Showing 72001 words to 75000 words out of 261814 words

Chapter 25 - AMEENATOU

Mamuhgee   

21 Nov 2024

9940

da aketa kokarin farawa gadan gadan.

Su mum Atee dasu mummy Sarat da jamaarsu sun kawo lefen auren Wanda ya amsa sunan lefen gaske na auren masu abun duniya Dan kuwa sosai dadah da umman fadila datazo tarbon lefen sbd Jamaal da siddeeq harma da Haroon din suka girgiza da tarin kayan da aka kawo din tareda wasu mahaukatan sarkokin Dalma(zinari/gwal/gold).

Da dadah da umman fadila sai Jamaar amanar dadah biyu da suka taho bikin Tim daga Nasarawa Dan lasa arzikin Suma da Kuma tabbatarda amanarsu Dan idan Basu taho auren budurwan gidan Babbah ba yar gaban goshin dadah dasu Hafiz ai basuyi komaiba.

Duk da basuda wani karfi Saida Babbah ya fidda kudi masu Dan kauri a Dan abinda suke Tarawa na bikin ya Bada tukuicin da sedai masu aikin da sukai shigo da kayan ne suka karba Amma mum Atee Sam kin karba sukai suna nuna ai ba komai bazasu karba tukuicin ba bayan a cikin ransu dukkaninsu qyanqyamin taba kudin ma sukeyi sbd Yan dari biyar biyar ne a hade dubu hamsin cif.

Su umma anan duka wuni sunata duba kayan har dare suna sake Saka albarka da adduar fatan farin ciki me dorewa a auren.

Washe gari masu gyara na musamman aka turowa Ameenatou wadda za'a fara gyarawa Tin daga satin har satin auren Wanda ya rage saura sati biyu cif.

Ranar farko da aka fara yimata gyaran ta fara sauyawa abinta sbd fatarta irin me santsin Nan ce dake karban komai da wuri,

Farin ciki da dokin datake ciki itada Haroon ya wuce duk inda ake tinani sbd karfi da yaji duk yanda Babbah da Dadah suka Kai basa ganin laifi ko illan komai datakeyi Saida suka ringa Jin kunya da mamakin irin son datake wa Haroon Wanda ya Sakasu shiga tsoro da duqufa da adduar Allah yasa irin girman son dayake mata ya tabbata a rayuwar auren nasu yakuma barsu tare har karshen rayuwarsu.

Haroon a wannan lokacin yana cikin kwanakin farin cikin rayuwarsa me tsananin gaske da Bai taba samun kansa a cikinsu ba Wanda Hakan ya sanyaya zuciyar 'dan uwansa da mahaifiyarsa akansa wadda Bata isoba har lokacin Amma ta sheda farin cikin Da Haroon dinta yake ciki Wanda takejin a matsayinta na uwa a garesa tayi missing Daman basa wannan farin cikin dasuke Gani tareda shi sedai tana Jin dadi har ranta daya samesa sanadin macen dayakeson.

Jamaal tausayin dan uwan nasa ne ya Sanyaya zuciyarsa bata cikin farin ciki ko walwala kwata kwata Dan Bai taba ganinsa a irin wanna kyakkyawar yanayinba tsawon rayuwarsu Dan haka yake tayasa farin cikin Samun abinda shi Bai samuba Dan kuwa a nasa labarin Bai taba samun farin soyayya a tareda wadda yaso din ba, duk lokacinda suka dauka a tare lafiyanta koyaushe itace abinda take gaban soyayyarsu Dan haka har suka rabu Basu taba samun kansu a cikin irin wannan farin cikin ba Dan haka baisan Menene yanayinba da yanda ake samun Kai acikinsa.

Koda yaushe a waya suke maqale da juna suna magana tana nuna masa duk abinda akai mata na gyaran Amarya Wanda kullum take sake sauyawa sosai tana fita budurwan datake cikin Hutu da gyara sosai Dan tinda suka taho Lagos din Bata sake fita ko gate ba daga gyara sai Hutu da AC datake Sha da lafiyayyar abinci me gyara jiki take ci.

Har lokacin Bai dawo ba Haroon din Yana Nasarawa n Abuja aikinsu gap yake da kammaluwa Wanda yake Jin kaman Yana Neman rasa kansa kafin gama aikin ya koma Lagos din.

