Showing 84001 words to 87000 words out of 261814 words
kafafunsa,
Toshewa kirjinsa yakeyi Yana Jin kaman bazai iya Jan numfashi ba ga idanuwansa da suka fara ganin babbiyu Dan haka yafara bin Bango Baya Gani sosai ya juya Yana dafe gefen kansa da hannu Daya Yana kokarin Bude idanuwansa dakyau da basa Gani sosai bayan gasu a buden.
Tsananta rawa jikinsa yakeyi sosai,
Mummunan faduwa yayi Yana gap da Isa motarsa sbd tsananin da jikinsa yayi Dan haka da rarrafe ya nufi kofar ficewa ya fice yabar Motarsa a gurin Yana rarrafawa duhun gaske Yana qara rufe idanuwansa.
BB dayake nesa sosai daga gidan sbd bayan ya koma Mam sakashi dawowa yayi akan ya tabbatarda ya riqe tsawon lokacin da suka dauka a tare Dan haka ya dawo batareda ya tabbatarda su waye da waye a cikin gidan ba gashi Kuma Yana shakkar Isa gurin sosai ko shiga a samu matsala Dan baisan takun Jamaal ba.
Idanuwansa akan gidan da duk motsin dazai fito cikinsa yake Dan haka Yana hango motsi ya fito daga maboyarsa ahankali tareda Dan biyu duhun ya iso gurin daidai lokacinda Haroon yake fara buga kansa a Kan titin dayake tsit Babu kowa ko motsin komai..
Tareda yayi da sauri tareda rufe masa Baki ya janyesa da sauri daga gurin yayi cikin duhu dashi Yana Jin kirjinsa na harbawa Yana leqa hanyar gidan baiga ko motsin kowaba dazai fito daga ciki.
Sunkutar Haroon yayi gaba Dayansa duk girmansa sbd shi kansa BB din ba qaramin Mai qarfin gaske bane sbd a Bude yake kaman basamude.
Gurin motarsa Dake nesa da gidan ya nufa dashi ya Bude ya Sakasa ciki tareda rufe motar yana juyawa yaga har lokacin Babu kowa yaja motar yabar gurin da sauri sbd Baya buqatan cigaba da jiran indai Haroon daga ciki yake tareda su Omar din yasan me zai masa duk abinda suka tattauno zasuji koma Menene adaren Nan.
****Jamaal irin roko da tabbaci tareda alkawarin da yayiwa Dad da Babbah akan auren ya Saka jikinsu sanyi Jin irin halinda Haroon yake ciki da ciwon dayake cin kansa batareda shi kansa ya sani ba,
Sanar dasu yayi alkwarine ya dauka ana auren zai tafi tareda Haroon din da Ameenatou gurin mum dinsu acan zasu zauna duk wannan yaqin batareda ko dayansu cikin su biyun ba zaayisa wanna alkwarine yayi musu.
Kallansa Dad Omar da idanuwansa sukai jajir yayi sbd Babu abinda Jamaal zai rokesa a rayuwarsa yaji bazai iya basa ba Amma kuma yanzu ana magana ne akan 'yarsa da Bai hadata da kowaba hakama tafi komai na duniyar Nan Daya mallaka mahimmanci da daraja Mai girman gaske a zuciyarsa.
Babbah a nasa bangaren farin cikin Ameenatou ne kadai abinda yake tsaye a ransa,
Tsananin Son da Ameenatou kewa Haroon shine babbar matsalar Dake tayar da hankalinsa Dan kuwa Babu wani abu komai girmansa da zai ciresa daga zuciyarta...
Omar kuwa Jamaal Dayake cikin tsaka me wuyar gaske akan Dan uwansa ya kalla Yana Jin abubuwa da yawa a zuciyarsa gameda auren Wanda zaifi farin ciki da Jin dadin tareda samun cikakkiyar nutsuwa ko bayan mutuwa ace Jamaal ne igiyoyin auren 'yarsa suke hannunsa,
Auren Ameenatou tamkar wani babban nauyin da mutum baisan dashine ba zai dauka Dan kuwa dukiyarta gaba Daya nauyinta akansa zasu sauka,
Haroon bazai taba iyawaba sedai Kuma so yayi gaggawan shiga lamarin nasa da Ameenatou Amma Kuma aurenta ba abune Mai saukin gaske ba garesa,
"Jamaal kayi mun alkawarin zaka tsaya ka tsayu ka zama kariya ga 'yata?
Ka mun alkawarin zaka Hana duk wani cuta tarwatsa rayuwanta?
