Showing 156001 words to 159000 words out of 261814 words
Abdul sbd yasan shikam ya huta inshallah Yana cikin rahamar Allah Amma a duk lokacinda ya Kalli yanda suke fama da Ameenatou idan rikicin ciwonta ya tashi akan sai ankaita gurin Jamaal ko sister Ashley sai yaji ya sake tsanar duka wanda yake ahanlin seelahs.
Sunsha fama da tashin hankali da damuwa akan Ameenatou da ciwonta farko farkon dawowansu da ita har suka Saba suka fahimci abubuwan datake so da Wanda bataso,
Kullum duk tsanani duk rintsi sai Hafiz ya shigo mata da kayan tea da fruits sbd sune abinda take ci Sam sam Bata Wani son abinci sai an hada da dubaru da Kiran Ashley take ci..
Duk Wani tsananin so da kulawan da suke Bata a abaya a yanzu data koma haka sai suka ninku sbd ko quda da sunada hali bazasu so ya sauka a jikinta ba,
Tattalinta sukeyi tareda tsananta nema Dan hada abinda zasu samar mata lafiya,
Hafiz aiki yakeyi tuquru tareda Neman Aiki da takardunsa,hakama Babbah ya sake ya qara samun lafiya sosai yafara fita Neman Shima.
An dauki lokaci Dan haka itama Ameenatou din tini ta sake a cikinsu hankakinta ya kwanta Kuma ahankali ahankali sai tana samun sauki kanta na sakewa harma kaman tana tinawa Kokuma kokarin Tina abubuwa da dama na rayuwarta.
Hafiz ya Dade komawa mutum me Tsananin zuciya da son 'yanta Kai,
Abinda ya samesu ya tabasa sosai tareda sauya masa rayuwa,
Rayuwa yakeson shi da iyayensa da yar uwarsa suyi kaman kowa,
Rayuwa yakeson suyi ta yanci da tsayawa Kai,
Rayuwa yakeson suyi batareda tsoron kowaba ko shakkar kowane lokaci Wani abu zai iya samunsa,
Bazai taba iya yadda suci gaba da boyo suna yawon garuruwaba sbd suna tsoron rasa rayuwarsu ko Kuma 'yar uwarsa,
Radadi da zafin Hakan sune suke cinsa Akoda yaushe dasu yake kwana dasu yake tashi,
Idan Yanason bawa rayuwarsu cikakkiyar kariya da yanci to dole ya Tara nasa abin duniyar Shima Dan haka bayaji Baya Gani bayan aiki da Neman kudi kawai.
*******Dadah tinda suke indai zataiwa Ameenatou wanka a zaune take zaunar da ita a kujera da pant da halfvest a jikinta take mata wankan Dan haka Bata taba lura da yanda cikinta yake ba sai yau.
Zaunar da ita tayi taje ta dauko ruwan wankan tana ajiyewa Ameenatou ta zabura da sauri ta miqe tsaye daga ita sai halfvest da wando sbd kyankyason Dayayo cikinta daga karkashin bucket din.
Cikinta ne ya fito sosai fes dashi Wanda duk dare ta kwanta Bata iya Kwanciya daidai ya ringa juyi kenan tana jujjuyawa sbd rashin Jin dadinsa a jikinta Amma batasan me zatace ba Dan batama San wani abu a jikinta ba na Wani ran.
Makancewa Dadah take Neman yi gurin Bude ido da kafawa cikin Ameenatou idanuwanta gabanta yayi mummunan faduwan da sauran kiris paralyze ya kamata.
Sake yankewa gabanta yayi ya Fadi tana matsowa gurin Ameenatou din idonta a cikin Wanda yafara tsayi ya fito sosai.
"Innalillahi wainna ilaihirrajiun"
Hannunta dayayi mata wani irin nauyi sbd tashin hankali ta daga ta nufi cikin ta Dora Akai tareda dannawa kadan tajisa da taurin gaske,
Kafin ta cire hannunta Akai Ameenatou ta Dora hannunta akan na Dadah din tana cewa
"Babyn Ameenatou inji Ashley,
Ashley tace Babyn Ameenatou kada kowa ya tabasa.......