******Su Dad so biyu suna turawa Omar jeden gayyatarsa a matsayin Wanda zai karbanwa Haroon din auren Amma Yana toshe buqatansu ta Hakan sai gashi hankalinsu Yana Neman tashi da Hakan Dan haka Kai tsaye Mam yayi masa maganar Amma still dai ayyukan gabansa bazasu basa Daman zuwan ba ya sake Bada uzurinsa sbd Koda suke maganar ba Baya Nan Yana Japan Dan haka Kai tsaye ya Saka Ahmed ya tura musu zunzurutun kudi a matsayin gudunmawarsa data Saka su Dad din shiga mamaki da baqin gaske me tsanani.

Tsaban kudin suka kalla suna sake shiga qyashin gaske da bakin cikin irin yanda ya debo kudi irin wannan me yawa ya Basu kusan 500m as gudunmawarsa.

Shiru Dad Lameenu yayi lokacinda suke cikin tinanin abinyi gameda baqin cikin da Omar yake Neman sakasu Dan kuwa idan har zaayi auren Nan Bai tahoba tabbas Babu amfanin yin auren babba a garesu Dan duka kudi da dukiya me yawan da aketa zubarwa ana Shirin auren da akeson duniya ta sheda auren SEELAHs duk Dan sbd Omar din yazo ne Amma Kuma komai Yana Neman lalacewa a daidai lokacinda Babu time na Neman mafita ko gyara.

Mam da hankalinsa ya rabu biyu a yanzu akan yanda komai na ayyukansu ke tafiya daidai da Kuma sauyin Haroon Daya fara Sakasa Jin so da kaunan Dan nasa me tsanani na cikeda sedai Kuma Yana shakkar Shima yazo yayi auren mace ta sauya masa shi yazo Kuma baida abinda zaiyi masa barazana dashi Dan tankwarasa Dan haka gaskia gwara ya kama dukiyan dayake son kamawa Koda yayansa sun juya masa Baya yanada abinda bazai taba Jin zafi ba.

Lameenu wani numfashi ya sake Yana dagowa ya Kalli Mam da Shima yake Nisa cikin nasa tinanin ya sauke numfashi Yana ajiye wayar hannunsa daya gama da BB akan a Turo Yan jarida gidan Babbah zasu tafi Kai masa ziyara Yana son a yada abinda ya hadasu din sbd Omar yaga abinda sukeson ya Gani.

Mam da Baisan me Lameenu ke nufi ba yace

"Kayi duk yanda zakayi Omar yazo kasar nikuma wanna Karan nayi alkawarin cike aikin komai da hannuna batareda matsala ko dayaba wannan alkawarina ne."

Murmushin Daya tsaya iya fuska lameenu ya sake Yana Jin dadin Hakan Dan yasan aikin da Mam yasaka hannunsa da kansa aciki kaman cikan alkwarine Da Baya tashi cikar wannan aikin Dan haka ya sake murmusawa Dan shi a nasa bangaren ya gama yadda da indai akwai abinda Babbah ya sani gameda Omar da abinda ya Haifa to tabbas Omar Saiya taho wannan auren idan yaga Babbah a tareda su din.

****Da yamma a gidan Babbah Dad Lameenu yayi Sallah tareda su a masallaci bayan sun Dade suna tattauna maganar daurin auren ya bawa Ameenatou kyautan motan da ita aka taho gidan wadda ta tareda katin gayyatan da aka bugo na musamman me tsadan gaske.

Yan jaridan da BB ya turo sun dauko bayanan da yiwa motar hotuna da Kuma yiwa Babbah da Alh Lameenu din hotunan da suka fito da kyau.


Babbah Bai karbi motan ba ya Saka aka mayar akan bayan auren idan Ameenatou ta dawo hannunsu an Bata acan.

Dayake ba damuwa Daman sukai da lamarin ba Yana dawowa da ita aka ajiye kawai sedai a Daren aka hada labarin dasukeson a hada dauke da hoton Babbah Dana Dad Lameenu suna dariya cikin farin ciki dayake nuna shakuwansu da kusanci sosai.


Washe gari bayan Dad Lameenu din ya gama karantawa kallan fuskanta Babbah yayi wadda ta fito da kyau akan

"mahaifin Sirikitar Seelahs Mal Nuhu babbah ya nuna farin cikinsa da Jin dadinsa ga kyautan motar da sirikansa da kansu suka kawiwa yarsa har gida amatsayin tukuicin auren dansu"

Kai tsaye tareda invitation dinsu na musamman na auren da hoton dayake dauke da wainnan bayanan ya Saka aka yada kafin kace me labarin ya fara yaduwa har inda basa zato.