Kamun alkwarin ko Dan uwanka zaka tsayu gabansa ka zama katangar karfenta idan ya kasa Bata kariya da tsaron Daya kamata,
Idan na bawa Haroon auren 'yata ka sani shi auren na basa Amma Kaine na bawa Amanarta ta har abada,
Ni amatsayin mahaifin Daya haifeta Kaine na bawa aurenta da kaina kaikuma ka karbanwa Dan uwanka Dan haka idan har ka Aminta shi ka bawa auren tabbas bazan Hanaka ba sedai Kasani har abada ni Amanar 'yata na baka Kaine ka aura mata Dan uwan naka.
Jajayen idanuwan Jamaal ya dago Babbah ya fara kalla Wanda Shima shi yake kalla zuciyarsa na rawa hakama jikinsa amsarsa suke Jira Dan dai shi Kam Babbah bayajin zai aminta da auren sedai kafin yayi magana Jamaal ya fadawa Dad maganganun da suka hatta jikin Babbah yin sanyi baisan lokacinda Hawaye suka sake gangaro masa ba sbd yanajin tabbas Shima ya amince a aurawa Haroon din Ameenatou sbd Jamaal ya kashe musu jiki da alkawarin Daya dauka tareda Amanar Ameenatou Daya tabbatarwa dad din idan har su Dad dinsa sun samu damar taba ko suturar jikin Ameenatou da dukiyarta to bayan ransa ne Inshallah.
Ahmed Daya kasa riqe kansa akan tsananin kaunar dayakewa Jamaal rungumesa yayi sbd Daman yasan Jamaal namijin gaske ne ko Dad Omar baice komaiba jininsa yafi karfin ganin cutatarwa indai Jamaal Yana sane,
Kaunar datake tsakanin Jamaal da Omar kaunace irin ta asalin 'da da uban da suka hada jini,
Yanda yake Jin Dad Omar ko mahaifinsa Baya jinsa a cikin ransa Hakan,
Shi kansa Omar yanda yakejin Jamaal ko ransa ko cewa Yayi yaje da kansa ya sanarwa su Mamman waye yarsa zaiyi sbd yasan bazasu iya komai Dan itaba.
Rungumesa Ahmed yayi Yana Jin nauyin dayake zuciya da kansa sun rage na alkwarin bawa Omar da 'yarsa kariya Koda da rayuwarsa ne.
Har lokacin Jamaal zuciyarsa wani irin nauyi da daci ne danne da ita Dan haka Dad Omar ma dayake Jin nauyi da tsananin dacin zuciya rungumesa yayi sai alokacin hawayen Jamaal din suka gangaro daga idanuwansa Shima Dad Omar sai alokacin nasa suka gangaro Dan Bai taba zubda Hawaye ga rabuwarsa da Yan uwansa ba sai yau din Badan abin Baya cin zuciya da ruhinsa ba sai Dan baisamu Wanda daidai irin radadin ne aransaba sai yau din Dan yasan radadin dayake ransa shine yake ran Jamaal.
A cikin daren Omar ya sanar dashi komai daya Dade a rubuce na sunan AMEENATOU dayake kan komai na Abinda ya mallaka Dan haka Babbah yaji hankalinsa ya sake tashi Dan kaman sun sake nutso ne shida iyalansu da Ameenatou din cikin wutar qaddarar da zata kona kowa Dan haka take yaji zazzabi da ciwon kirji na rufesa,
Jamaal ma ciwon kan ne tareda zazzabin gaske ya rufesa sbd kirjinsa Daya toshe Dan haka cikin karfin hali ya fito kusan su babban da Dad Omar na bayansa suka fito gurin sedai babban tashin hankalin da suka tarar a wajen ne ya Saka jiri diban Dad Omar da Jamaal lokaci Daya sbd tabbatarda motar Haroon ce a gurin pake.
Ahmed ma dayake cikin shock saurin tare Omar yayi Yana kallan motar da tashin hankali yace
"Haroon Yana gurin Nan??
Babbah na Jin Hakan jiri ya zubar dashi jikin motar Omar Dake gurin Yana ambatar "Qalu innalillahi wainna ilaihirrajiun.
Jamaal Daya ji kansa na sake daukan masifaffiyar zafi da sauri ya nufi motar yaganta a rufe
Ahmed da Shima cikin tashin hankalin ya zagaya Baya ya zagayo koina gidan baiga Haroon dinba ya dawo saiga key din motarsa a kasa gurin yashe.
