma Me ake nufi da duka bayanan da akeyiba abinda ta sani kawai shine Haroon ya rasu hakama Yaya Abdul to Amma a Ina ta samo cikin jikinta?
Aure Akai mata da wani batareda tana cikin hankalin kanta ba.........

Fashewan ruwan nakuda ne masu karfi ya Saka dukkaninsu dago jajayen idanuwansu suna kallan ruwan dayake gangarowa daga karkashinta.

Dadah na ganin Hakan tayo kanta sedai Kuma take azabbiyar ciwon mara ta tinkarota gadan gadan cikin tsananin ciwo da azaba ta dago jajayen idanuwanta ta Kalli dadah Dake tambayarta nakuda ta taso ne?.

Fitowa su babbah sukai daga dakin sbd sosai nakudar ta taso mata me azabar radadi.

Rikicewa Dadah ke Neman yi Amma sbd dare ne dole ta nutsu tafara taimaka mata tinda Babu Daman zuwa asibiti yanzu hakama Babu Daman Kiran Mai Taimkawan.


Cikin qanqanin lokaci Ameenatou tafara ficewa hayyacinta sbd azaba da wahala,

Hafiz kuwa sai duba wayarsa yakeyi Yan fatan gari ya waye da wuri ya fita Neman kudi kafin a haihun Babu komai na abinci Kokuma abin Sha a gidan bare kudin siyan magani.

Babbah kuwa gabaki Daya fita hayyacinsa yake Neman yi da ciwon kirji ya taso masa sosai sbd ranar yau din tana dawo masa da tinanin komai na ranar da Aminatunsa take nakudar haihuwan Ameenatoun Kuma a ranar ne ya rasata rashi na har abada.


Nakudarta tayi nauyi sosai Dan haka tafara gabalaita karfinta yafara karewa daqyar suka samu Safiya tayi Hafiz ya fita jiki na rawa zuciya ba kwari Neman abinda zai samo ya kawo ko asibiti ne sai atafi akaita.

Yana fita Dadah dataga tana Neman rasa 'yarta fita tayi hayyacinta ga hadari me tsanani ya Hadu ana kokarin fara yayyafi ta fita ta Nemo Hafsatu me karban haihuwa Dake maqota dasu.
#MAMUH*_Arewabooks@Mamuhgee_*
#ZafafaBiyar
98

*_AISHA's COLLECTION_*
Hajiyata Kinason kiyi kasuwanci amma bakida jari?
Ko kuma kinada jarin amma bakisan maiya kamata ki fara saidawa ba?
Tou hajiya nesa tazo kusa ga sauki yazo na kawo muku inda zaku samu kaya a cikin farashin sari,muna saida kaya kala-kala inda zaki samu a cikin sauqi da rahusa.Akwai varieties of women accessories ranging from Atamfa, Laces and shoes at both wholesale and retail..
Hajiya da kayan da kika sani da Wanda Baki saniba harma da Wanda Baki taba Gani ba na kayan alfarma da burgewa da asalin kyau na quality kizo karki bari ayi Babu ke,
ko kasuwaci ko sanyawa,ko ankon biki,lefen alfarma,kayan sallah..komaima namu inshallah na musamman ne da zakiji dadin kasancewa a cikin kasuwanci damu...
Join our group to see lot of our amazing products 👇

Location: LAGOS
We deliver nationwide

09013833502

https://chat.whatsapp.com/JRkPEIt0xVj2vuE8HAGRUL



************
DAWOWA LABARI
Ameenatou tsananin azaba ya Sakata somewa tana kwance kaman Babu Rai a jikinta Babbah ya iso kofar gidan da taxi din Daya samo daidai lokacin Shi Kuma Hafiz Yana kokarin tsayawa wani passenger Daya samu zai hau mashin dinsa wayarsa Dake aljihunsa tayi ringing Ya Ciro Yana Dan kare wayar da hannunsa sbd ruwan sama Baya ganin me Kiran sosai.

Bai ga suna ko numbern data kira dinba sbd ruwa Dan haka daukan Kiran kawai yayi tareda dorawa a kunne kafin yayi magana Kai tsaye yaji muryan da ko bacci ya tashi zai ganeta ta ambaci sunanta cikin Wani irin nutsuwa da Kamala tareda tsagwaron ilimin Daya ratsashi duk da akwai sauran rashin hayaniyar ciwon da yayi.

Sakin mashin din Hafiz yayi sauran kadan su kife yayi saurin riqe kan mashin din Yana kashewa muryansa na rawa ya amsa da cewa

"Sir Omar Kaine???

Wani kukan da Babu Shiri na farin ciki ya fashe dashi Yana sauka kan mashin din ya koma gefe tareda sunkuyar da kan Yana kuka Mai ratsa zuciya Dan kashe wayar ma yayi Dan bazai iya kukan a kunnen Omar ba.

Sake Kiransa Omar din yayi sai alokacin yaga numbern Nigeria ce take ya qarasa rudewa kukansa na qaruwa ya amsa.

"Hafiz Address naku kadai zaka tiro yanzu zan sameku aduk inda kuke indai a Nigeria ne,
Sbd sakonka da muka samu a shekaran jiya yau dinnan na sauka Ina Nigeria da kaina zan daukeku dukanku mu tafi inda ya kamata."

Hawayen Hafiz qaruwa sukai sbd harya cire tsammanin samowa yar uwarsa kudin da dole zaa buqata.