Yanke jiki Dadah tayi a bakin toilet din tsakar gidan ta zube qasa zaune jikinta na wata irin rawa sosai zuciyarta na tsananin bugun datake Neman bugawa.
Bakin na rawa tace
"Me kikace?
Zaunawa a kujeran wankanta tayi tana cewa
"Ashley tace baby ne anan Kuma babyn Ameenatou ne"
Hannu Dadah ta Dora Akai tanason fasa ihun tashin hankali Amma Kuma batasan ma me zata fada a cikin ihun ba.
Babbah Baya gidan hakama Hafiz bare a taimaketa da radadin dayake Neman illata ganinta da Jinta,
Rarrafawa tayi ta dafa ta tashi sbd kasa yadda dataji tanayi da wannan mugun fata da mafarkin.
Hannuwanta na rawa jikinta Babu karfi ko kadan ta danne abinda take ji Akai wankan tana kasa kallan cikin Dan tsoro ma takeji fatanta zancen rashin hankalin Ameenatou dinne kawai take maganar baby a cikinta duk da girman cikin ma ga fada Hakan Amma bazata iya yadda cikin mutum na haihuwa ne a jikin 'yar yarinyarsu ba da batama cikin hankalin kanta.
Kwata kwata ba nutsuwa ko Kwanciyar hankali ko Daya a tareda dadah suka fito ta shiryata cikin doguwar rigar material da Hafiz ya siyo mata su a kayan sawa tinda batada wasu kayan a tareda su.
Duk yanda taso dafa abincin Rana kasawa Dadah tayi sbd zazzabi ne na tashin hankali ya rufeta take,
Tea kawai ta hadawa Ameenatou din ta Bata tana sake zurfafa a tinanin abubuwa da dama da Suka sauya daga Ameenatou din Daya kamata ace sun gane Amma sbd ganin rayuwarta ma ta sauya gaba Daya ya Sakasu daukan duka akan kanta ne Daya juya.
Karfe Hudu na yamma Babbah ya dawo gidan dauke da ledan fruits Daya siyo a hanyarsa ta dawowa daga inda ya samu Yana Dan shiga kasuwancin dabbobin Daya Saba.
Zazzabin Daya tarar da Dadah ya Sakasa mamaki Yana zaunawa yace
"To lafiya dai kuwa?
Meya sameki ne tinda lafiya kalau muka fita muka barki kina aikin gidan,
Ko cizon sauro ne? To Amma Kuma ai bamada Wani sauro tinda Akai akai anawa gidan feshi sbd yar buduwata da banason sauro ya ciza"
Ajiyan zuciya ta sauke idanuwanta sai a lokacin suka cika da wasu hawaye masu tsananin radadi da ciwo ta dago ta Kalli Ameenatoun Dake kwance tana bacci ita Kuma tanai mata fita.
Ajiyan zuciya ta sake saukewa a Karo na uku kafin ta dago ta Kalli Babbah Daya zuba mata ido Yana jiran abinda zata fada Dan bayason delay a gurin Bada labari ko Fadar Abu.
Sanyi jikinta yayi hakama muryanta tace
"Babbah Ameenatou ciki ne a jikinta ga dukkanin alama Dan ni dai na kasa tabbatarwa a rude nake Kuma itama da kanta tace baby a cikin Ameenatou....."
Kallan Ameenatou din yayi kafin ya juyo da kallansa kan Dadah yace
"Meyasa haryanxu kin kasa sabawa da yanayin tashin lafiyanta,
Kinsan yanzu batasan me take fada ba batasan Menene wannan ba bare wancan."