Babbah na ganin Hakan yayi zaman Yan bori a gurin Yana cewa
"Shikenan haukarsa ta motsa zaije ya sanar WA mahaifinsa"
Zabura yayi da sauri ya nufi Omar Yana cewa
"Wallahi tinda baida cikakkiyar lafiya tsaf zai iya sanarwa ubansa,ku yi wani abu Akai ko wlh tallahi a cikin Daren Nan na tattara iyalina ku nememu ku rasa wlh ko zaka sake ganina sai qiyama idan mun hadu gaban Allah."
Dad Omar da Baya ma gane me Babbahn ke fada motarsa ya nufa Dan sauri Shima Jamaal tasa ya nufa Ahmed ne yasamu karfin halin Jan Babbah ya jefa mota ya rufe suka tayarda motacinsu kaman masu wasan tsere cikin mugun gudun Daya Saka Babbah sake shiga tashin hankali suka hau titi su sukai kudi shi yayi arewa kowannensu Yana Saka Kiran wayar Haroon din ba kakkautawa.
Jamaal kaman zai tashi sama haka ya figi motar Yana Saka Kiran Haroon din idanuwansa na rikidewa gaba Daya Dan kuwa kowannensu tsoronsa kada Haroon din ya nufi su Dad Dan haka tabbas yaji wani abu shiyasa ya bar gurin a halinda basuda tabbacinsa tinda ga key din motarsa yashe a gurin.
#MAMUH#
#JAMAAL JEEY SEELAH
#AMEENATOU JDEN SEELAH
#OMAR JDEN SEELAH
#MAM SEEELAH
#LAMS SEELAH
#THE SEELAHS
#WAR
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOU_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBiyar
#BestLove
54
BB kuwa Kai tsaye gidansa ya nufa Dan Haroon din Kuma harya Isa Bai Hadu da wata matsala ta jamian tsaro ba Dan haka Yana Isa yayi parking motarsa a harabar gidansa ya Bude ya fito ya zagayo ya Bude motar ya dauko Haroon din Wanda ciwonsa yakai kololuwan tashi sai fizga yakeyi Yana jijjiga kansa Yana buga kan a jikin hannuwansa idanuwansa a rintse.
Kai tsaye Dayan dakinsa yakaisa ya zubar a kasa tareda juyawa ya fice daga dakin Yana Ciro wayarsa ya Saka Kiran babban yaransa.
Yana daukan wayar Kai tsaye BB yace
"Killer ka kawomin Ps biyu yanzun Nan"
"Yes oga" killer ya fada daga bangarensa Yana kashe wayar tareda ture macen datake kansa tana lashesa kaman sweet har Saida kanta ya bugu da Bango ko a jikinsa ya miqe tsaye Yana kama dadar kansa datake a watse ya Saka Roba ya daureta tsakiyar Kai Yana nufar toilet ya wanko jikinsa ya fito,
Underwear yafara sakawa kafin ya Saka Jean Akai ya Saka shirt ya dauki wayarsa da key din motarsa yafice bayan ya shiga dayar dakinsa da mugayen kwayoyin rayuwa suke ciki ya dauko wadda ogan ya buqata.
Koda killer ya iso gidan BB ya tube yayo wanka dagashi sai underwear Wanda kusan Babu abinda na jikinsa da baka Gani.
Dakin suka nufa Yana miqawa killer hannu ya amsa fitinanniyar kwayar wadda take hade da ruwan alluran ta,
Tsananin karfi da balain dayake tattareda ita uku ake tanata asha Daya alluran Kuma tafi komai balai da masifa Dan hadda tsananin azabar gaske ne da ita Dan haka suna shiga dakin ya daga allurar Bai tsaya wata wata ba ya kama wuyan Haroon ya soka masa ita tareda dure masa ruwanta gabaki Daya Wanda yayi daidai da budewan idanuwansa cikin tsananin azabar da Bai taba samun kansa aciki ba take ya qame kaman Sanda kafin jikinsa ya saki gaba Daya Hawaye na gangaro gefen Idanuwansa da sukai duhu gaba Daya Baya ganin komai.
Sakin kansa BB yayi gaba Daya ya yanke jiki agurin ya zube kansa na bugawa da bakin table Dake gurin gashinsa na fashewa jini na fitowa ahankali ya lumshe idanuwansa Yana Jin jijiyan jikinsa kaman suna tsinkewan hakama jinin dayake jikinsa yana konewa cikin wata sanyayyar azaba Mai radadin gaske ga ganinsa gaba Daya ya dauke Baya ganin komai Baya Jin komai.
Dad Lameenu ne da BB ya kira tin Yana hanya ya shigo dakin bayan BB ya Bude masa kofar Yana kallansa tareda basa tabbacin Haroon din bayaji Baya ganin Komai.