********
_Greece_

Dattijo ne Dan zaka zama confused akan shekarunsa and Hutu da wayayyar ilimin data gama ratsa rayuwansa Tako wanne Sako ya koma half bature kwatakwata.

Zaune yake a cikin lafiyayyar balcony din gidansa Mai tsananin yalwa da tsari irin na masu kudin gaske dayake Shan iska Yana sanye da farin glass Daya qarawa farar fuskansa kyau sosai da qara fitarda sirrin kyau da Kwanciyar hankalin da Allah ya wadacesa dashi yana karanta mahimman bayanai a Apple iPad datake hannunsa kafarsa Daya na kan Daya hakama gabansa table ne da laptop take Akai a Bude da alama itama wani sakon ya karanta kafin daga gefe qaramin tea cup ne Daya Sha coffee yabari a gurin.

Ahmed ne da Shima ya sauya sosai kaman wani lafiyayyan dattijon bakin bature Shima Hutu da kudi sun ratsashi ya iso gurinsa Kai tsaye da tasa iPad Shima a hannunsa.

Yana isowa kafin yace komai iPad din ya jiye a gaban Omar jeden Kai tsaye Yana cewa

"Ya kamata kaga abinda yake faruwa" ya nuna masa screen din iPad din.

Idanuwa Omar ya juya akan iPad din yana zare farin Glass din idanuwansa idonsa Kai tsaye akan fuskan Babbah da suketa azaban nema ya sauka a tareda Lameenu a gefensa suna dariya cikin farin ciki da shaquwa.

Hannuwansa Dake rawa ahankali yakai ya dauki iPad din a hannunsa Yana kafe hoton da ido kafin idanuwansa suka gangara akan abinda yake rubuce Wanda shine yake Saka Ahmed zufa da motsawan zuciya cikin tashin hankalin da Bai taba tinanin samun kansa ba.

Alh Omar Dayake Neman kasa gane komai saurin miqa hannu yayi Yana Neman ruwan Sha sbd yawunsa da suka qafe take.


****
SEELAHs sun shiga satin farin cikinsu Dan aikin project ya kammala an kaddamar
Fadan farin cikinsu Baya yiyuwa musamman Dad Lameenu dayake ganin sun tsallake rijiya da Baya Dan haka sune cikin farin ciki sosai.

Haroon sosai ya samu lambar yabo da karramawa tareda burge abokan huldodinsu da yawa ciki hadda turawa da yawa da suka yaba da aikin Dan haka take SEELAHs suka ringa samun manyan proposals masu zafin gaske Daya Saka su Jin duniya ta sake dawowa hannunsu Kuma a cikin satin suka samu sabuwar babbar Hulda daga Ashalawa wadda ta sake Saka kan Lameenu gigicewa shi Kuwa Mam a yanzu alfaharin gaske yakeyi da Haroon Wanda yake cikin farin ciki Shima sosai ya ringa Jin kaunar Dan uwansa na sake kere dukkanin abinda yakeso a rayuwarsa.

Dan haka a Lagos aka shirya hadaddiyar lafiyayyar dinner da aka barar da mahaukatan kudin gaske ta kammaluwan aikin.

Kusan duk wani babba dayaci ya tayar da Kai dayake mu'amalantar seelah ko sanatayya ya halarci dinner din wadda aka sakawa matakan tsaro da securities sosai.
Karfe goma Sha biyu da kusan Rabi aka gama dinner din wadda tsarinta yake na asalin Yan boko da masu kudin da muqami sai business tycoons kowa ya watse.

A daidai wannan lokacin da aka gama dinner din seelahs a wannan lokacin ne jirgin Omar jeden ya sauka a Abuja Nigeria.
#MAMUH#


*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
47
Sabon drivern da suke tareda shi tin Baya Wanda dashi kadai Ahmed ya yadda yayi contacting Tin kafin zuwansu ayau din aka tanadi lafiyayyar motan da zata daukosu daga airport har Mansion dinsa Dayake jere Dana Yan uwan nasa.