Girgiza Kai dadah tayi idanuwanta na sake cikowa da Hawayen da suka gangaro mata tace
"Ciki Kam akwaisa da alama Dan gashinan a bayyane harya fito Dan kuwa da alama zaiyi wata hudu komai fiye,
Kullum saitace cikin Ameenatou tsalle sosai na dauka idan tana Jin yunwa take Fadar Hakan shiyasa duk ta fada saina Bata Wani abin taci da alama Motsi ne yake mata.......
Ajiye kankanar Daya dauka zai Sha Babbah yayi Yana sake kallan Ameenatou din dakyau ya dawo da kallansa kan Dadah idanuwansa na sauyawa yace
"Wai maganar me kikeyi??
Cikin haihuwa ko me??
Gyada Kai tayi hawayenta na sake gangarowa.
"Ni bangansa ba to" ya fada muryansa na sarqewa.
"Nima wlh bantaba Gani ba sai yau Amma wlh Babbah naga ciki me girma Kam ni Amma na kasa yadda da cikin mutum ne a jikinta,
Nidai muje asibiti a duba mana Dan jinina Neman Hawa yakeyi da wannan babban tashin hankalin dayafi kowanne dayake Shirin bayyanar mana"
Wani azababben zufan tashin hankali ne ya fesowa Babbah lokaci Daya a ko Ina jikinsa,
Hannunsa dayake Dan rawa yakai goshinsa ya share tareda qurawa Ameenatou idanuwansa dasuka qarasa sauyawa gaba Daya suna yin wani Jan tashin hankali da masifa.
Kaman tasan abinda ake ciki ta juya Kwanciyarta ahankali zuwa Dayan bangaren Wanda Hakan ya bayyanarda cikin sosai take Babbah ya sarqe da yawun bakinsa da suka kasa wucewa sbd muguwar bushewan da maqoshinsa yayi take.
"Innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Badai ciki ba wannan sedai koshi ne yayi mata yawa Amma tayaya zaa samu ciki a jikin yarinyar datake budurwa Babu miji,Babu hankali Kuma tana can killace asibitin da baama barin kowa shiga sai dole.
Wurgi yayi da kayan gabansa Yana miqewa tsaye jikinsa na sake jiqewa da zufa ya Saka takarmansa Yana cewa
"Shiryo asibiti zamu yanzu basai gobe ba"
Miqewa dadah tayi tareda shiga daki ta shirya ta fito ta dauko hijab ta tayarda Ameenatou ta Saka mata suna kokarin fitowa Hafiz ya dawo ya tsaya Yana kallansu cikin mamaki Amma Kuma ganin Babbah a mummunan halinda Bai taba ganinsa ba a ciki ya Sakasa Maida kallansa kan Dadah da jikinta yake a mace gaba Daya Babu kuzarin komai,
Ameenatou ya kalla itama yaga ita baccinta ne ma Bai isheta ba fuskanta duk a daure sedai itama a kasalance take.
Magana zaiyi Babbah ya dakatar dashi ta hanyar cewa suje kawai.
Ciki ya shiga ya ajiye ledan siyayyar kayan tea da wasu abubuwan Daya siyo ya fito ya rufe gidan ya biyo bayansu zucuyarsa Shima tini tayi nauyi ta shiga Wani mummunan damuwa Yana fatan ba wani abin ne ya samu Ameenatou dinba Dan zuciyarsa bazata iya dauka ba Dan yanzu haka duka nemansa akanta ne sbd ita yakeson yaga sun samu sauyin rayuwa itada iyayensu.
Mota Babbah ya tsayar ko Gani sosai bayayi sbd yanda zuciyarsa ke bugawa da hawan jinin Daya kamasa take Amma bazai iya tsayawa ba idan ba asibitin suka Isa ba likita ya kallesa ya fada masa gaskia duk da yasan gaskiyar zata iya illata rayuwansu gabaki dayansu Dan Ameenatou itace hasken zuciya idanuwansu da illa Daya gareta tamkar radadin mutuwa ne garesu.
Shiga motar sukai Hafiz na gaba ya kasa tambayar komai sbd fargaban abinda zaa iya fada masa duk da Bai taba kawo tinanin ciki ba sbd abune da yama manta da cewan ita macece ma gaba Daya.