Tsayuwa Dad Lameenu din yayi akansa tareda kallan BB Wanda Shima killer ya kalla aka Ciro kwayar killer na kokarin rabawa uku BB yace ya basa a Hakan.
Cikin tsananin firgici da tashin hankali killer din duk rashin imaninsa ya Kalli BB din sbd ko ukun idan aka ranata akasha ba qaramin Neman kashe mutum takeyiba bare duka Kuma har gida biyu.
Karban kwayoyin Yan kanana dasu BB yayi baiyi wata wata ba ya Bude bakin Haroon dayake kwance kaman gawan data rasa gatan suturtawa ya zuba masa su duka tareda karban ruwan da Alh Lameenu yake miqa masa ya zuba masa take suka wuce maqoshinsa.
Suna shiga kafin ma su fara aiki BB ya bari fuskansa da karfi tareda tayar dashi zaune duk da jikinsa asake yake Babu abinda yake Aiko a jikinsa.
Cikin tsananin mawuyacin halin da ko mara Imani Saiya zubar masa da Hawaye ya Bude bakinsa kansa na masa wani hayaqin masifa da balai yafara jijjiga Yana cewa
"Ameenatou itace 'yarka Dad Omar, Dad Omar ka auramun Ameenatou sbd mutuwa zanyi idan na rasata, Ameenatou bazan taba barin kowa yasan itace 'yar da ake nemaba ko da Hakan zaiyi sanadin Raina Dad Omar,
Babbah ku bani Ameenatou,
Jamaal ku bani Ameenatou,
Dad Omar ka taimakeni ka cika mun burin auren Ameenatou.......""
Sakinsa BB yayi tareda ja Baya da tsananin karfi jikinsa na daukan wani rawa da tashin hankalin da Bai taba tinanin shiga ba sbd Jin Abinda Haroon ke fada,
Shi kansa Lameenu Baya yayi da sauri Saida killer ya tarosa sbd firgici da shock din abinda yaji din.
Haroon kuwa sanqarewa yakeyi jini na fitowa bakinsa da hancinsa sosai sedai Bai Dena magana ba hakama jikinsa Bai Dena jijjiga ba.
Da sauri cikin masifaffen tashin hankali da tsoron abinda yake Gani da Wanda yaji Dad Lameenu ya Kalli BB Yana cewa suyi sauri su gogewa Haroon din jinin su mayar dashi inda zaa samesa kada ya mutu a hannunsu.
Suma Dake cikin tashin hankali sake shiga sabon tashin hankalin sukai sbd sanin waye Mam idan 'dansa ya mutu a hannunsu Dan haka ba Bata lokaci suka daukesa suka Kai mota
Kusan motarsu data Lameenu a tare suka fice su sukabi wata hanyar Shima yabi wata.
Tafiya sukeyi suna gudu sosai suna kallan Haroon din Wanda yake zubarda jini sosai har lokacin cikin mafi tsananin azabar rayuwarsa da Bai taba jiba.
Tafiya me tsayi sukai kafin suka Isa inda BB din ya daukosa suka ajiyesa agurin suka gudu batareda kowa ya gansu ba.
Suna barin gurin motar siddeeq da shima ya shiga layin masu tsananin Neman Haroon din sbd zautuwan da Jamaal ke Neman yi gurin Nemansa Yana Sako Kai a layin Dan sake dubawa sai gashi kuwa yayi mummunan Gani Dan halinda ya samu Haroon din saura kadan ya buga zuciyarsa,
Bazai iya barin Jamaal ya gansa a wannan mummunan halinba Dan haka hankali tashe ya daukesa tsaban shiga rikici Kai tsaye Mansion din ya nufa dashi sedai Yan Isa ganin abin yayi muni Dad ya nema Kai tsaye sbd shi kansa jijjiga jikinsa yakeyi tsaban tashin hankali.
Mam na fitowa kallo Daya yayiwa Haroon ya Yanke jiki ya Fadi sbd zuciyarsa data buga irin bugun da zai iya kamuwa da shanyewan Rabin jiki mum Atee ce tayi saurin rikesa itama jikinta na daukan rawar tsoro da firgita sbd ganin abinda yafi karfin nata rashin Imanin.
Daukansa Akai aka nufi ciki dashi Kai tsaye bangarensa Akai dashi zuwa lokacin jikinsa sake sanqarewa yakeyi Dan haka suna Isa Kai tsaye toilet siddeeq ya wuce dashi ya Saka a bathtub din dayake cike da ruwan sanyi.
Dad kasa tsayuwa yayi ya qarasa gurin Haroon din dayake sanqare acikin ruwan jini har lokacin Yana fitowa ta hancinsa.