Hannuwansa har rawa sukeyi ya rubuta komai ya turawa Omar din tareda share hawayensa ya buga mashin da Dan abinda ya samu na cinikin dayayi ya buga wayar Babbah ya bisu zuwa asibiti.

Yana Isa asibitin ya tararda ance Aiko zaa yiwa Ameenatou din Dan haka hankalinsa yayi mummunan tashi take damuwansa da radadin zuciyansa suka ninku.

Dadah idanuwanta wata irin bushewa sukai hakama Babbah kowannensu kallo Daya zakai masa ka hango tsagwaron damuwa da qunci tattare dasu.

An samu anbata taimakon gaggawa nakudar ta Dan lafa Dan haka akace su tafi su Nemo kudin aikin kafin dare.

Babu zabin Daya wuce Babbah fita zuwa nema Shima Hafiz fita yayi cikin ruwan saman suka ringa yawon Neman kudi,

Dadah da aka bari kuwa zucuyarta sai tsinkewa takeyi sbd fargaba da tsoro tareda tashin hankali.

Duk ruwan saman da akeyi akan Babbah da Hafiz suka qare Dan haka tini Babbah ciwo yafara kokarin rufesa Amma ya danne yaci gaba da yawon daqyar ya hada dubu 7
Shikuwa Hafiz karshe dai guraren 9 na dare mashin din nasa ya siyar ya nufo asibitin hankali tashe jikinsa har wani rawa yakeyi sbd tashin hankali,yunwa kishirwa da zazzabin dukan ruwan Daya wuni yanasha.

Shigowansa asibitin yayi daidai da shigowan wata fitinanniyar motar da kaf asibitin Basu taba samun ziyarar Bako Mai irinta ba ta shigo asibitin tareda parking.

Ahmed ne ya Bude kofar gaba ya fito a natse cikin blue shaddda me tsananin tsada sai kofar Baya da aka Budewa farin kyakkyawan dattijon da kwatjinsa ya cike gurin gabaki Daya.

Babbah ne dayake zaune Yana rawar sanyi zuciya na cikin qunci yafara ganinsa bakinsa na rawa ya furta "OMAR"

dadah ce ta juya da sauri ta Kalli gurin hakama Hafiz cak ya tsaya daga inda yake tsaye cikin tsananin mamakin Daya Sakasa sakin ledojin hannunsa Yana kallan Omar din zuciyarsa na cika da dukkanin farin ciki.

Shi kansa Omar dukkaninsu yake kallo yanajin Kauna da tsananin tausayinsu Yana yanka koina nasa yanajin tabbas alkwarin daya daukarwa kansa na bazai sake rabuwa dasu ba har abada Yana sake ratsashi sbd lokaci yayi na ya bayyanawa duniya yarsa dasu Babbah a matsayin ahalinsa na jini Dan kuwa Dadah kamar jininsa take tinda kanwar kasim dinsa ce.

Tin kafin ya qaraso gurinsu wata nurse ta fito a masife tana cewa


"Ina iyayen Ameenatou Nuhu Babbah?
Kun shirya kokuwa haryanxu Baku samo kudinba mu kyaleku duk abinda ya sameta ko babyn laifinku ne,
Idan Kun samo kudin kuje ku biya komai Nan da awa Daya zaa shiga da ita tiyatar."


Juyawa tayi ta shigewanta ciki.

Kasa motsi Omar yayi hakama Ahmed sbd Jin Abinda nurse din ta fada.

Babbah ne da tashin hankali da masifar tayi masa tareda tsananin ciwon dayaketa dannewa tin dazu suka Fi karfinsa ya yanke jiki ya Fadi a gurin.

Taimakon gaggawa aka fara basa batareda an tsaya zancen komaiba Kuma Ahmed take ya gabatar da komai suka dauke Ameenatou da cikinta ya Saka Dad dinta kusan yanke jikin Shima Amma ya daure suka kwashesu daga asibitin ko wata asibitin Basu tafi ba ticket kawai suka Siya suka wuce abuja direct dasu Hafiz kawai aka bari ya hado duka sauran takardunsu da abubuwan buqatansu ya biyo bayansu da tsakar dare Shima ta jirgin.

Suna Isa abuja Kai tsaye wata tsadaddiyar asibiti aka wuce da Ameenatou din wadda ta qarasa gabaicewa sosai,

Duba da yanayinta Babu bata lokaci aka shiga Cs da ita shikuma Babbah dubasa Akai tareda Kwantar dashi a Wani lafiyayyan daki acan sama Mai komai a tsare kaman ba asibiti ba.



*********
Anyi CS din Ameenatou lafiya an Ciro mata lafiyayyan baturen Babynta Namiji Wanda girmansa kadai zai sake tabbatar maka sa lafiyayye ne.

A hannun Alh Omar jden aka miqa babyn wanda yake kamanni Sak da Ameenatou din sedai haskensa yayi yawan da yazo a bature sosai sbd gashinsa ma ba kaman na babies dinmu bane.

Shiru yayi tareda zubawa babyn idanuwansa jikinsa na sanyi Amma Kuma har cikin ransa yakejin kaunar babyn tinda ya Riga ya kasance jinin Ameenatou dinsa Dan haka baida zabin Daya wuce ya kaunacesa koma waye ubansa Dan yaji bayanin komai a bakin dadah da Hafiz.

Babbah Yana Dan Jin jikin sosai Dan haka shi hutawa sosai aka barsa yayi ya samu ya warware.

Ameenatou ma Ko data farfado har lokacin Hawaye ne ke gangarowa

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login