Suna Isa asibitin Hafiz ya sake shiga rikitaccen tinanin ko Wani ciwon ne ya kama Ameenatou Dan haka ya matso da sauri ya kama hannunta Yana kallan fuskanta zaiyi magana Babbah ya silale qasa ya zauna Yana cewa Hafiz yayi komai likita zasu Gani yanzu yanzu.
Jin Hakan ya saki hannunta nauyin zuciyarsa na qaruwa ya Isa inda ake yanka Kati ya biya komai take aka Basu Kati sbd Babu layi Kuma asibitin private ne Dan haka duka abinda ya samo haka ya tattarasu Akai komai akace a shigo da ita.
Dukkaninsu suka shiga dakin ganin likitan.
Kallansu Dr yayi da mamakin ganin su dukan yace su fita ita kadai zasu bari.
Hafiz ne ya samu karfin yi masa bayanin matsalarta ta Rashin hankalin.
Hakan ya Saka Dr din Dan kallansu yace to yanzu Menene matsalanta.
Kallan Babbah Dadah tayi kafin ta Kalli Ameenatou din
Shi Kuma Hafiz su babban ya kalla Yana jiran Jin Abinda ya kawosu.
#MAMUH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
#ZafafaBiyar
96
*_AISHA's COLLECTION_*
Hajiyata Kinason kiyi kasuwanci amma bakida jari?
Ko kuma kinada jarin amma bakisan maiya kamata ki fara saidawa ba?
Tou hajiya nesa tazo kusa ga sauki yazo na kawo muku inda zaku samu kaya a cikin farashin sari,muna saida kaya kala-kala inda zaki samu a cikin sauqi da rahusa.Akwai varieties of women accessories ranging from Atamfa, Laces and shoes at both wholesale and retail..
Hajiya da kayan da kika sani da Wanda Baki saniba harma da Wanda Baki taba Gani ba na kayan alfarma da burgewa da asalin kyau na quality kizo karki bari ayi Babu ke,
ko kasuwaci ko sanyawa,ko ankon biki,lefen alfarma,kayan sallah..komaima namu inshallah na musamman ne da zakiji dadin kasancewa a cikin kasuwanci damu...
Join our group to see lot of our amazing products 👇
Location: LAGOS
We deliver nationwide
09013833502
https://chat.whatsapp.com/JRkPEIt0xVj2vuE8HAGRUL
*************
Cikin sanyi da nauyin zuciya Dadah ta Bude Baki tace,
"Cikinta ne muka ga yayi girma Kuma Babu rashin lafiyar komai"
Kallan Ameenatou din yayi kafin ya Kalli su Babbah yace su Basu gurin Abar Dadah kawai.
Fitowa sukai Babbah kirjinsa na wani irin toshewa,
Hafiz riqesa yayi sbd har lokacin Bai fahimci komai ba.
Zaunar da Babbah yayi batareda ya iya cewa komaiba sbd ganin lamarin me girma ne Dan ba qaramin lamari ke Saka Babbah shiga wannan mummunan halin ba.
Zaunawa sukai shiru shiru kowa da abinda zuciyarsa ke sakawa cikin damuwa da fargaba har tsawon mintina kafin aka fito dasu zuwa gurin scanning tareda Dadah wadda bata iya kallansu ba.
Can ma Basu Wani jima sosai ba suka dawo suka shige office din ganin likitan sai gashi Shima daga bayan ya dawo ya shige.
Dadah ce ta fito ta kira su Babbahn ciki.
Tasowa sukai suka shiga suna kallan Ameenatou Dake zaune duk zazzabi na Neman taso mata sbd bata Saba wahala ba hakama duk an cakuda mata ciki gurin scanning ga yunwa tanaji.
Likitan mamakinsa ya fara bayyanarwa tareda tambayarsu basusan ciki bane da tana dauke da cikin kusan wata BIYAR Amma ace Basu gane ba.