Wani irin kukan da baisan yanada shi bane ya fashewa Dad din Yana ihun ambatar Haroon din daidai Nan Lameenu yashigo Shima kafafunsa na rawar tashin hankali da tsoron abinda zai iya biyo Baya.
Kamo Haroon din yayi Shima Yana ambatar sunansa sedai Haroon Babu abinda yake ji a lokacin.
Sosai jinin yake sake gudu Wanda ya Saka siddeeq kasa riqe kansa ya kira Jamaal Wanda yaketa bulayi a titin Lagos Yana Neman Haroon din Yanajin abinda siddeeq ya fada Kai tsaye ya juyo motarsa kaman zai tashi sama yayo mansion din.
Isowansa yayi daidai da wani tarin jinin gaske da Haroon ya feso daga bakinsa Mai yawa jikinsa na qarasa sakewa gaba Daya a jikin Dad Wanda yake rungume da Haroon din qamqam Yana Jin Abinda Bai taba ji ba na ganin zaka rasa Wanda kake tsananin so da dukkanin rayuwarka.
Ganin Dan uwansa ya Saka Jamaal karasawa kafafunsa na Neman sarewa hakama zuciyarsa koina yankewa yaji tana yi.
Dad Lameenu da sauri ya janye daga Haroon din ya bawa Jamaal guri.
Hannuwansa duka biyu yakai cikin ruwan ya kamo Dan uwansa Yana fitowa dashi sbd gaba Daya jikinsa ya lalace da jini
Bai tsaya komaiba ficewa yayi dashi daga dakin ya fita dashi Dad Wanda ya kasa motsawa daga inda yake tsaban mutuwan dayakejin duka jikinsa yayi Babu inda ke motsuwa mum Atee ce ta kamasa suka fito suma suka marawa Jamaal din Baya.
Asibiti Jamaal ya nufa dashi cikin gaggawa aka karbesa sedai hadda Jamaal din aka shiga sbd samun damun tsayar da jininsa da ya zube sosai Dan take jininsa ya fara yin qasa.
Dayake da yawan manyan doctors din asibitin sunsan Dr Jamaal Seelah din baa hanasa shigaba Dan shine ya tsayar da jinin sedai ana buqatan jinin sakawa Jamaal din da gaggawa take ya kwanta aka fara diban nasa ana sakawa haroon din Wanda ya koma daidai sedai Babu inda yake motsi a jikinsa yayi fari fayau a cikin kankanin lokaci ya koma abin tausayin da zaka dauka shekarunsa ashirin a kwance.
A waje kuwa Dad da mum Atee da siddeeq ne sai Dad Lameenu da mummy Sarat duka tsit gurin ya dauka bayan Kaida kawo Babu abinda siddeeq keyi su kuwa Dad aketa Neman Kiran likita ya dubasa sbd jininsa yayi mummunan hawan dayake buqatan maganin gaggawa Shima.
#MAMUH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBoyar
55
Dad Omar ma tin kafin a ga Haroon din jininsa yahau Shima har yana Naman zubewa dole Ahmed ya dawo dashi gida Shima aka Nemo likita.
Babbah ma a gida likitan aka Nemo sbd take ya rafke zuciya na ciwo sosai hankalin nasa Iyalin yayi mummunan tashi.
A cikin Daren abubuwa da yawa sun faru marasa dadi da tashin hankali tareda Saka hawan jinin mutane da dama,
Sai guraren asuba Haroon ya farka sedai cikin yanayin Daya Sakasa tsiyayo da Hawaye masu zafin gaske Yana kallan Dan uwansa Dake gabansa zaune Yana kallansa idanuwansa jajir
Ko baa fada ba yasan irin radadin dayake zuciyar JAMAAL bamai faduwa ne ba,
Wani numfashi Mai dumi ya sauke ahankali hawayen cikin idonsa na gangarowa yanason magana Amma ya kasa sbd baisan me zai fada ba,
Abu uku zuciyarsa a yanzu kadai take so sbd samun sanyin da sassaucin azaban dayake ji na cin jininsa,
Ganin mahaifiyarsa,ganin Ameenatou da Kuma Jamaal din Wanda shi gashinan a gabansa.
Ahankali ya Bude bakinsa cikin sanyi da karfin hali yace
"Nagode"
Sukan Jamaal kalmar tayi Dan haka ya miqe tsaye Yana kokarin danne tausayi da tsinkewan da zuciyarsa keyi tareda nauyin dayake ji a kirjinsa yace
"Ka manta yau daurin aurenka???
Murmushi Haroon