Babu amfani ko kadan ga gujewa zama gidansa dayake hade da masu tinda abinda yafi so da kauna duniyarsa fiyeda komai ta riga ta shiga hannunsu Dan haka ya yanke shawaran tinkaransu kaman yanda suka tinkaresa Dan yasan Nemansa ne sukeyi Kai tsaye shiyasa suka bayyanawa duniya fuskan Babbah Dan ya Gani duk da baida tabbacin sun gane asalin waye 'yarinyar da suke Shirin aurawa dansu din Hakan yake son tabbatarwa Dan baida ikon kowanne irin motsin da zai Saka babynsa a hadarin da zai illata masa ita sbd a yanda aka kawo sauran kwanaki ne kadai suka ragewa auren bayajin Babbah zai fahimci abinda yake son ya fahimta Amma dai Kuma bayajin har abada zai iya bayarwa ko barin 'yarsa da ita kadaice jininsa Kuma Jaden daya data rage ta shiga hannunsu Mamman.

A cikin Daren su dukkanin iyalan seelahs da suka dawo suka tararda koina na wutar mansion din Jden a kunne ta haskaka koina na zagayen gidan Wanda Hakan ya tabbatar musu da an kunna switch na wutan gidan gaba Daya dayake kashe hakama securities ne na musamman koina zagaye da gidan Wanda Koda suka fita hidiman bikin Babu ko Daya a mansion din.

Babban abinda ya sake raya mansion din shine matar Ahmed da yayansa biyu dasuke tareda su duka a cikin gidan Dayake kusan tsarin Mansion dinsa na can Greece Dan haka a cikin Daren ma'aikatan da duka aka Riga aka tanadar musu suka iso gidan cikin abinda Bai wuce awanni ba aka hau aikin gyaran gidan kafin su iso shiyasa Koda suka iso komai tsaf Babu abinda yake tashi sai kamshin freshners dana manyan humidifiers dana burners dayake tashi a duk inda ka Saka kafafunka da sanyin ACs da Suma suke aiki.

Ma'aikatan kusan guda biyar ne aka kawo dukkaninsu mata sai namiji Daya da shikuma harabar Mansion din itace tasa.

Mum Noor matar Omar da har lokacin ta riga ta rasa cikakkiyar lafiyanta akan abinda ya faru Bata Gani sosai hakama Bata iya tafiya sai akan wheelchair itama hakanan suka taho sbd yazo da niyar zama ya fuskanci wainda suke son fuskantarsa Amma zuwan na yarsa ne Daya danne dukkanin abinda yake ji akanta tsawon shekarun ya nesanta da ita sbd Bata kariya da rayuwar Kwanciyar hankali batareda tsoro ko fuskantar hatsarin dayake tattareda wata dukiyar ba,

Taimako da kyakkyawar rayuwar dayaso Basu itada su Babbah duk ya danne kansa ya janye daga garesu sbd koma huldan dazaiyi dasu a boye su Mam zasu iya bibiyan Hakan su mata illa.

Yayan Ahmed ba wani shekaru ne dasu ba sbd ya Dade sosai sosai baiyi aureba har Saida ya fara manyanta ma Dan haka suke Yara daidai kusan Ameenatou din Amma tama girmesu da shekaru biyu zuwa uku haka Dan babbar kenan sai namijin Wanda duka duka yanzu yakeda 10yrs zuwa 11 Dan haka masu aiki tini suka fara kokarin kaisu dakinsu Dan taimaka musu dasu wanka da sauransu.

Mai aikin da itace kaman babba a cikinsu sunanta Zahida itace ta Kai kayan kowannensu dakinsa ta fito ta nufi dakin yar budurwan wadda batasan sunanta ba Saida taji mom dinta ta ambaci sunanta da Fatmah kafin ta kama itama.

Abincin alfarma marasa nauyi irin Wanda sukasan zasu iya ci ne dayake dukkanin masu aikin kwararri ne aka dauko wainda albashinsu ma na musamman ne suka jere a makeken dining din Wanda Babu abin buqatan ci da Sha da baa jere ba cikin tsari.

Alh Omar ne a sama gaba Daya da mum Noor
A qasa Kuma Dayan bangaren Ahmed da nasa Iyalin ne dakin Fatmah daban hakama dakin Arfat daban.

Dukkaninsu Babu Wanda zai iya cin wani abinci a Daren sbd gajiyan dasuke tattare da ita,basa wani Jin yunwa sbd sunci snacks dasu tea da sai sauransu a jirgi so basa wani Jin yunwa Hutu kawai suke buqata.