Fiddo idanuwa Hafiz yayi da sauri cikin tsananin tashin hankali da mamaki me karfi Ya kalli Ameenatou kafin ya Kalli Babbah da Dadah murya na sarkewa yace
"Ciki Kuma?
Cikin haihuwan 'yaya ko me??
Budurwan Babbah ake magana kokuwa wata daban??
Kukan da Dadah ta fashe dashi jikinta gabaki Daya Yana daukan rawa ya Saka likitan yin shiru cikin mamaki da tausayinsu Dan alama dai Wani ya lallaba cikin rashin hankalinta yayi mata cikin.
Daqyar Babbah ya iya Bude Baki da Dan karfin Daya rage masa yace
"Likita kace ciki?Kuma harna wata biyar?"
Ajiyan zuciya Dr ya sauke cikin sanyi kafin ya gyada Kai Yana cewa
"Eh inshallah"
Wani abu me nauyin gaske ne ya danne zuciyar Babbah Wanda ya Saka idanuwansa fara yin duhu Yana dafe kirjinsa.
Hafiz ne yayi karfin halin tare babban shida likita suka fito dashi Dadah kuwa kuka takeyi mara sauti tana share Hawaye.
Mota suka shiga da Babbah suka nufi gida Babu Wanda ya iya magana a cikinsu sbd babu Wanda zuciyarsa take bugawa daidai ko kadan,
Dadah sbd kuka Koda suka iso idanuwanta sunyi mummunan kumbura,
Hafiz kuwa idanuwansa ne sukai Wani mugun jajir hannuwansa na Dan rawa ya damqe takardan awon cikin datake hannunsa.
A tsakar gidan suka zauna kowa shiru Babu Wanda ya iya cewa komai har lokacin hakama Babu Wanda yake Gani ko ji daidai.
Wani radadi me tsanani idanuwan Hafiz keyi sbd abinda yake cinsu,
Zuciyarsa radadin Datake yasa har lokacin jikinsa yar rawa yakeyi,
Rintse idanuwansa yayi ya sake budewa sai kawai ya fashe da wani irin kuka Mai ciwo da radadin zuciya sbd ya kasa riqe abinda yake ji.
Kukansa ya Saka gidan ya sake daukan tsit hakama Babbah hawayen dayake riqewa ne suka gangaro masa Shima zucuyarsa na sake nauyi.
Kuka sosai Hafiz ke yi dukkanin jikinsa na jijjiga da rawa,
Duk masifar da suka shiga Bai taba kuka irin haka ba sai yau,
Kuka yakeyi sosai kaman ba namiji Mai karfin hali da jarumta ba.
Dukkaninsu kuka sukai Saida idanuwansu sukai jajir Ameenatou na zaune gefe tana Shan fruits itama jikinta a Sanyaye.
Sun jima a wannan mummunan yanayin kafin Hafiz ya miqe ya dibi ruwa a bucket ya shige toilet.
Wanka da alwala yayo ya fito ya shirya ya wuce masallaci sallan magrib da ake kira.
Babbah kuwa Saida Dadah ta taimaka masa ya samu yayi alwalan yayi sallan a gida Dan bazai iya fita.
Itama sallan tayi tareda Ameenatou Dake gefenta.
Shiru gidan yai Babu Wanda ke ko dogon motsi,
Saida Akai ishai Hafiz ya dawo gidan ruwa kadai yasha ya shige ya kwanta.
Ameenatou din kadai Dadah ta bawa tea Tasha ta shiryata ta kwanta Suma suka shige sbd Babbah tini ya shige sbd lafiyansa datake rawa tini zazzabi me karfi ya rufesa da nauyin kirji me tsanani.
Yanda suka ga Rana haka suka ga Daren Dan Babu Wanda ya samu bacci ya ziyarci idanuwansa idan ba Babbah da ciwo ya rufesa a cikin Daren Wanda daqyar sukaga safe suka tattarasa zuwa asibiti.
*******Jinyar kusan sati biyu Babbah yayi a asibiti kafin aka sallamosa suka dawo,
Hafiz Shima ciwon ne yake Neman kwantar dashi Amma yayi karfin zuciya yaqi barin Hakan sbd idan ya kwanta shine bangon gidan Dan komai shike nemowa Dan haka ya sake sakawa kansa karfin hali Amma zucuyarsa bata qara lafiya ba daga ranar da cikin Ameenatou din ya bayyana garesu hakama Babbah lafiya tini tafara masa rawa gashi sun rufe maganar cikin a tsakaninsu batareda sun tsaya Jan maganar inda cikin ya fitoba sbd cutace ta tabbata an musu mummunan illa,
Idan ma sunje asibitin wahala ce zasusha kudin ma zuwan Lagos a yanzu basuda shi hakama Babbah har abada bazai yadda a nunawa Ameenatou dinsa yatsa ba,.kaman yanda suka reneta Babu Uba Hakan zasu reni abinda zata Haifa Babu Wanda har abada zai San fyade Akai aka samesa matiqar Yana Raye.
Ta bangaren Hafiz ma yabar maganar ne a yanzu Badan yabarta har abada ba Dan kuwa duk Wanda ya keta haddin yar uwarsa bazai sake zaman lafiya ba a rayuwarsa daga ranarda yacika kudinsa na inganta rayuwarsu zuwa Wani matsayin.,,
Bazai taba barin a nuna Yar uwarsa da yatsa akan ta haihu ba sbd duk Wanda yayi Hakan zai iya komai akansa,
Amma Kuma a yanzu babbar buri da qudurinsa shine Hana Hakan faruwa ta hanyar Saka rayuwarta matsayinsa Babu Wanda ya Isa ko kallo biyu yayiwa abinda ta Haifa da wata manufar.
***********
Abubuwa sun fara yiwa iyalin gidan Babbah nauyi sbd Babbah da lafiya taqisa Sam Dan haka kullum a yawon Neman lafiyarsa ake asibiti
Hakama Ameenatou ma lafiya nata yin qasa sbd cikin da yanzu da gaske de ya fito tsufa yake yi,
Dadah ce a tsaye gurin hidima da Ameenatou da Babbah shikuma Hafiz gaba Daya ya koma abin tausayi sbd wahalar nema Dan cinsu da neman lafiyansu harma da sauran abubuwan.
Da kansa shi kadai yakai Ameenatou Akai mata register na awon ciki Yana Kaita duk bayan sati Daya sbd Dadah idan zasu barinta akeyi kulawa Da Babbah idan Kuma yaji sauki sai ita takai Ameenatou din awo.
Rayuwa tayiwa Hafiz nauyi sosai Dan Babu abinda yake kalla kaman haihuwan Ameenatou da Baya kaunar ko kadan tazo da matsala,
Hakama Babbah koyaushe maganarsa daya shine Hafiz yayi kokari ya tanadi komai kada Ameenatou ta haihu da matsala ko buqatan komai.
Duk yanda hafiz yake kokarin ganin samun aiki lamarin ya gagara Dan haka kullum yawon aikin karfi yakeyi shiyasa ba Wani abu yake samu ba duka wahalance yake koyaushe,
Cikin Ameenatou Koda ya shiga wata 8 Hafiz ya sauya kamanni gabaki Daya sbd azabar rayuwa da wahala tareda nauyin dayake kansa da yayi masa yawa,
Duk zafin Nemansa da yanda yake tinanin samun mafita kafin haihuwan Ameenatou lamarin ya tsaya cak Dan haka kawai ya yankewa kansa shawarar abinda zai inganta rayuwar Ameenatou dinsu da abinda zata Haifa tareda tsaronsu da samun yancinsu tareda tsayawa su fuskanci komai da kowa kansu a tsaye dan haka batareda sanin kowaba yafara neman hanyar da zai sanar da OMAR JADEN inda suke dan yasan duk inda yake zuwa yanzu yana can yana nemansu.
A yanzu dai Kam