Arfat da Bai Saba da koina ba hasalima shi Bai taba zuwa Nigeria ba tinda aka haifesa Dan haka kwata kwata qin yadda masu aikin su kusantosa yayi wanka yayi abinda ya shirya cikin kayan bacci ya fito ya nufi dakin Fatmah ya kwanta tareda ita itama duk da Bata san Kwanciya dashi Amma sbd bakuntan gidan ya Sakata kyalesa bayan sunyi sallah tea me zafi ta buqata daga masu aikin kawai Tasha ta kwanta.


Duk yanda Mam suka shiga mamakin abinda yake faruwa Basu nemesa ba sbd dare yayi Suma Kuma a matiqar buqatan hutun suke sbd hidiman da aka Sha Dan haka suka bari zuwa da safe Dan tabbatarda idan Omar jden dinne ya sauka Nigeria.


******Washe garin ranar da mamaki kowa ya wayi gari da ganin dawowan Wanda baa taba tinanin Gani ko yaddar zai dawo din ba wato Alh Omar jeden seelah wadda tini labarin ya fara yaduwa.

Mam da Lameenu da kansu suka taho yi masa barka da sauka cikeda farin ciki Mai tsananin gaske da nuna yabawarsu batareda nuna komai a fuska ba,
Shima Bai nuna komaiba cikin farin ciki da nuna kewan juna ya bayyana farin cikin ganinsu.

Fira suka zauna sosai cikin kewa da murnan kasancewansu tare da juna a yau din bayan tsawon lokaci sun Hadu a matsayin brothers da aka Sansu.

Mum Noor Bata nuna komai ba sbd ba komai ma ta sani ba Dan haka sosai aka Hadu anata murna da farin ciki musamman dasu mum Atey suka shigo hakama su mummy Sarat ma duk sun shigo hadda su Aliyah anata murna harma da matar Ahmed Aunt Didi Wanda take wayayyar mace sosai Kuma ta waye ga ilimi Dan haka ta saki jikinta ta sake acikinsu.

A tare duka ahalin sukai breakfast qatuwar dining din gidan Dad Omar ana sake tattauna bayan rabuwa da Kuma murnan auren Haroon Daya sake hada auren.

Bayan breakfast shigewa su Dad suka sake yi Babu Wanda yake jinsu suna palonsa anata maganganu.

Su mum Atee ma sun jima sosai kusan a gidan aka wuni gaba Daya sai daga baya kowa ya koma masu fita Kuma irinsu Aliya tini ta qara gaba duk da Dad Omar tana yinsa sbd Yana kaunarsu sosai hakama wasu lokutan idan ta Kalli tazarar dukiya Dan rayuwan dayake da shi da 'yannansa su Dad dinta sai take Jin inama shine ya haifeta gashi a waye fiyeda Dad dinda da ilimin da kallansa kadai zakai kasan ya gama shigarsa Tako ina.

Sai dare Jamaar gidan suka samu Hutu da gidan yayi tsit sukaci abinci gaba dayansu a dining kafin kowa ya shige dakinsa yayi wanka ya kwanta Dan samun hutawa.

Washe gari Haroon ne da Bai samu zuwa ba jiyan ya taho yayiwa Dad din sannu da zuwa cikin farin ciki sosai.

Zuba masa idanuwa Dad Omar din yayi Yana karantarsa cikin nutsuwa da kulawa a matsayinsa n Wanda zai auri yarsa ta cikinsa.

Haroon sosai yake kauna da girmama Dad Omar shima Amma Kuma kusanci da kaunan Dake tsakanin Jamaal da Dad Omar din Babu Wanda zai iya shiga ko samun irinta Dan haka Shima Omar yake kaunar Haroon har ransa sbd kaunar dayakewa Jamaal da Dr Aleena Amma Badan mahaifinsa ba.

Haroon ya Jima a gidan Shima kafin ya fito Kai tsaye ya nufi ganin amaryansa.

A Daren Ahmed da Omar suka fita sedai Bai nufi gidan Babbah Kai tsaye ba Wanda suka samu bayanin komai nasa da gidansa,
Zuwa gidansa Kai tsaye yanada hadari Dan haka masallacin da babban yake sallah ya nufa Dan yin sallan ishai acan.

Babbah tareda Abdul da Hafiz suka fito daga gida suka nufi masallaci kowanne da sauran ruwan alwala a fuskansa Hafiz na latsa wayarsa Babbah na masa maganar meyasa yake zuwa

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login